Abin takaici ne, matuka, kan yadda wasu ‘yan kasar Afirka ta Kudu, ke ci gaba da cutar da ‘yan Nijeriya da ke zaune a kasar da kuma sauran wasu ‘yan cirani, da suka shiga cikin kasar da suka fito daga kasashen da ke Afirka.
Akasarin ‘yan cirianin sun tsallaka iyakokin kasashen su, zuwa cikin kasar Afrika ta Kudu ne, saboda samun sa’ida, kan zaman kuncin rayuwa da matsatin attalin arziki da suke fuskanta a kasashen su, domin su samu ayyukan da za su, rufawa kansu asiri
Tarihin Afrika ta Kudu dai, ba zai taba cika ba, ba tare da Ambato sunan dangwagwarmayar nemowa kasar ‘yancin kai ba wato Nelson, musamman duba da cewa, a wancan lokacin, Nijeriya ta tsaya tayin daka, domin ganin kasar, ta samu ‘yancin kanta, amma sai dai, abin bakin ciki, a yau sai wasu ‘yan Afika ta Kudu, suka mayar da kasar fagen daga, na dirkawa ‘yan Nijeriya na jiki, har da ma, kaiwa ga kashe wasunsu.
Kazalika, ana kuma ta kone shagunan ‘yan Nijeriya, inda iyalai, ke ci gaba da kulli Kucciya, duba da yadda a makwannin da suka shige, wasu ‘yan Afirka ta Kudu marasa imani, suka hallaka wasu ‘yan Nijeriya biyu.
Ana dai yin amfani da wata kungiya a kasar da ake kira da Dudula, bisa nufin aikata manufar, musamman domin ganin an yiwa bakin haure a kasar, korar Kare, kuma babbar manufar kungiyar shi ne, domin a kai hare-haren kan bakaken fata.
Karin wani abin takaicin shi ne, duk irin wannan cin mutucin da ake yiwa bakin haren, ana yi masu ne, a gaban jami’an tsaro, inda jami’an tsaron, suke nuna halin ko in kula, kan ta’asar da ‘yan Afirka ta Kudu, suke aiwatarwa.
A nan za mu iya cewa, ofishin jakadanci na Nijeriya da ke a birnin Johannesburg, ya yi gaskiya, kan fitar da sanarwar gargadin ‘yan Nijeriya da ke a Afirka ta Kudu, musamman ‘yan kasuwa, da su tabbatar da sun kulle shagunansu, domin kaucewa, masu kai hare-haren.
Dan katabus din da shugaban kasar Cyril Ramaphosa ta bakin Ministan kula da harkokin cikin gida na kasar Ronald Lamola, shi ne, yin tir, da kai hare-haren.
A gafe daya kuma, Ministan kula da harkokin ‘yan sanda na kasar Firoz Cachalia, ya ayyana nuna kymar ta bakaken fata da ke zaune a kasar, a matsayin, abin da kasar, ba za ta laumunta ba.
Za a iya cewa, wadannna kalaman nasu, sun yi dai-dai, amma a bangare daya, za a iya cewa, ba su da wani alfanu, domin kuwa, kalamai ne da mahkuntan kasar, suka saba yi, shekaru da dama da suka shude, matukar ana samu irin wannan yanayin, na cin zarfin bakaken fata a kasar.
Misali, a irin wannan nuna wayar launin fata an hallaka bakin haure 62 tare da tarwatsa dubbansu, daga matsugunan su, a 2008.
Kazalika, kai hare-haren a kan bakaken fata, ya basu daga yankin Durban zuwa Johannesburg, a 2015, wanda sai da ta kai ga, an tura dakarun sojin kasar, domin kwantar da kura.
Bugu da kari an samu kai wasu hare-haren, kan ‘yan kasuwa ‘yan Nijeriya a 2019, inda lamarin ya kai ga, gwamnatin tarayya ta wancan lokacin, ta yiwa babban kwamishinan kasar nan kiranye da kuma ‘yan Nijeriya, inda lamarin ya kai ga, harzuka wasu ‘yan Nijeriya, suka gudanar da zanga-zangar, yunkurin kai hare-hare, a kan ‘yan Afirka ta Kudu, da ke a jihar Legas da Abuja.
Duk da yin tir da mahukuntan Afirka ta Kudu ke yi kan wannan halin dabbacin na wasu .
Abin tambaya a nan shi ne, shin akwai wani abu da ya sauya?
Hakazalika, a 2026, an ci gaba da hallaka ‘yan Nijeriya a Afirka ta kudu, lamarin da ya sanya, a karo na hudu ko na biyar, a tarihin kasar, aka yiwa mukaddashin babban Kwamishinan kasar nan, kiranye, zuwa Abuja.
A ra’ayin wannan Jaridar, matsin tattalin arziki da ya yiwa wasu ‘yan Afrika ta Kudu tsanani ne, musamman duba da cewa, rashin aikin yi a kasar, ya kai kaso 33, inda wannan kason, ya haura kusan na duniya, sai su ke fakewa da Guzuma, sun harbin Karsana, wato cin zarafin ‘yan Nijeriya, har da ma, kai wa matakin hallaka su.
A gefe daya kuma, jami’iyyar ANC mai mulki a kasar, nauyi ya yi mata, musamman kan gazawar ta, ba samarwa da ‘yan kasar, ababen more rayuwa, wanda hakan ya sanya, wasu ‘yan kasar, suka buge da cin mutuncin ‘yan Nijeriya, da ke zaune a kasar.
Bugu da kari, wasu kwararru da suka tofa albarkacin bakin su, sun yi ittifaki da cewa, gazawar gwamnatin kasar, hakan ya kara sanya wa, wasu ‘yan Afirka ta kudu, huce fishin su, a kan bakingazawaryanayin da daukar daukar hukunci a kan bakin hauren, domin kawai, su fice daga cikin kasar.
Wani abu da ‘yan kasar Afirka ta kudu suka jahilta shi ne, ‘yan Afirka da ke a kasar suke da shugunan da suke gudanar da kasuwancin su a Soweto, ba su ne hummul haba’isin janyo rashin aikin yi a Afirka ta kudu ba, hakan ‘yan kasuwa ‘yan Nijeriya da ke a Johannesburg, ba su ne makasudin gazawar gwamnatin ANC, na samar da ingantaccen tsarin tattalin arzikin kasar ba.
Kazalika, ‘yan kwadago ‘yan kasar Zimbabwean da ke a birnin Cape Town, ba su da wata nasaba da gazawar kebe wani gwagwabin kaso, a cikin ksafin kudi, na Cape Town, domin gwamnatin jihar, ta samar da ababen more rayuwa ga ‘yan jihar.
A nan, za a iya cewa, shuwagabanin baya, da suka mulki kasar a baya, su ne, suka fi cancanta, a dorawa laifin yanayin da kasar, ke ci gaba da fuskanta, har zuwa yau.
Kusan gum da shuwagabannin kasar suka kan cin mutuncin bakin hauren, ya nuna a zahiri, suna kawai tsoron fushin ‘yan kasar ne.
A nan, za mu iya cewa, matakan da gwamnatin tarayya ta dauka, na kwaso ‘yan Nijeriya zuwa gida abu ne, da ya dace, inda aka fara dawo da mutane 130 tare da kuma yiwa babban mukaddashin kwamishina na kasar nan, kiranye.
Sai dai, babbar tambayar da ta kamata Nijeriya da kungiyar AU su bijiro da ita ita ce, ya batun matakan da za a dauka, kan irin kisan gillar da ake yiwa bakaken fata bakin haure, a Afirka ta kudu?
A kwanan baya, an ruwaito Sakataren Majalisar Dinkin Duniya Antonio Guterres, ya bayyana takaicinsa, kan hare-haren nuna wayar launin fata da bakaken fata, ke kai wa a kan ‘yanuwansu, bakaken fata inda ya yi nuni da cewa, wannan halin na rashin imani, ba shi da wani bagire ko kusa, a cikin harkar mulkin Demokiradiyya, na kowacce irin kasa.
Ya zama tilas gwamnatin Afirka ta kudu, ta gaggauta cafkewa tare da kuma hukunta duk wanda aka samu da hannu, na kai hare-haren domin a hukunta su.
Bugu da kari, mika ta’aziyya da mahukuntan Afirka ta kudu suka yi kan kasan bakin hauren, bai wadatar ba, dole ne a tabbatar da an samar da adalci, ga iyalan ‘yan Nijeriya da hare-haren ya rutsa da su.















Discussion about this post