Ofishin yada labarai na majalisar gudanarwar kasar Sin, ya gudanar da taron “tattaunawar magadan garuruwa na duniya na 2026” a birnin Beijing, daga ranar 2 zuwa 3 ga watan nan na Yuni. Magadan garuruwa da wakilan birane fiye da 30 daga kasashe 6 na Afirka, da suka hada da Morocco, Seychelles, Tunisia, Senegal da sauransu, tare da wasu wakilan kungiyar hadin kan birane na yawon bude ido ta duniya (WTCF), sun halarci taron.
Wadanda suka halarci taron sun gudanar da tattaunawa mai zurfi, da musayar ra’ayi kan “karfafa musayar wayewar kai, da ci gaba da abotar gargajiya tsakanin Sin da Afirka”, tare da fidda hanyoyin ci gaban musayar al’adu da hadin gwiwar birane tsakanin Sin da Afirka.
Shekara ta 2026 ita ce cika shekaru 70 da kulla huldar diflomasiyya tsakanin Sin da kasashen Afirka, kuma ita ce “shekarar musayar al’adu tsakanin Sin da Afirka”. Da yawa daga cikin wakilan birane na Afirka da suka halarci taron sun bayyana cewa, suna fatan karfafa hadin gwiwa da Sin a fannoni kamar na al’adu da yawon bude ido.
A yayin taron, mataimakin magajin garin Ziguinchor na Senegal, El Hadji Saer Faye ya ce, bayan shekaru da yawa, hadin gwiwar Sin da Afirka ya fadada, daga taimako na gargajiya, da samar da ababen more rayuwa, zuwa fannoni kamar na binciken kimiyya, da ilimi da kuma musayar al’adu. Ya ce a mataki nan gaba, Sin da kasashen Afirka za su ci gaba da zurfafa hadin gwiwa mai amfani a fannoni daban-daban, don inganta jin dadin jama’a. (Amina Xu)















Discussion about this post