An fitar da jadawalin wasannin zagayen farko na gasar cin kofin Carabao na kakar wasa ta 2026/2027, inda ƙungiyoyi 70 suka san abokan karawarsu.
Za a fara gasar ne da wasan da zai haɗa Tranmere Rovers da Rochdale ranar 1 ga watan Agusta, sannan York City za ta kara da Crawley Town ranar 3 ga watan Agusta.
Ƙungiyoyin da suka yi nasara a waɗannan wasanni za su ƙara da Bradford City da Watford a zagaye na gaba.
Mai riƙe da kofin gasar, Manchester City, wadda ta doke Arsenal da ci 2-0 a wasan ƙarshe da aka buga a watan Maris, ba za ta buga zagayen farko ba, domin za ta shiga gasar ne daga zagaye na gaba.
A ɓangaren Arewa, daga cikin manyan wasannin akwai Middlesbrough da Wrexham, Burnley da Notts County, Derby County da Lincoln City, da kuma Wolves da Port Vale.
A ɓangaren Kudu kuma, za a fafata tsakanin QPR da Millwall, Swansea da Birmingham, West Ham da Portsmouth, Leicester City da Northampton Town, da sauran wasanni.
Dukkanin wasannin zagayen farko za a buga su ne a farkon watan Agustan shekarar 2026.













