ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

An Nemi A Yi Hattara Da Guguwar Sauya Sheƙar Siyasa Da Ta Kama Jihar Adamawa

by Bello Hamza
3 months ago
Hattara

Wani jigo a jam’iyyar APC ta Jihar Adamawa ya yi kira ga jagororin jam’iyyar na ƙasa da su yi takatsantsan a kan shirin da ‘yan jam’iyyar adawa ta PDP suke yi na tururuwar sauya sheƙa zuwa jam’iyyar APC a jihar, saboda a cewarsa shirin su na dawowa jami’yyar APC yana iya kassara jam’iyyar tare da cutar da asalin yan jam’iyyar da suka yi wa jam’iyyar bauta na shekara da shekaru.

Wannan bayanin ya fito ne daga bakin Sanata Abdurrahaman Buba Kwacham, Sarkin Fulanin masarautar Mubi kuma shugaban ƙungiyar matasan Arewacin Nijeriya a hirarsa da manema labarai a Abuja.

  • Ƙoƙarin Amurka Na Ganin An Haramta Shari’a A Nijeriya Ya Haifar Da Cece-kuce
  • Ramadan: Lokutan Buda-Baki Da Sahur Na Azumi Na 9

Ya ce ba wai yana yaki da shugowar Gwamna Fintiri da jama’arsa suke ƙoƙarin yi ba ne amma ya kamata a tabbatar da cewa, shigowarsu bai danne ‘yan asalin jam’iyyar ba waɗanda suka yi azumin fiye da shekara 8 ba tare da an dama da su ba.

ADVERTISEMENT

Ya kara da cewa, tsarin jam’iyyar APC na cewa, Gwamna ne shugaban jam’iyya a jiha ko da kuwa yanzun nan ya shigo jam’iyyar abu ne da ya kamata a yi watsi da shi, domin babu adalci an ciki, “Ba gwamna kadai a ke buƙata ba a wajen cin zaɓe ba, dole a tabbatar ana tafiya tare da talakawa masu kada ƙuri’a, saboda haka ya kamata a samar da ƙofar da suma za su san ana yi da su” in ji shi.

A kan haka ya buƙaci a gaggauta soke dokar domin hakan zai iya kawo wa jam’iyyar cikas wajen cin zaɓe, “Mun ga irin haka a Jihar Zamfara inda Gwamna Dauda Lawal ya kayar da gwamnan da ke kan kujerar mulki”.

LABARAI MASU NASABA

2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

Daga nan ya yi watsi da masu yada cewa, yana adawa ne da shigowar Gwamna Fitiri jam’iyyar APC saboda yana fargabar ko Gwamna zai iya neman takarar kujerar Sanata a yankin Adamawa ta tsakiya, inda shima daga nan ya fito, kuma ana raɗe-raɗin zai tsaya takarar kujerar sanata “Bana tsoron fuskantar kowa a fagen zabe musamman ma da a yanzu dokar zaɓe ta soke tsarin DELIGET wajen fitar da dan Takara a zaɓukan cikin gida na jam’iyyu.

“Ina da yakinin talakawa na tare dani, kuma shune za su fitar da dan takara a dukkan matakai, wannan karon babu batun kashe kuɗi domin sayen deliget kamar yadda ‘yan siyasa suka rinƙa yi a baya” in ji shi.

Daga ƙarshe Sanata Buba Kwacham ya nemi ‘yan siyasar Jihar Adamawa su haɗa kai tare da kai zuciya nesa domin tabbatar da zaman lafiya tare da kuma gudanar da siyasa mai tsafta.

Hattara
Bello Hamza
+ postsBio
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Dole Ne Afirka Ta Zamanantar Da Sufurin Jiragen Ruwa —Ɗantsoho
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Yadda Oyetola Ya Ƙaddamar Da Babban Taron Ƙungiyar  PMAWCA A Legas
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Lokaci Ya Yi Da Matasan Nijeriya Za Su Ƙwato Ƙasarsu — Kwamred Yahaya Abdullahi
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Kamfanin Dangote Na Kara Karfafa Hadin Gwiwar Tattalin Arziki Da Jihar Neja

MASU ALAKA

Atiku Ne Ya Fi Dacewa Da Tikitin Takara A ADC Amma Ya Kamata Ya Janye — Baba-Ahmed
Labarai

2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

June 4, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada
Labarai

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa
Labarai

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Next Post
Fintiri Ya Fice Daga PDP Zuwa APC

Fintiri Ya Fice Daga PDP Zuwa APC

Discussion about this post

LABARAI MASU NASABA

Atiku Ne Ya Fi Dacewa Da Tikitin Takara A ADC Amma Ya Kamata Ya Janye — Baba-Ahmed

2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

June 4, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.