ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Alhazan Neja Sun Yi Watsi Da Kalaman Gwamna Bago A Kan NAHCON

by Sulaiman and Bello Hamza
2 years ago
Nahcon

Ana ci gaba da mayar da martani a kan kiran da Gwamnan Jihar Neja, Umaru Bago ya yi na neman a soke Hukumar Alhazai ta Nijeriya NAHCON a kan ikirarinsa na yadda hukumar ta tafiyar da harkokin aikin Hajjin wannan shekarar.

Martani na baya-bayan na ya fito ne daga wasu Alhazan jihar, inda suka ce Gwamnan ya nuna son rai a kalamansa kuma ba da yawun alhazan Jihar Neja da ma na Nijeriya gaba daya ya yi wadanna maganganun ba.

“Ba da yawunmu gwamnan ya yi kalaman ba, in ka lura ma masaukan da gwamnatin jihar ta kama mana a Makkah yana can bayan gari ne nesa da Harami.

ADVERTISEMENT

“Ba mu samun zuwa gudanar da sallolin mu a masallacin harami saboda nisa amma gwamnan ya kawar da kansa daga wannan mastalar yana magana a kan Tanti masu alfarma (Tent A) a Muna saboda shi ne ta shafa ba sauran Alhazai abin yan shafa ba” in ji wani Alhaji mai suna Halilu Usman daga jihar.

A martaninsa, Jami’in watsa labarai na hukumar Alhazan Jihar Neja, Jibrin Usman Kodo ya bayyana cewa, lallai masaukan alhazan jihar a Makkah ya yi nisa da Harami amma sun samar da motoci 7 da ke zirga- zirgar kai Alhazai zuwa masallacin Harami da dawo da su domin gudanar da ibadunsu. Ya bayyana haka ne a takardar manema labarai da ya sawa hannu a ranar Alhamis a Makkah.

LABARAI MASU NASABA

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Amma kuma a wani bincike, wakilinmu ya ga yadda wasu Alhazan Jihar Neja ke taka sayyada daga masaukinsu zuwa Harami,: “Motoci biyu kawai ke zirga-zirgar daukar Alhazai suma ba akai-akai ba.

“Kamar yadda ka gani, da yawa cikinmu takawa muke yi na wajen awa biyu zuwa da dawowa Harami shi ya sa wadanda basu da karfi suke zamansu a otal.

“Ta yaya jihar da ta kasa samar wa da alhazanta ingantaccen masauki kusa da Harami za ta nemi a karbe harkokin gudanar da aikin hajji gaba daya daga Hukumar NAHCON?,” tambayar da wani Alhaji kuma dan kasuwa mai suna Abubakar Umar ya yi wa waklinmu ke nan.

Haka kuma kungiyoyi da masu ruwa da tsaki a kan harkokin aikin hajji da dama sun yi fatali da kalaman Gwamna Bago na a soke hukumar aikin Haji ta Nijeriya NAHCON, inda suka nuna cewa, kiran ba shi tattare da wata hikima.

Kungiyar ‘Independent Hajj Reporter, IHR’ ta nuna rashin amincewa da kalaman na Bago a cikin sanarwa da ta fitar ranar Litinin inda shugabanta na kasa Ibrahim Muhammad ya sanya wa hannu. Kungiyar ta kara da cewa, a dokoki na duflomasiya, kasar Saudiya tana hulda ne da hukumar Alhazai daya tak daga kowace kasa ba hukumomin Alhazai ba, ‘Wannan kira na Bago na nufin kasar Saudiya za ta yi hulda da hukumomin Alhazai 36 ke nan daga Nijeriya, abin kuma da ba zai yiwu ba kenan” in ji ta.

Haka kuma wata kungiyar ‘yan jarida masu kula da aikin hajji mai suna ‘Media Awareness Initiatibes for Hajj (MAI-HAJJ)’ ta yaba wa hukumar NAHCON a kan yadda ta gudanar da harkokin aikin hajji a wannan shekarar, musamman a bangaren abin da ya shafi masaukai da abincin da aka ciyar da Alhazai a Masha’.eer (Mina and Arafat).

Kungiyar ta bayyana haka ne a takardar sanarwar da ta raba wa manema labarai ranar Juma’a 28 ga watan Yuni 2024, wanda mataimakin shugabanta na yankin arewa Uwais Abubakar Idris da jami’inta na watsa labarai, Malam Kabiru Yusuf suka sanya wa hannu.

“Yawancin alhazan da ‘yan jaridarmu suka tattauna da su sun nuna yadda aka ci abinci har ana zubarwa a Mina da Arafat saboda yawan abincin da NAHCON take ciyar da aalhazai.,” in ji kungiyar.

Kungiyar ta kuma yi watsi da kalaman Gwamnan Nija, ta ce ba a taba samun aikin hajin da ba bu mastala ba a duk duniya, amma dole a yaba wa NAHCON musamman shugabanta Malam Jala Ahmed Arabi.

NAHcon
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace
  • Sulaiman
    ’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin
  • Sulaiman
    Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi
  • Sulaiman
    Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”
NAHcon
Bello Hamza
+ posts Bio
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Hijira 1448:Za A Samu Yalwar Tattalin Arziƙi A Nijeriya —Sheikh Muhajjadina
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    NPA Ta Samar Da Tashoshin Jiragen Ruwan Da Za Su Ƙarfafa Kasuwanci Da Ƙasashen Duniya – Dantsoho
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Gwanjon Kadarori: Kotun Daukaka Kara Ta Kori Karar Da Sani Sha’aban Ya Shigar
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Amfani Da Matar Soja Wajen Isar Da Sakon Bukata

MASU ALAKA

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi
Labarai

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”
Ra'ayi Riga

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma
Labarai

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Next Post
An Yi Taron “Inganta AI+ Da Gina Sabon Karfin Samar Da Hajoji Da Hidimomi Masu Karko” A Shanghai

An Yi Taron "Inganta AI+ Da Gina Sabon Karfin Samar Da Hajoji Da Hidimomi Masu Karko" A Shanghai

LABARAI MASU NASABA

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026
Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026
Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

June 24, 2026
Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.