Tsohon Shugaban Jam’iyyar APC na ƙasa, Dakta Abdullahi Umar Ganduje, ya sake jaddada cewa yana nan daram a cikin jam’iyyar APC, yana mai cewa shi ba ɗan siyasar da ke yawo daga jam’iyya zuwa jam’iyya ba domin biyan buƙatun kansa. Ya kwatanta kansa da cewa ba “ungulu ce da ke tashi daga wani itace zuwa wani ba.
“Ganduje ya bayyana haka ne yayin da ya musanta wasu fastoci da ke yawo a shafukan sada zumunta, waɗanda ke iƙirarin cewa ya fice daga APC ya koma jam’iyyar NDC. Ya ce waɗannan fastocin ƙarya ne, kuma an ƙirƙire su ne domin yaɗa ruɗani da rikita mambobin APC da jama’a.
A cikin wata sanarwa da tsohon Kwamishinan Yaɗa Labarai kuma tsohon Shugaban Ma’aikatansa, Kwamared Muhammad Garba, ya fitar, Ganduje ya ce bai taɓa tunanin barin APC ba, jam’iyyar da ya jagoranta a matsayin Shugabanci na ƙasa. Ya ƙara da cewa iƙirarin cewa ya koma NDC ba shi da tushe, kuma ba ya da wata ma’ana ta siyasa ko ta hankali.
Sanarwar ta ce APC har yanzu ita ce jam’iyya mafi girma kuma mafi ƙarfi a Nijeriya, tana ci gaba da samun karɓuwa a faɗin ƙasar nan ƙarƙashin jagorancin Shugaba Bola Ahmed Tinubu. Ta kuma zargi wasu masu neman tayar da fitina da ƙirƙirar fastocin domin ɓata sunan Ganduje da haddasa ruɗani a cikin jam’iyyar.
Ganduje ya bayyana cewa an gano waɗanda suka ƙirƙira da kuma yaɗa fastocin na bogi, yana gargadin cewa idan ba su janye su tare da daina yaɗa su ba, za a ɗauki matakin shari’a a kansu. Ya buƙaci mambobin APC da sauran jama’a su yi watsi da fastocin, tare da jaddada cewa zai ci gaba da aiki tare da Shugaba Tinubu da shugabannin APC wajen ƙarfafa jam’iyyar da aiwatar da manufofin Renewed Hope Agenda.














