Mai magana da yawun ma’aikatar harkokin wajen kasar Sin Lin Jian, ya ce amincewar Amurka da manufar kasar Sin daya tak a duniya, da sanarwa uku ta hadin gwiwa tsakanin sassan biyu, da ma martaba alkawura da gwamnatocin baya na Amurka suka yi dangane da batun yankin Taiwan, nauyi ne na kasa da kasa da ya wajaba Amurka ta sauke.
Lin Jian, wanda ya bayyana hakan a Alhamis din nan, yayin taron manema labarai na yau da kullum, lokacin da yake amsa tambaya mai nasaba da hakan, ya kara da cewa, “Amincewar hakan daga bangaren Amurka tushe ne na cimma alakar Sin da Amurka mai nagarta, da daidaito kuma mai dorewa.
Kazalika, Lin ya ce batun Taiwan ginshiki ne cikin manyan moriyar kasar Sin, kana tushe ne na alakar siyasa tsakanin Sin da Amurka. A cewarsa, “Dagewar Sin wajen kare hadin kan al’ummar kasa, da martabar yankunanta batu ne da ba zai taba sauyawa ba. Bugu da kari, ayyukan ‘yan a ware masu neman ballewar yankin Taiwan, da zaman lafiya a zirin Taiwan abubuwa ne biyu da ba za su taba haduwa wuri guda ba.
Jami’in ya ce, abu ne mai matukar muhimmanci a samar da matsaya a fili, kuma mai karfi game da adawa da neman “’yancin Taiwan”, tare da tabbatar da zaman lafiya da daidaito a zirin Taiwan. (Saminu Alhassan)















Discussion about this post