ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

An Nemi A Yi Hattara Da Guguwar Sauya Sheƙar Siyasa Da Ta Kama Jihar Adamawa

by Bello Hamza
6 months ago
Hattara

Wani jigo a jam’iyyar APC ta Jihar Adamawa ya yi kira ga jagororin jam’iyyar na ƙasa da su yi takatsantsan a kan shirin da ‘yan jam’iyyar adawa ta PDP suke yi na tururuwar sauya sheƙa zuwa jam’iyyar APC a jihar, saboda a cewarsa shirin su na dawowa jami’yyar APC yana iya kassara jam’iyyar tare da cutar da asalin yan jam’iyyar da suka yi wa jam’iyyar bauta na shekara da shekaru.

Wannan bayanin ya fito ne daga bakin Sanata Abdurrahaman Buba Kwacham, Sarkin Fulanin masarautar Mubi kuma shugaban ƙungiyar matasan Arewacin Nijeriya a hirarsa da manema labarai a Abuja.

  • Ƙoƙarin Amurka Na Ganin An Haramta Shari’a A Nijeriya Ya Haifar Da Cece-kuce
  • Ramadan: Lokutan Buda-Baki Da Sahur Na Azumi Na 9

Ya ce ba wai yana yaki da shugowar Gwamna Fintiri da jama’arsa suke ƙoƙarin yi ba ne amma ya kamata a tabbatar da cewa, shigowarsu bai danne ‘yan asalin jam’iyyar ba waɗanda suka yi azumin fiye da shekara 8 ba tare da an dama da su ba.

ADVERTISEMENT

Ya kara da cewa, tsarin jam’iyyar APC na cewa, Gwamna ne shugaban jam’iyya a jiha ko da kuwa yanzun nan ya shigo jam’iyyar abu ne da ya kamata a yi watsi da shi, domin babu adalci an ciki, “Ba gwamna kadai a ke buƙata ba a wajen cin zaɓe ba, dole a tabbatar ana tafiya tare da talakawa masu kada ƙuri’a, saboda haka ya kamata a samar da ƙofar da suma za su san ana yi da su” in ji shi.

A kan haka ya buƙaci a gaggauta soke dokar domin hakan zai iya kawo wa jam’iyyar cikas wajen cin zaɓe, “Mun ga irin haka a Jihar Zamfara inda Gwamna Dauda Lawal ya kayar da gwamnan da ke kan kujerar mulki”.

LABARAI MASU NASABA

PDP Ta Musanta Mara Wa APM Baya A Bauchi

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

Daga nan ya yi watsi da masu yada cewa, yana adawa ne da shigowar Gwamna Fitiri jam’iyyar APC saboda yana fargabar ko Gwamna zai iya neman takarar kujerar Sanata a yankin Adamawa ta tsakiya, inda shima daga nan ya fito, kuma ana raɗe-raɗin zai tsaya takarar kujerar sanata “Bana tsoron fuskantar kowa a fagen zabe musamman ma da a yanzu dokar zaɓe ta soke tsarin DELIGET wajen fitar da dan Takara a zaɓukan cikin gida na jam’iyyu.

“Ina da yakinin talakawa na tare dani, kuma shune za su fitar da dan takara a dukkan matakai, wannan karon babu batun kashe kuɗi domin sayen deliget kamar yadda ‘yan siyasa suka rinƙa yi a baya” in ji shi.

Daga ƙarshe Sanata Buba Kwacham ya nemi ‘yan siyasar Jihar Adamawa su haɗa kai tare da kai zuciya nesa domin tabbatar da zaman lafiya tare da kuma gudanar da siyasa mai tsafta.

Hattara
Bello Hamza
+ postsBio
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Jihar Kano Za Ta Amfana Matuka Da Gidauniyar Aliko Dangote – Masu Ruwa Da Tsaki
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    An Nuna Damuwa Kan Sake Kamun Da DSS Ta Yi Wa Boɗejo Bayan Samun Belin EFCC
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Dole Al’ummar Arewa Su Rungumi Hanyoyin Kasuwanci Na Zamani —Alfa Musa
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Ba Mu Taba Biyan Kudin Fansa Ba Kuma Ba Za Mu Biya Ba – Kwamishinan Katsina

MASU ALAKA

Taron PDP Na Ƙasa: Ɓangaren Wike Ya Kafa Sabon NWC A Abuja
Labarai

PDP Ta Musanta Mara Wa APM Baya A Bauchi

September 9, 2026
Sojoji
Manyan Labarai

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

September 9, 2026
'Yan Bindiga
Labarai

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Next Post
Fintiri Ya Fice Daga PDP Zuwa APC

Fintiri Ya Fice Daga PDP Zuwa APC

LABARAI MASU NASABA

Taron PDP Na Ƙasa: Ɓangaren Wike Ya Kafa Sabon NWC A Abuja

PDP Ta Musanta Mara Wa APM Baya A Bauchi

September 9, 2026
Sojoji

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

September 9, 2026
Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.