ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Alhazan Neja Sun Yi Watsi Da Kalaman Gwamna Bago A Kan NAHCON

by Sulaiman and Bello Hamza
2 years ago
Nahcon

Ana ci gaba da mayar da martani a kan kiran da Gwamnan Jihar Neja, Umaru Bago ya yi na neman a soke Hukumar Alhazai ta Nijeriya NAHCON a kan ikirarinsa na yadda hukumar ta tafiyar da harkokin aikin Hajjin wannan shekarar.

Martani na baya-bayan na ya fito ne daga wasu Alhazan jihar, inda suka ce Gwamnan ya nuna son rai a kalamansa kuma ba da yawun alhazan Jihar Neja da ma na Nijeriya gaba daya ya yi wadanna maganganun ba.

“Ba da yawunmu gwamnan ya yi kalaman ba, in ka lura ma masaukan da gwamnatin jihar ta kama mana a Makkah yana can bayan gari ne nesa da Harami.

ADVERTISEMENT

“Ba mu samun zuwa gudanar da sallolin mu a masallacin harami saboda nisa amma gwamnan ya kawar da kansa daga wannan mastalar yana magana a kan Tanti masu alfarma (Tent A) a Muna saboda shi ne ta shafa ba sauran Alhazai abin yan shafa ba” in ji wani Alhaji mai suna Halilu Usman daga jihar.

A martaninsa, Jami’in watsa labarai na hukumar Alhazan Jihar Neja, Jibrin Usman Kodo ya bayyana cewa, lallai masaukan alhazan jihar a Makkah ya yi nisa da Harami amma sun samar da motoci 7 da ke zirga- zirgar kai Alhazai zuwa masallacin Harami da dawo da su domin gudanar da ibadunsu. Ya bayyana haka ne a takardar manema labarai da ya sawa hannu a ranar Alhamis a Makkah.

LABARAI MASU NASABA

PDP Ta Musanta Mara Wa APM Baya A Bauchi

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

Amma kuma a wani bincike, wakilinmu ya ga yadda wasu Alhazan Jihar Neja ke taka sayyada daga masaukinsu zuwa Harami,: “Motoci biyu kawai ke zirga-zirgar daukar Alhazai suma ba akai-akai ba.

“Kamar yadda ka gani, da yawa cikinmu takawa muke yi na wajen awa biyu zuwa da dawowa Harami shi ya sa wadanda basu da karfi suke zamansu a otal.

“Ta yaya jihar da ta kasa samar wa da alhazanta ingantaccen masauki kusa da Harami za ta nemi a karbe harkokin gudanar da aikin hajji gaba daya daga Hukumar NAHCON?,” tambayar da wani Alhaji kuma dan kasuwa mai suna Abubakar Umar ya yi wa waklinmu ke nan.

Haka kuma kungiyoyi da masu ruwa da tsaki a kan harkokin aikin hajji da dama sun yi fatali da kalaman Gwamna Bago na a soke hukumar aikin Haji ta Nijeriya NAHCON, inda suka nuna cewa, kiran ba shi tattare da wata hikima.

Kungiyar ‘Independent Hajj Reporter, IHR’ ta nuna rashin amincewa da kalaman na Bago a cikin sanarwa da ta fitar ranar Litinin inda shugabanta na kasa Ibrahim Muhammad ya sanya wa hannu. Kungiyar ta kara da cewa, a dokoki na duflomasiya, kasar Saudiya tana hulda ne da hukumar Alhazai daya tak daga kowace kasa ba hukumomin Alhazai ba, ‘Wannan kira na Bago na nufin kasar Saudiya za ta yi hulda da hukumomin Alhazai 36 ke nan daga Nijeriya, abin kuma da ba zai yiwu ba kenan” in ji ta.

Haka kuma wata kungiyar ‘yan jarida masu kula da aikin hajji mai suna ‘Media Awareness Initiatibes for Hajj (MAI-HAJJ)’ ta yaba wa hukumar NAHCON a kan yadda ta gudanar da harkokin aikin hajji a wannan shekarar, musamman a bangaren abin da ya shafi masaukai da abincin da aka ciyar da Alhazai a Masha’.eer (Mina and Arafat).

Kungiyar ta bayyana haka ne a takardar sanarwar da ta raba wa manema labarai ranar Juma’a 28 ga watan Yuni 2024, wanda mataimakin shugabanta na yankin arewa Uwais Abubakar Idris da jami’inta na watsa labarai, Malam Kabiru Yusuf suka sanya wa hannu.

“Yawancin alhazan da ‘yan jaridarmu suka tattauna da su sun nuna yadda aka ci abinci har ana zubarwa a Mina da Arafat saboda yawan abincin da NAHCON take ciyar da aalhazai.,” in ji kungiyar.

Kungiyar ta kuma yi watsi da kalaman Gwamnan Nija, ta ce ba a taba samun aikin hajin da ba bu mastala ba a duk duniya, amma dole a yaba wa NAHCON musamman shugabanta Malam Jala Ahmed Arabi.

NAHcon
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    PDP Ta Musanta Mara Wa APM Baya A Bauchi
  • Sulaiman
    Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara
  • Sulaiman
    Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5
  • Sulaiman
    Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana
NAHcon
Bello Hamza
+ posts Bio
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Jihar Kano Za Ta Amfana Matuka Da Gidauniyar Aliko Dangote – Masu Ruwa Da Tsaki
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    An Nuna Damuwa Kan Sake Kamun Da DSS Ta Yi Wa Boɗejo Bayan Samun Belin EFCC
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Dole Al’ummar Arewa Su Rungumi Hanyoyin Kasuwanci Na Zamani —Alfa Musa
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Ba Mu Taba Biyan Kudin Fansa Ba Kuma Ba Za Mu Biya Ba – Kwamishinan Katsina

MASU ALAKA

Taron PDP Na Ƙasa: Ɓangaren Wike Ya Kafa Sabon NWC A Abuja
Labarai

PDP Ta Musanta Mara Wa APM Baya A Bauchi

September 9, 2026
Sojoji
Manyan Labarai

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

September 9, 2026
'Yan Bindiga
Labarai

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Next Post
An Yi Taron “Inganta AI+ Da Gina Sabon Karfin Samar Da Hajoji Da Hidimomi Masu Karko” A Shanghai

An Yi Taron "Inganta AI+ Da Gina Sabon Karfin Samar Da Hajoji Da Hidimomi Masu Karko" A Shanghai

LABARAI MASU NASABA

Taron PDP Na Ƙasa: Ɓangaren Wike Ya Kafa Sabon NWC A Abuja

PDP Ta Musanta Mara Wa APM Baya A Bauchi

September 9, 2026
Sojoji

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

September 9, 2026
Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.