ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, July 15, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Bukatar Kawo Karshen Akidar Kyamar Baki A Kasar Afirka Ta Kudu

by Leadership Hausa and Sulaiman
2 months ago
Baki

Abin takaici ne, matuka, kan yadda wasu ‘yan kasar Afirka ta Kudu, ke ci gaba da cutar da ‘yan Nijeriya da ke zaune a kasar da kuma sauran wasu ‘yan cirani, da suka shiga cikin kasar da suka  fito daga kasashen da ke Afirka.

Akasarin ‘yan cirianin sun tsallaka iyakokin kasashen su, zuwa cikin kasar Afrika ta Kudu ne, saboda samun sa’ida, kan zaman kuncin rayuwa da matsatin attalin arziki da suke fuskanta a kasashen su, domin su samu ayyukan da za su, rufawa kansu asiri

Tarihin Afrika ta Kudu dai, ba zai taba cika ba, ba tare da Ambato sunan dangwagwarmayar nemowa kasar ‘yancin kai ba wato Nelson, musamman duba da cewa, a wancan lokacin, Nijeriya ta tsaya tayin daka, domin ganin kasar, ta samu ‘yancin kanta, amma sai dai, abin bakin ciki, a yau sai wasu ‘yan Afika ta Kudu, suka mayar da kasar fagen daga, na dirkawa ‘yan Nijeriya na jiki, har da ma, kaiwa ga kashe wasunsu.

ADVERTISEMENT

Kazalika, ana kuma ta kone shagunan ‘yan Nijeriya, inda iyalai, ke ci gaba da kulli Kucciya, duba da yadda a makwannin da suka shige, wasu ‘yan Afirka ta Kudu marasa imani, suka hallaka wasu ‘yan Nijeriya biyu.

Ana dai yin amfani da wata kungiya a kasar da ake kira da Dudula, bisa nufin aikata manufar, musamman domin ganin an yiwa bakin haure a kasar, korar Kare, kuma babbar manufar kungiyar shi ne, domin a kai hare-haren kan bakaken fata.

LABARAI MASU NASABA

Ana Ci Gaba Da Tafka Muhawara Kan Shirin Gwamnati Na Haramta Masana’atun Sarrafa Robobi

Kisan Gillar Marabar Jos: Bai Kamata Jinin Malama Ummulkhairi Ya Tafi A Banza Ba

Karin wani abin takaicin shi ne, duk irin wannan cin mutucin da ake yiwa bakin haren, ana yi masu ne, a gaban jami’an tsaro, inda jami’an tsaron, suke  nuna halin ko in kula, kan ta’asar da ‘yan Afirka ta Kudu, suke aiwatarwa.

A nan za mu iya cewa, ofishin jakadanci na Nijeriya da ke a birnin Johannesburg, ya yi gaskiya, kan fitar da sanarwar gargadin ‘yan Nijeriya da ke a Afirka ta Kudu, musamman ‘yan kasuwa, da su tabbatar da sun kulle shagunansu, domin kaucewa, masu kai hare-haren.

Dan katabus din da shugaban kasar Cyril Ramaphosa ta bakin Ministan kula da harkokin cikin gida na kasar Ronald Lamola, shi ne, yin tir, da kai hare-haren.

A gafe daya kuma, Ministan kula da harkokin ‘yan sanda na kasar Firoz Cachalia, ya ayyana nuna kymar ta bakaken fata da ke  zaune a kasar, a matsayin, abin da kasar, ba za ta laumunta ba.

Za a iya cewa, wadannna kalaman nasu, sun yi dai-dai, amma a bangare daya, za a iya cewa, ba su da wani alfanu, domin kuwa, kalamai ne da mahkuntan kasar, suka saba yi, shekaru da dama da suka shude, matukar ana samu irin wannan yanayin, na cin zarfin bakaken fata a kasar.

Misali, a irin wannan nuna wayar launin fata an hallaka bakin haure 62 tare da tarwatsa dubbansu, daga matsugunan su, a 2008.

Kazalika, kai hare-haren a kan bakaken fata, ya basu daga  yankin Durban  zuwa Johannesburg, a 2015, wanda sai da ta kai ga, an tura dakarun sojin kasar, domin kwantar da kura.

Bugu da kari an samu kai wasu hare-haren, kan ‘yan kasuwa ‘yan Nijeriya a 2019, inda lamarin ya kai ga, gwamnatin tarayya ta wancan lokacin, ta yiwa babban kwamishinan kasar nan kiranye da kuma ‘yan Nijeriya, inda lamarin ya kai ga, harzuka wasu ‘yan Nijeriya, suka gudanar da zanga-zangar, yunkurin kai hare-hare, a kan ‘yan Afirka ta Kudu, da ke a jihar Legas da Abuja.

Duk da yin tir da mahukuntan Afirka ta Kudu ke yi kan wannan halin dabbacin na wasu .

Abin tambaya a nan shi ne, shin akwai wani abu da ya sauya?

Hakazalika, a 2026,  an ci gaba da hallaka ‘yan Nijeriya a Afirka ta kudu, lamarin da ya sanya, a karo na hudu ko na biyar,  a tarihin kasar, aka yiwa mukaddashin babban Kwamishinan kasar nan, kiranye, zuwa Abuja.

A ra’ayin wannan Jaridar,  matsin tattalin arziki da ya yiwa wasu ‘yan Afrika ta Kudu tsanani ne, musamman duba da cewa, rashin aikin yi a kasar, ya kai kaso 33, inda wannan kason, ya haura kusan na duniya, sai  su ke fakewa da Guzuma, sun harbin Karsana, wato cin zarafin ‘yan Nijeriya, har da ma, kai wa matakin hallaka su.

A gefe daya kuma, jami’iyyar ANC mai mulki a kasar, nauyi ya yi mata, musamman kan gazawar ta, ba samarwa da ‘yan kasar, ababen more rayuwa, wanda hakan ya sanya, wasu ‘yan kasar, suka buge da cin mutuncin ‘yan Nijeriya, da ke zaune a kasar.

Bugu da kari, wasu kwararru da suka tofa albarkacin bakin su, sun yi ittifaki da cewa, gazawar gwamnatin kasar, hakan ya kara sanya wa, wasu ‘yan Afirka ta kudu, huce fishin su, a kan bakingazawaryanayin da daukar daukar hukunci a kan bakin hauren, domin kawai, su fice daga cikin kasar.

Wani abu da ‘yan kasar Afirka ta kudu suka jahilta shi ne,  ‘yan Afirka da ke a kasar suke da shugunan da suke gudanar da kasuwancin su a Soweto, ba su ne hummul haba’isin janyo rashin aikin yi a Afirka ta kudu ba, hakan ‘yan kasuwa ‘yan Nijeriya da ke a Johannesburg, ba su ne makasudin gazawar gwamnatin ANC, na samar da ingantaccen tsarin tattalin arzikin kasar ba.

Kazalika, ‘yan kwadago ‘yan kasar Zimbabwean da ke a birnin Cape Town, ba su da wata nasaba da gazawar kebe wani gwagwabin kaso, a cikin ksafin kudi, na Cape Town, domin gwamnatin jihar, ta samar da ababen more rayuwa ga ‘yan jihar.

A nan, za a iya cewa, shuwagabanin baya, da suka mulki kasar a baya, su ne, suka fi cancanta, a dorawa laifin   yanayin da kasar, ke ci gaba da fuskanta, har zuwa yau.

Kusan gum da shuwagabannin kasar suka kan cin mutuncin bakin hauren, ya nuna a zahiri, suna kawai tsoron fushin ‘yan kasar ne.

A nan, za mu iya cewa, matakan da gwamnatin tarayya ta dauka, na kwaso ‘yan Nijeriya zuwa gida abu ne, da ya dace, inda aka fara dawo da mutane 130 tare da kuma yiwa babban mukaddashin kwamishina na kasar nan, kiranye.

Sai dai, babbar tambayar da ta kamata Nijeriya da kungiyar AU su bijiro da ita ita ce, ya batun matakan da za a dauka, kan irin kisan gillar da ake yiwa bakaken fata bakin haure, a Afirka ta kudu?

A kwanan baya, an ruwaito Sakataren Majalisar Dinkin Duniya Antonio Guterres, ya bayyana takaicinsa, kan hare-haren nuna wayar launin fata da bakaken fata, ke kai wa a kan ‘yanuwansu, bakaken fata inda ya yi nuni da cewa, wannan halin na rashin imani, ba shi da wani bagire ko kusa, a cikin harkar mulkin Demokiradiyya, na kowacce irin kasa.

Ya zama tilas gwamnatin Afirka ta kudu, ta gaggauta cafkewa tare da kuma hukunta duk wanda aka samu da hannu, na kai hare-haren domin a hukunta su.

Bugu da kari, mika ta’aziyya da mahukuntan Afirka ta kudu suka yi kan kasan bakin hauren, bai wadatar ba, dole ne a tabbatar da an samar da adalci, ga iyalan ‘yan Nijeriya da hare-haren ya rutsa da su.

Baki
Leadership Hausa
Website |  + posts Bio
  • Leadership Hausa
    Tallafa Wa Yara Masu Buƙatu Na Musamman Shi Ne Burina
  • Leadership Hausa
    Dole Mata Su Rungumi Sana’o’i Domin Tsira Daga Takaicin Zamani —Ramatu Bello
  • Leadership Hausa
    Batun Dakile Shan Taba Sigari A Tsakanin Yara A Nijeriya
  • Leadership Hausa
    Har Yanzu Akwai Sauran Rina A Kaba Game Da Makomar Yara A Nijeriya
Baki
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya
  • Sulaiman
    Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026
  • Sulaiman
    An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”
  • Sulaiman
    Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

MASU ALAKA

Ana Ci Gaba Da Tafka Muhawara Kan Shirin Gwamnati Na Haramta Masana’atun Sarrafa Robobi
Ra'ayinmu

Ana Ci Gaba Da Tafka Muhawara Kan Shirin Gwamnati Na Haramta Masana’atun Sarrafa Robobi

July 10, 2026
Kisan Gillar Marabar Jos: Bai Kamata Jinin Malama Ummulkhairi Ya Tafi A Banza Ba
Ra'ayinmu

Kisan Gillar Marabar Jos: Bai Kamata Jinin Malama Ummulkhairi Ya Tafi A Banza Ba

July 3, 2026
sikila
Ra'ayinmu

Buƙatar Mayar Da Hankali Wajen Kawo Ƙarshen Ciwon Sikila A Nijeriya

June 26, 2026
Next Post
Sin Za Ta Ci Gaba Da Aiki Tare Da Sassan Kasa Da Kasa Wajen Wanzar Da Zaman Lafiya A Gabas Ta Tsakiya

Sin Za Ta Ci Gaba Da Aiki Tare Da Sassan Kasa Da Kasa Wajen Wanzar Da Zaman Lafiya A Gabas Ta Tsakiya

LABARAI MASU NASABA

‘Yansanda Sun Kama Shugaban PFIPC, Adeyemi

‘Yansanda Sun Kama Shugaban PFIPC, Adeyemi

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

‘Yansanda Sun Kama Wani Kan Zargin Yi Wa ‘Yan Bindiga Safarar Makamai A Kano

July 15, 2026
Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

July 14, 2026
Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

July 14, 2026
An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

July 14, 2026
Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

July 14, 2026
Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

July 14, 2026
Katsina: Kotu Ta Yanke Wa Hauwa’u Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya Kan Taimaka Wa ’Yan Bindiga

Kotu Ta Tsare Shugaban Makaranta Da Malami Kan Zargin Lalata Da Ɗaliba Mai Shekara 6 A Gombe

July 14, 2026
An Bankado Muguwar Aniyar Japan Ta Haifar Da Tashin Hankali A Tekun Kudancin Sin

An Bankado Muguwar Aniyar Japan Ta Haifar Da Tashin Hankali A Tekun Kudancin Sin

July 14, 2026
Layin Dogo Tsakanin Tanzaniya Da Zambiya Ya Zama Shaidar Abota Tsakanin Sin Da Afirka

Layin Dogo Tsakanin Tanzaniya Da Zambiya Ya Zama Shaidar Abota Tsakanin Sin Da Afirka

July 14, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.