ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

An Nemi Tinubu Ya Sanya Baki Kan Rashin Biyan Fansho

by Sani Anwar and Sulaiman
5 months ago
tinubu

Kungiyar ’yan fansho ta Nijeriya (NUP), ta bukaci shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu, da ya tsawatar wa gwamnonin jihohin kasar, domin kawar da duk wani bashin da ‘yan fansho suke bin jihohin.

Kazalika, kungiyar ta ce; kiran nata ya zama wajibi, domin har yanzu ’yan fansho a matakin kasa da kasa, ba sa cin gajiyar sauye-sauyen da ake samu, duk da cewa; gwamnatin tarayya na ci gaba da kawo dauki ga wadanda suka yi ritaya.

  • Gwamna Uba Sani Ya Kulla Yarjejeniyar Naira Biliyan 15  Don  Inganta Wutar Lantarki  A  Kaduna
  • Sin Ta Fitar Da Mizanin Kasa Na Kyautata Nagartar Na’urar Adana Lantarki

Shugaban kungiyar na kasa, Kwamared Godwin Abumisi ne ya yi wannan kira a lokacin da yake taya shugaban kasar murnar cika shekara 74 a duniya.

ADVERTISEMENT

Sanarwar ta kara da cewa, “Kungiyar ‘yan Fansho ta Nijeriya (NUP), na taya mai girma shugaban kasa, Bola Ahmed Tinubu murnar cika shekara 74 da haihuwa.

Kungiyar ta yi nuni da cewa, a yayin da ‘yan fansho a fadin kasar nan ke taya shugaban kasar murna, saboda la’akari da manufofin da suka inganta jin dadi da martabar wadanda suka yi ritaya, hakan ba zai yiwu a jihohi ba.

LABARAI MASU NASABA

PDP Ta Musanta Mara Wa APM Baya A Bauchi

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

Da yake yin karin haske kan muhimman nasarorin da aka samu a matakin tarayya, NUP ta yi nuni da amincewa da karin kudin fansho da kimanin naira 32,000 a duk wata ga masu karbar fansho, inda ta bayyana hakan a matsayin babban taimako a cikin kalubalen tattalin arzikin da ake fuskanta a halin yanzu.

Ya kara da cewa, karin “hukunci na nuna jajircewa da jin kai, wanda ya kawo saukin da ake bukata ga wadanda suka yi ritaya da suke kokawa da tsadar rayuwa,” ya kara da cewa; hakan ya sake farfado da fata a tsakanin ‘yan fansho a fadin kasar.

Kungiyar ta kuma yaba da amincewar da gwamnatin tarayya ta yi na kimanin naira biliyan 700, don kawar da wasu basukan da ake bin su a karkashin tsarin bayar da gudunmawar fansho (CPS) da kuma naira biliyan 57 ga ‘yan fansho a karkashin tsarin (DBS), tare da lura da cewa; matakin na magance basussukan da aka dade ana bin su.

Kungiyar ta NUP, ta kara amincewa da kokarin warware basussukan da ake bin ‘yan fansho, musamman ma wadanda ke cikin ma’aikatun gwamnati a karkashin tsarin fa’ida, inda ta ce; matakin ya taimaka wajen dawo da kwarin guiwar gwamnati na aiwatar da ayyukanta.

Ta kuma yaba da yadda ake ci gaba da biyan kudaden fansho na wata-wata da kuma yadda gwamnatin tarayya ta dauki matakin magance jinkiri.

“Muna kara yaba wa ci gaba da biyan kudaden fansho na wata-wata, da kuma sanya baki wajen biya a kan lokaci, wanda hakan ya nuna kyakkyawan jagoranci.”

Yayin da take yaba wa wannan kokari, NUP ta jaddada cewa; har yanzu ‘yan fansho da dama na jihohi, ba sa cin gajiyar irin wadannan sauye-sauye, don haka akwai bukatar shugaban kasa ya shiga tsakani.

“Muna kira ga girma shugaban kasa da ya yi amfani da damar da yake da ita, don samun galaba a kan gwamnonin jihohi wajen aiwatar da cikakken karin albashin da aka amince da shi ga ‘yan fansho na jihohi, ta yadda wadanda suka yi ritaya a matakin kasa baki-daya za su amfana da wadannan sauye-sauyen,” in ji sanarwar.

Kungiyar ta kuma nanata muhimmancin bin diddigin tsarin inshorar lafiya da ake shirin yi wa ‘yan fansho.

“Mun kuma sake nanata cewa, shirin Inshorar Lafiya da aka tsara na ‘yan fansho, ya na da matukar muhimmanci. Muna fatan amincewa da shi da kuma fitar da kudade, don gaggauta aiwatar da shi nan da dan wani lokaci,” in ji ta.

Fansho
Sani Anwar
+ posts Bio
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    Ko Kun San Amfanin Kwanciya Da Bangaren Hagu?
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    2027:Mata Shida Da Ke Takarar Neman Shugabancin Nijeriya
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    Dambarwa A Kasuwancin Iyalan Indimi
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    Illar Shan Taba Sigari Da Dangoginta
Fansho
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    PDP Ta Musanta Mara Wa APM Baya A Bauchi
  • Sulaiman
    Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara
  • Sulaiman
    Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5
  • Sulaiman
    Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

MASU ALAKA

Taron PDP Na Ƙasa: Ɓangaren Wike Ya Kafa Sabon NWC A Abuja
Labarai

PDP Ta Musanta Mara Wa APM Baya A Bauchi

September 9, 2026
Sojoji
Manyan Labarai

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

September 9, 2026
'Yan Bindiga
Labarai

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Next Post
AU Ta Yi Maraba Da Shawarar Sin Da Pakistan Kan Dawo Da Zaman Lafiya A Gabas Ta Tsakiya

AU Ta Yi Maraba Da Shawarar Sin Da Pakistan Kan Dawo Da Zaman Lafiya A Gabas Ta Tsakiya

LABARAI MASU NASABA

Taron PDP Na Ƙasa: Ɓangaren Wike Ya Kafa Sabon NWC A Abuja

PDP Ta Musanta Mara Wa APM Baya A Bauchi

September 9, 2026
Sojoji

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

September 9, 2026
Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.