ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

An Nemi A Yi Hattara Da Guguwar Sauya Sheƙar Siyasa Da Ta Kama Jihar Adamawa

by Bello Hamza
4 months ago
Hattara

Wani jigo a jam’iyyar APC ta Jihar Adamawa ya yi kira ga jagororin jam’iyyar na ƙasa da su yi takatsantsan a kan shirin da ‘yan jam’iyyar adawa ta PDP suke yi na tururuwar sauya sheƙa zuwa jam’iyyar APC a jihar, saboda a cewarsa shirin su na dawowa jami’yyar APC yana iya kassara jam’iyyar tare da cutar da asalin yan jam’iyyar da suka yi wa jam’iyyar bauta na shekara da shekaru.

Wannan bayanin ya fito ne daga bakin Sanata Abdurrahaman Buba Kwacham, Sarkin Fulanin masarautar Mubi kuma shugaban ƙungiyar matasan Arewacin Nijeriya a hirarsa da manema labarai a Abuja.

  • Ƙoƙarin Amurka Na Ganin An Haramta Shari’a A Nijeriya Ya Haifar Da Cece-kuce
  • Ramadan: Lokutan Buda-Baki Da Sahur Na Azumi Na 9

Ya ce ba wai yana yaki da shugowar Gwamna Fintiri da jama’arsa suke ƙoƙarin yi ba ne amma ya kamata a tabbatar da cewa, shigowarsu bai danne ‘yan asalin jam’iyyar ba waɗanda suka yi azumin fiye da shekara 8 ba tare da an dama da su ba.

ADVERTISEMENT

Ya kara da cewa, tsarin jam’iyyar APC na cewa, Gwamna ne shugaban jam’iyya a jiha ko da kuwa yanzun nan ya shigo jam’iyyar abu ne da ya kamata a yi watsi da shi, domin babu adalci an ciki, “Ba gwamna kadai a ke buƙata ba a wajen cin zaɓe ba, dole a tabbatar ana tafiya tare da talakawa masu kada ƙuri’a, saboda haka ya kamata a samar da ƙofar da suma za su san ana yi da su” in ji shi.

A kan haka ya buƙaci a gaggauta soke dokar domin hakan zai iya kawo wa jam’iyyar cikas wajen cin zaɓe, “Mun ga irin haka a Jihar Zamfara inda Gwamna Dauda Lawal ya kayar da gwamnan da ke kan kujerar mulki”.

LABARAI MASU NASABA

Ndume Ya Bayyana Dalilin Da Ya Sa Yake Goyon Bayan Ƙudirin Kafa ‘Yansandan Jihohi

EFCC Za Ta Gurfanar Da Shugaban Miyetti Allah Kan Zargin Almundahanar Dala Miliyan 2.53

Daga nan ya yi watsi da masu yada cewa, yana adawa ne da shigowar Gwamna Fitiri jam’iyyar APC saboda yana fargabar ko Gwamna zai iya neman takarar kujerar Sanata a yankin Adamawa ta tsakiya, inda shima daga nan ya fito, kuma ana raɗe-raɗin zai tsaya takarar kujerar sanata “Bana tsoron fuskantar kowa a fagen zabe musamman ma da a yanzu dokar zaɓe ta soke tsarin DELIGET wajen fitar da dan Takara a zaɓukan cikin gida na jam’iyyu.

“Ina da yakinin talakawa na tare dani, kuma shune za su fitar da dan takara a dukkan matakai, wannan karon babu batun kashe kuɗi domin sayen deliget kamar yadda ‘yan siyasa suka rinƙa yi a baya” in ji shi.

Daga ƙarshe Sanata Buba Kwacham ya nemi ‘yan siyasar Jihar Adamawa su haɗa kai tare da kai zuciya nesa domin tabbatar da zaman lafiya tare da kuma gudanar da siyasa mai tsafta.

Hattara
Bello Hamza
+ postsBio
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Hijira 1448:Za A Samu Yalwar Tattalin Arziƙi A Nijeriya —Sheikh Muhajjadina
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    NPA Ta Samar Da Tashoshin Jiragen Ruwan Da Za Su Ƙarfafa Kasuwanci Da Ƙasashen Duniya – Dantsoho
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Gwanjon Kadarori: Kotun Daukaka Kara Ta Kori Karar Da Sani Sha’aban Ya Shigar
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Amfani Da Matar Soja Wajen Isar Da Sakon Bukata

MASU ALAKA

Ndume Ya Bayyana Dalilin Da Ya Sa Yake Goyon Bayan Ƙudirin Kafa ‘Yansandan Jihohi
Manyan Labarai

Ndume Ya Bayyana Dalilin Da Ya Sa Yake Goyon Bayan Ƙudirin Kafa ‘Yansandan Jihohi

June 25, 2026
EFCC Za Ta Gurfanar Da Shugaban Miyetti Allah Kan Zargin Almundahanar Dala Miliyan 2.53
Manyan Labarai

EFCC Za Ta Gurfanar Da Shugaban Miyetti Allah Kan Zargin Almundahanar Dala Miliyan 2.53

June 25, 2026
Maroko Ta Zama Ƙasa Ta Farko Daga Afirka Da Ta Tsallaka Zuwa Zagaye Na 32 A Gasar Kofin Duniya
Labarai

Maroko Ta Zama Ƙasa Ta Farko Daga Afirka Da Ta Tsallaka Zuwa Zagaye Na 32 A Gasar Kofin Duniya

June 25, 2026
Next Post
Fintiri Ya Fice Daga PDP Zuwa APC

Fintiri Ya Fice Daga PDP Zuwa APC

LABARAI MASU NASABA

Ndume Ya Bayyana Dalilin Da Ya Sa Yake Goyon Bayan Ƙudirin Kafa ‘Yansandan Jihohi

Ndume Ya Bayyana Dalilin Da Ya Sa Yake Goyon Bayan Ƙudirin Kafa ‘Yansandan Jihohi

June 25, 2026
EFCC Za Ta Gurfanar Da Shugaban Miyetti Allah Kan Zargin Almundahanar Dala Miliyan 2.53

EFCC Za Ta Gurfanar Da Shugaban Miyetti Allah Kan Zargin Almundahanar Dala Miliyan 2.53

June 25, 2026
Maroko Ta Zama Ƙasa Ta Farko Daga Afirka Da Ta Tsallaka Zuwa Zagaye Na 32 A Gasar Kofin Duniya

Maroko Ta Zama Ƙasa Ta Farko Daga Afirka Da Ta Tsallaka Zuwa Zagaye Na 32 A Gasar Kofin Duniya

June 25, 2026
Zan Ware 10bn Don Inganta Ilimin Matasa Idan Na Ci Zabe – Atiku

‘Yan Nijeriya Ba Sa Bukatar ‘Yan Jarida Su Faɗa Musu Suna Jin Yunwa — Atiku

June 25, 2026
Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026
Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.