ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Amurka Ta Bayyana Dalilin Janye Jakadanta Daga Nijeriya Da Wasu Kasashe 29

by Leadership Hausa
9 months ago
TULSA, OK - MARCH 18: Former United States President Donald Trump stands on the floor during the Division I Mens Wrestling Championship held at the BOK Center on March 18, 2023 in Tulsa, Oklahoma. (Photo by Shane Bevel/NCAA Photos via Getty Images)

TULSA, OK - MARCH 18: Former United States President Donald Trump stands on the floor during the Division I Mens Wrestling Championship held at the BOK Center on March 18, 2023 in Tulsa, Oklahoma. (Photo by Shane Bevel/NCAA Photos via Getty Images)

Shugaba Donald Trump, ya janye jakadan Amurka na Nijeriya, Richard M. Mills Jr., da na wasu manyan kasashe 29 na duniya.

Ambasada Mills, wanda aka nada a ranar 25 ga Yuli, 2024, yana cikin jakadu 13 da ke aiki a kasashen Afirka, wanda masu sharhi a Washington suka ce; hakan na nufin sake fasalin manufofin harkokin wajen Amurka a kan ajandar Trump.

  • Sheikh Al-Sudais Ya Gargadi Masu Ibadah Kan Kiyaye Darajar Masallatan Harami
  • An Yi Bikin Murnar Cika Shekaru 15 Da Kafuwar Asibitin Abota Na Sin Da Ghana

A cewar kamfanin dillancin labarai na AP, jami’an diflomasiyyar da abin ya shafa, wadanda aka nada, da yawa daga cikinsu an nada su ne a lokacin gwamnatin Biden, amma sai suka ci gaba da rike mukamansu tun a farkon watannin Trump a ofis, an sanar da su a makon da ya gabata cewa; wa’adinsu zai kare a watan Janairun 2026.

ADVERTISEMENT

Wani jami’in da ke da masaniya kan ci gaban ya shaida wa AP cewa, “Jakadan suna aiki ne bisa yardar shugaban kasa, duk da cewa; yawancisu suna kan mukaminsu na tsawon shekaru uku zuwa hudu.”

Jami’an, wadanda suka bukaci a sakaya sunansu, sun bayyana cewa; ba korar jakadun aka yi daga ma’aikatar harkokin wajen ba, za a mayar da su Washington ne, domin wasu ayyukan daban idan sun zabi ci gaba da aikin nasu.

LABARAI MASU NASABA

PDP Ta Musanta Mara Wa APM Baya A Bauchi

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

Ma’aikatar Harkokin Wajen Amurka, ta ki tabbatar da adadin wakilan da abin ya shafa, amma ta kare matakin, tana mai bayyana shi a matsayin “daidaitaccen tsari a kowace gwamnati.”

A cikin wata sanarwa da ma’aikatar ta fitar ta ce, “Jakada wakilin shugaban kasa ne, kuma hakkin shugaban kasa ne tabbatar da cewa; yana da mutane a kasashe wadanda kare muradu da ajandar Amurka ita ce farko.”

Afirka ita ce yankin da aka fi fama da matsalar, inda aka kira jakadu daga kasashe 13: Burundi, Kamaru, Cape Berde, Gabon, Cote d’Iboire, Madagascar, Mauritius, Nijar, Nijeriya, Rwanda, Senegal, Somalia da kuma Uganda.

Yankin Asiya zuwa Pacific ya biyo bayan sauye-sauye na jakadanci shida a Fiji, Laos, Tsibirin Marshall, Papua New Guinea, Philippines, da Bietnam. Sauran wadanda abin ya shafa sun hada da jakadu a kasashen Turai hudu (Armenia, Macedonia, Montenegro, da Slobakia), biyu a Gabas ta Tsakiya (Algeria da Masar), biyu a Kudancin Asiya (Nepal da Sri Lanka), da biyu a Yammacin Duniya (Guatemala da Suriname).

Janye jakadun, ya yi nuni da daya daga cikin manyan sauye-sauyen diflomasiyya a karkashin wa’adin Trump na biyu.

Leadership Hausa
Website |  + postsBio
  • Leadership Hausa
    Karuwar Farin Jinin Gwamna Umaru Bago A Siyasar Jihar Neja
  • Leadership Hausa
    Kyakkyawan Tsarin Laken Asiri Zai Dakile Shirin Magudin Zabe A Nijeriya —Mohammed
  • Leadership Hausa
    Batun Dawo Da Tallafin Mai Da Atiku Ya Yi Na Ci Gaba Da Tayar Da Kura
  • Leadership Hausa
    Batun Guguwar Kakar Yakin Neman Zabukan 2027 A Nijeriya

MASU ALAKA

Taron PDP Na Ƙasa: Ɓangaren Wike Ya Kafa Sabon NWC A Abuja
Labarai

PDP Ta Musanta Mara Wa APM Baya A Bauchi

September 9, 2026
Sojoji
Manyan Labarai

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

September 9, 2026
'Yan Bindiga
Labarai

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Next Post
A Bangaren Kyawawan Dabi’u, Annabi SAW Ma’aiki Ne Ga Duk Halitta

A Bangaren Kyawawan Dabi'u, Annabi SAW Ma'aiki Ne Ga Duk Halitta

LABARAI MASU NASABA

Taron PDP Na Ƙasa: Ɓangaren Wike Ya Kafa Sabon NWC A Abuja

PDP Ta Musanta Mara Wa APM Baya A Bauchi

September 9, 2026
Sojoji

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

September 9, 2026
Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.