Gwamnan Jihar Kano, Abba Kabir Yusuf, ya buƙaci Hukumar Yaki da Masu Yi Wa Tattalin Arziki Zagon Ƙasa (EFCC) da Hukumar Yaki da Cin Hanci da Rashawa da Sauran Laifuka Masu Alaka da Hakan (ICPC) da su sanya ido kan yadda ake raba takin zamani na tallafi a faɗin jihar domin tabbatar da gaskiya da riƙon amana. Hakan na ƙunshe ne cikin wata sanarwa da Darakta Janar na Yaɗa Labarai da Hulɗa da Jama’a na Gidan Gwamnatin Kano, Sunusi Bature Dawakin Tofa, ya fitar a ranar Alhamis.
Gwamna Yusuf ya bayar da wannan umarni ne yayin ƙaddamar da rabon manyan motocin dakon taki 150 ga manoma a ƙananan hukumomi 44 na jihar. Ya ce shigar da hukumomin yaƙi da cin hanci cikin aikin na da nufin tabbatar da cewa takin ya isa hannun manoma na haƙiƙa tare da daƙile karkatar da shi, ko boyewa da sauran hanyoyin almundahana.
Gwamnan ya buƙaci shugabannin ƙananan hukumomi 44 da su gudanar da rabon cikin gaskiya, da adalci da riƙon amana, yana mai cewa shirin zai taimaka wajen rage tsadar noma, da ƙara yawan amfanin gona da kuma inganta wadatar abinci. Ya kuma yi gargaɗin cewa duk wanda aka samu da laifin karkatar da takin ko kawo cikas ga shirin zai fuskanci hukunci bisa tanadin doka.
Gwamna Yusuf ya sake jaddada ƙudirin gwamnatinsa na tabbatar da gaskiya, da rikon amana da amfani da dukiyar al’umma yadda ya kamata, yana mai bayyana noma a matsayin ginshikin tattalin arziƙin Jihar Kano.














