Jami’an Hukumar Yaƙi da Cin Hanci da Rashawa (EFCC) reshen shiyya ta 2 da ke Ikoyi, Lagos, sun fara bincike kan wani da ake zargi da yin bogin lauya, John Anoruo, bisa zargin mallakar hatimin ƙungiyar lauyoyi ta Nijeriya (NBA) na jabu.
An kama Anoruo, wanda ke jagorantar gudanar da wata cibiyar bayar da shawara kan harkokin shari’a da ilimi a yankin Ikorodu na Jihar Legas, a ranar Litinin, 20 ga Afrilu, 2026.
A cewar EFCC cikin wata sanarwa da ta wallafa a shafinta na Facebook a ranar Talata da yamma, lamarin ya samo asali ne bayan Anoruo ya shigar da ƙorafi mai ɗauke da kwanan watan 22 ga Satumba, 2025, a madadin wasu kwastomominsa kan kamfanin Global West Vessel Specialist Nigeria Limited.
Sai dai bincike ya nuna cewa ƙorafin da kuma wasiƙar janye ƙarar mai ɗauke da kwanan watan 5 ga Maris, 2026, duk suna ɗauke da hatimin NBA na jabu, wanda Anoruo ya amsa cewa ya samo shi ne daga wata cibiyar kasuwanci da bai bayyana ba a Legas.
A yayin binciken, mutumin mai shekaru 55 ya ce duk da cewa ya samu digirin lauya a shekarar 2018 daga Jami’ar Nijeriya da ke Nsukka (UNN), bai halarci Makarantar Horas da Lauyoyi ta Nijeriya ba, wadda dole ne ga duk wanda zai yi aikin lauya a Nijeriya.
EFCC ta ce za a gurfanar da wanda ake zargin a gaban kotu da zarar an kammala bincike.















Discussion about this post