Babbar Kotun Tarayya da ke Abuja ta sanya ranar 26 ga Mayu domin yanke hukunci a shari’ar da ke neman hana tsohon shugaban ƙasa Goodluck Jonathan tsayawa takarar shugaban ƙasa a zaɓen 2027.
Mai shari’a Peter Lifu ne ya ɗage sauraron ƙarar zuwa ranar bayan kammala sauraron hujjojin lauyoyin ɓangarorin biyu a ranar Litinin.
Rahotanni sun bayyana cewa wani lauya mai suna Johnmary Jideobi ne ya shigar da ƙarar yana neman kotu ta hana Jonathan gabatar da kansa ga kowace jam’iyya a matsayin ɗan takarar shugaban ƙasa a 2027.
Mai ƙarar ya kuma roƙi kotun da ta hana INEC karɓa, da tantancewa ko wallafa sunan Jonathan a matsayin ɗan takarar shugaban ƙasa, yana mai cewa kundin tsarin mulkin Nijeriya bai ba shi damar sake tsayawa takara ba bisa tanade-tanaden sashe na 137(3) na kundin tsarin mulkin 1999.















Discussion about this post