ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Bukatar Kawo Karshen Akidar Kyamar Baki A Kasar Afirka Ta Kudu

by Leadership Hausa and Sulaiman
3 weeks ago
Baki

Abin takaici ne, matuka, kan yadda wasu ‘yan kasar Afirka ta Kudu, ke ci gaba da cutar da ‘yan Nijeriya da ke zaune a kasar da kuma sauran wasu ‘yan cirani, da suka shiga cikin kasar da suka  fito daga kasashen da ke Afirka.

Akasarin ‘yan cirianin sun tsallaka iyakokin kasashen su, zuwa cikin kasar Afrika ta Kudu ne, saboda samun sa’ida, kan zaman kuncin rayuwa da matsatin attalin arziki da suke fuskanta a kasashen su, domin su samu ayyukan da za su, rufawa kansu asiri

Tarihin Afrika ta Kudu dai, ba zai taba cika ba, ba tare da Ambato sunan dangwagwarmayar nemowa kasar ‘yancin kai ba wato Nelson, musamman duba da cewa, a wancan lokacin, Nijeriya ta tsaya tayin daka, domin ganin kasar, ta samu ‘yancin kanta, amma sai dai, abin bakin ciki, a yau sai wasu ‘yan Afika ta Kudu, suka mayar da kasar fagen daga, na dirkawa ‘yan Nijeriya na jiki, har da ma, kaiwa ga kashe wasunsu.

ADVERTISEMENT

Kazalika, ana kuma ta kone shagunan ‘yan Nijeriya, inda iyalai, ke ci gaba da kulli Kucciya, duba da yadda a makwannin da suka shige, wasu ‘yan Afirka ta Kudu marasa imani, suka hallaka wasu ‘yan Nijeriya biyu.

Ana dai yin amfani da wata kungiya a kasar da ake kira da Dudula, bisa nufin aikata manufar, musamman domin ganin an yiwa bakin haure a kasar, korar Kare, kuma babbar manufar kungiyar shi ne, domin a kai hare-haren kan bakaken fata.

LABARAI MASU NASABA

Shin Nijeriya Ta Shirya Tunkarar Dawowar Annobar Ebola?

Buƙatar Samar Da Alƙibla Ta Musamman Ga Gidajen Gyaran Hali Na Ƙasar Nan

Karin wani abin takaicin shi ne, duk irin wannan cin mutucin da ake yiwa bakin haren, ana yi masu ne, a gaban jami’an tsaro, inda jami’an tsaron, suke  nuna halin ko in kula, kan ta’asar da ‘yan Afirka ta Kudu, suke aiwatarwa.

A nan za mu iya cewa, ofishin jakadanci na Nijeriya da ke a birnin Johannesburg, ya yi gaskiya, kan fitar da sanarwar gargadin ‘yan Nijeriya da ke a Afirka ta Kudu, musamman ‘yan kasuwa, da su tabbatar da sun kulle shagunansu, domin kaucewa, masu kai hare-haren.

Dan katabus din da shugaban kasar Cyril Ramaphosa ta bakin Ministan kula da harkokin cikin gida na kasar Ronald Lamola, shi ne, yin tir, da kai hare-haren.

A gafe daya kuma, Ministan kula da harkokin ‘yan sanda na kasar Firoz Cachalia, ya ayyana nuna kymar ta bakaken fata da ke  zaune a kasar, a matsayin, abin da kasar, ba za ta laumunta ba.

Za a iya cewa, wadannna kalaman nasu, sun yi dai-dai, amma a bangare daya, za a iya cewa, ba su da wani alfanu, domin kuwa, kalamai ne da mahkuntan kasar, suka saba yi, shekaru da dama da suka shude, matukar ana samu irin wannan yanayin, na cin zarfin bakaken fata a kasar.

Misali, a irin wannan nuna wayar launin fata an hallaka bakin haure 62 tare da tarwatsa dubbansu, daga matsugunan su, a 2008.

Kazalika, kai hare-haren a kan bakaken fata, ya basu daga  yankin Durban  zuwa Johannesburg, a 2015, wanda sai da ta kai ga, an tura dakarun sojin kasar, domin kwantar da kura.

Bugu da kari an samu kai wasu hare-haren, kan ‘yan kasuwa ‘yan Nijeriya a 2019, inda lamarin ya kai ga, gwamnatin tarayya ta wancan lokacin, ta yiwa babban kwamishinan kasar nan kiranye da kuma ‘yan Nijeriya, inda lamarin ya kai ga, harzuka wasu ‘yan Nijeriya, suka gudanar da zanga-zangar, yunkurin kai hare-hare, a kan ‘yan Afirka ta Kudu, da ke a jihar Legas da Abuja.

Duk da yin tir da mahukuntan Afirka ta Kudu ke yi kan wannan halin dabbacin na wasu .

Abin tambaya a nan shi ne, shin akwai wani abu da ya sauya?

Hakazalika, a 2026,  an ci gaba da hallaka ‘yan Nijeriya a Afirka ta kudu, lamarin da ya sanya, a karo na hudu ko na biyar,  a tarihin kasar, aka yiwa mukaddashin babban Kwamishinan kasar nan, kiranye, zuwa Abuja.

A ra’ayin wannan Jaridar,  matsin tattalin arziki da ya yiwa wasu ‘yan Afrika ta Kudu tsanani ne, musamman duba da cewa, rashin aikin yi a kasar, ya kai kaso 33, inda wannan kason, ya haura kusan na duniya, sai  su ke fakewa da Guzuma, sun harbin Karsana, wato cin zarafin ‘yan Nijeriya, har da ma, kai wa matakin hallaka su.

A gefe daya kuma, jami’iyyar ANC mai mulki a kasar, nauyi ya yi mata, musamman kan gazawar ta, ba samarwa da ‘yan kasar, ababen more rayuwa, wanda hakan ya sanya, wasu ‘yan kasar, suka buge da cin mutuncin ‘yan Nijeriya, da ke zaune a kasar.

Bugu da kari, wasu kwararru da suka tofa albarkacin bakin su, sun yi ittifaki da cewa, gazawar gwamnatin kasar, hakan ya kara sanya wa, wasu ‘yan Afirka ta kudu, huce fishin su, a kan bakingazawaryanayin da daukar daukar hukunci a kan bakin hauren, domin kawai, su fice daga cikin kasar.

Wani abu da ‘yan kasar Afirka ta kudu suka jahilta shi ne,  ‘yan Afirka da ke a kasar suke da shugunan da suke gudanar da kasuwancin su a Soweto, ba su ne hummul haba’isin janyo rashin aikin yi a Afirka ta kudu ba, hakan ‘yan kasuwa ‘yan Nijeriya da ke a Johannesburg, ba su ne makasudin gazawar gwamnatin ANC, na samar da ingantaccen tsarin tattalin arzikin kasar ba.

Kazalika, ‘yan kwadago ‘yan kasar Zimbabwean da ke a birnin Cape Town, ba su da wata nasaba da gazawar kebe wani gwagwabin kaso, a cikin ksafin kudi, na Cape Town, domin gwamnatin jihar, ta samar da ababen more rayuwa ga ‘yan jihar.

A nan, za a iya cewa, shuwagabanin baya, da suka mulki kasar a baya, su ne, suka fi cancanta, a dorawa laifin   yanayin da kasar, ke ci gaba da fuskanta, har zuwa yau.

Kusan gum da shuwagabannin kasar suka kan cin mutuncin bakin hauren, ya nuna a zahiri, suna kawai tsoron fushin ‘yan kasar ne.

A nan, za mu iya cewa, matakan da gwamnatin tarayya ta dauka, na kwaso ‘yan Nijeriya zuwa gida abu ne, da ya dace, inda aka fara dawo da mutane 130 tare da kuma yiwa babban mukaddashin kwamishina na kasar nan, kiranye.

Sai dai, babbar tambayar da ta kamata Nijeriya da kungiyar AU su bijiro da ita ita ce, ya batun matakan da za a dauka, kan irin kisan gillar da ake yiwa bakaken fata bakin haure, a Afirka ta kudu?

A kwanan baya, an ruwaito Sakataren Majalisar Dinkin Duniya Antonio Guterres, ya bayyana takaicinsa, kan hare-haren nuna wayar launin fata da bakaken fata, ke kai wa a kan ‘yanuwansu, bakaken fata inda ya yi nuni da cewa, wannan halin na rashin imani, ba shi da wani bagire ko kusa, a cikin harkar mulkin Demokiradiyya, na kowacce irin kasa.

Ya zama tilas gwamnatin Afirka ta kudu, ta gaggauta cafkewa tare da kuma hukunta duk wanda aka samu da hannu, na kai hare-haren domin a hukunta su.

Bugu da kari, mika ta’aziyya da mahukuntan Afirka ta kudu suka yi kan kasan bakin hauren, bai wadatar ba, dole ne a tabbatar da an samar da adalci, ga iyalan ‘yan Nijeriya da hare-haren ya rutsa da su.

Baki
Leadership Hausa
Website |  + posts Bio
  • Leadership Hausa
    Yadda Arsenal Ta Lashe Gasar Firimiya Bayan Shekara 22
  • Leadership Hausa
    Ikirarin Cewa Sanata Abdul’aziz Yari Abubakar, Marafan Sokoto, Nauyi Ne Ga Jihar Zamfara Da Jam’iyyar APC Ba Ta Da Tushe
  • Leadership Hausa
    Nazarin Kisan Gillar Da ‘Yan Kato Da Gora Suka Yi Wa Wani Matashi A Biniwe
  • Leadership Hausa
    Zaben 2027: Akwai Bukatar A Yi Takatsantsan Domin Samun Cikakkiyar Nasara
Baki
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo
  • Sulaiman
    Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli
  • Sulaiman
    Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus
  • Sulaiman
    ’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

MASU ALAKA

Shin Nijeriya Ta Shirya Tunkarar Dawowar Annobar Ebola?
Ra'ayinmu

Shin Nijeriya Ta Shirya Tunkarar Dawowar Annobar Ebola?

May 29, 2026
Buƙatar Samar Da Alƙibla Ta Musamman Ga Gidajen Gyaran Hali Na Ƙasar Nan
Labarai

Buƙatar Samar Da Alƙibla Ta Musamman Ga Gidajen Gyaran Hali Na Ƙasar Nan

May 22, 2026
Daga Ƙarshe, Tinubu Ya Naɗa Jakadu Uku Bayan Tsawon Shekara 2 Ana Jira
Ra'ayinmu

2027: Batun Murabus Din Masu Rike Da Mukaman Gwamnati

April 3, 2026
Next Post
Sin Za Ta Ci Gaba Da Aiki Tare Da Sassan Kasa Da Kasa Wajen Wanzar Da Zaman Lafiya A Gabas Ta Tsakiya

Sin Za Ta Ci Gaba Da Aiki Tare Da Sassan Kasa Da Kasa Wajen Wanzar Da Zaman Lafiya A Gabas Ta Tsakiya

Discussion about this post

LABARAI MASU NASABA

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026
Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

June 3, 2026
Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

June 3, 2026
Hada Kai Da ’Yan Awaren Yankin Taiwan Ba Zai Haifar Da Ɗa Mai Ido Ba

Hada Kai Da ’Yan Awaren Yankin Taiwan Ba Zai Haifar Da Ɗa Mai Ido Ba

June 3, 2026
An Gudanar Da Taron Kasa Da Kasa Na Magadan Gari Na 2026 A Beijing

An Gudanar Da Taron Kasa Da Kasa Na Magadan Gari Na 2026 A Beijing

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.