ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Tuesday, July 7, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Amurka Ta Bayyana Dalilin Janye Jakadanta Daga Nijeriya Da Wasu Kasashe 29

by Leadership Hausa
6 months ago
TULSA, OK - MARCH 18: Former United States President Donald Trump stands on the floor during the Division I Mens Wrestling Championship held at the BOK Center on March 18, 2023 in Tulsa, Oklahoma. (Photo by Shane Bevel/NCAA Photos via Getty Images)

TULSA, OK - MARCH 18: Former United States President Donald Trump stands on the floor during the Division I Mens Wrestling Championship held at the BOK Center on March 18, 2023 in Tulsa, Oklahoma. (Photo by Shane Bevel/NCAA Photos via Getty Images)

Shugaba Donald Trump, ya janye jakadan Amurka na Nijeriya, Richard M. Mills Jr., da na wasu manyan kasashe 29 na duniya.

Ambasada Mills, wanda aka nada a ranar 25 ga Yuli, 2024, yana cikin jakadu 13 da ke aiki a kasashen Afirka, wanda masu sharhi a Washington suka ce; hakan na nufin sake fasalin manufofin harkokin wajen Amurka a kan ajandar Trump.

  • Sheikh Al-Sudais Ya Gargadi Masu Ibadah Kan Kiyaye Darajar Masallatan Harami
  • An Yi Bikin Murnar Cika Shekaru 15 Da Kafuwar Asibitin Abota Na Sin Da Ghana

A cewar kamfanin dillancin labarai na AP, jami’an diflomasiyyar da abin ya shafa, wadanda aka nada, da yawa daga cikinsu an nada su ne a lokacin gwamnatin Biden, amma sai suka ci gaba da rike mukamansu tun a farkon watannin Trump a ofis, an sanar da su a makon da ya gabata cewa; wa’adinsu zai kare a watan Janairun 2026.

ADVERTISEMENT

Wani jami’in da ke da masaniya kan ci gaban ya shaida wa AP cewa, “Jakadan suna aiki ne bisa yardar shugaban kasa, duk da cewa; yawancisu suna kan mukaminsu na tsawon shekaru uku zuwa hudu.”

Jami’an, wadanda suka bukaci a sakaya sunansu, sun bayyana cewa; ba korar jakadun aka yi daga ma’aikatar harkokin wajen ba, za a mayar da su Washington ne, domin wasu ayyukan daban idan sun zabi ci gaba da aikin nasu.

LABARAI MASU NASABA

Mutane 15 Sun Mutu A Hatsarin Mota A Jihar Kwara

Rashin Tsaro: Kisa Ne Ya Fi Cancanta Ga ‘Yan Ta’adda Ba Gyaran Hali Ba – Ɗan Majalisa Gagdi

Ma’aikatar Harkokin Wajen Amurka, ta ki tabbatar da adadin wakilan da abin ya shafa, amma ta kare matakin, tana mai bayyana shi a matsayin “daidaitaccen tsari a kowace gwamnati.”

A cikin wata sanarwa da ma’aikatar ta fitar ta ce, “Jakada wakilin shugaban kasa ne, kuma hakkin shugaban kasa ne tabbatar da cewa; yana da mutane a kasashe wadanda kare muradu da ajandar Amurka ita ce farko.”

Afirka ita ce yankin da aka fi fama da matsalar, inda aka kira jakadu daga kasashe 13: Burundi, Kamaru, Cape Berde, Gabon, Cote d’Iboire, Madagascar, Mauritius, Nijar, Nijeriya, Rwanda, Senegal, Somalia da kuma Uganda.

Yankin Asiya zuwa Pacific ya biyo bayan sauye-sauye na jakadanci shida a Fiji, Laos, Tsibirin Marshall, Papua New Guinea, Philippines, da Bietnam. Sauran wadanda abin ya shafa sun hada da jakadu a kasashen Turai hudu (Armenia, Macedonia, Montenegro, da Slobakia), biyu a Gabas ta Tsakiya (Algeria da Masar), biyu a Kudancin Asiya (Nepal da Sri Lanka), da biyu a Yammacin Duniya (Guatemala da Suriname).

Janye jakadun, ya yi nuni da daya daga cikin manyan sauye-sauyen diflomasiyya a karkashin wa’adin Trump na biyu.

Leadership Hausa
Website |  + postsBio
  • Leadership Hausa
    Batun Dakile Shan Taba Sigari A Tsakanin Yara A Nijeriya
  • Leadership Hausa
    Har Yanzu Akwai Sauran Rina A Kaba Game Da Makomar Yara A Nijeriya
  • Leadership Hausa
    Yadda Arsenal Ta Lashe Gasar Firimiya Bayan Shekara 22
  • Leadership Hausa
    Bukatar Kawo Karshen Akidar Kyamar Baki A Kasar Afirka Ta Kudu

MASU ALAKA

Mutane 15 Sun Mutu A Hatsarin Mota A Jihar Kwara
Labarai

Mutane 15 Sun Mutu A Hatsarin Mota A Jihar Kwara

July 6, 2026
Rashin Tsaro: Kisa Ne Ya Fi Cancanta Ga ‘Yan Ta’adda Ba Gyaran Hali Ba – Ɗan Majalisa Gagdi
Labarai

Rashin Tsaro: Kisa Ne Ya Fi Cancanta Ga ‘Yan Ta’adda Ba Gyaran Hali Ba – Ɗan Majalisa Gagdi

July 6, 2026
Mu Leka Yadda Kasar Sin Ke Raya Hakkin Dan Adam Daga Taron Gefe Na UNHRC
Ra'ayi Riga

Mu Leka Yadda Kasar Sin Ke Raya Hakkin Dan Adam Daga Taron Gefe Na UNHRC

July 6, 2026
Next Post
A Bangaren Kyawawan Dabi’u, Annabi SAW Ma’aiki Ne Ga Duk Halitta

A Bangaren Kyawawan Dabi'u, Annabi SAW Ma'aiki Ne Ga Duk Halitta

LABARAI MASU NASABA

Kasuwa Ce Ke Saita Tsarin Cinikayyar Sin Da EU In Ji Kakakin Ma’aikatar Harkokin Wajen Sin

Kasuwa Ce Ke Saita Tsarin Cinikayyar Sin Da EU In Ji Kakakin Ma’aikatar Harkokin Wajen Sin

July 6, 2026
Dukkan Kabilun Kasar Sin Na Zaman Tsintsiya Madaurinki Daya

Dukkan Kabilun Kasar Sin Na Zaman Tsintsiya Madaurinki Daya

July 6, 2026
Mutane 15 Sun Mutu A Hatsarin Mota A Jihar Kwara

Mutane 15 Sun Mutu A Hatsarin Mota A Jihar Kwara

July 6, 2026
Gwamnatin Sin Ta Fara Aika Zagayen Farko Na Kayakin Agajin Gaggawa Ga Venezuela

Gwamnatin Sin Ta Fara Aika Zagayen Farko Na Kayakin Agajin Gaggawa Ga Venezuela

July 6, 2026
FIFA Ta Tsallake Iyakarta Dangane Da Batun Dakatarwar Balogun – UEFA

FIFA Ta Tsallake Iyakarta Dangane Da Batun Dakatarwar Balogun – UEFA

July 6, 2026
Shugabannin Sin Da Madagascar Sun Yi Musayar Sakon Taya Murnar Cika Shekaru 20 Da Kulla Alakar Diflomasiyya Tsakaninsu

Shugabannin Sin Da Madagascar Sun Yi Musayar Sakon Taya Murnar Cika Shekaru 20 Da Kulla Alakar Diflomasiyya Tsakaninsu

July 6, 2026
Rashin Tsaro: Kisa Ne Ya Fi Cancanta Ga ‘Yan Ta’adda Ba Gyaran Hali Ba – Ɗan Majalisa Gagdi

Rashin Tsaro: Kisa Ne Ya Fi Cancanta Ga ‘Yan Ta’adda Ba Gyaran Hali Ba – Ɗan Majalisa Gagdi

July 6, 2026
Mu Leka Yadda Kasar Sin Ke Raya Hakkin Dan Adam Daga Taron Gefe Na UNHRC

Mu Leka Yadda Kasar Sin Ke Raya Hakkin Dan Adam Daga Taron Gefe Na UNHRC

July 6, 2026
ADC Ta Rushe Shugabannin Jam’iyyar A Kano, Ta Naɗa Kwamitin Riƙo

ADC Ta Rushe Shugabannin Jam’iyyar A Kano, Ta Naɗa Kwamitin Riƙo

July 6, 2026
Rundunar Sojin Ruwan Sin Ta Yi Gwajin Makami Mai Linzami Ta Amfani Da Jirgin Ruwa Mai Nutso

Rundunar Sojin Ruwan Sin Ta Yi Gwajin Makami Mai Linzami Ta Amfani Da Jirgin Ruwa Mai Nutso

July 6, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.