ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, July 15, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

An Nemi Tinubu Ya Sanya Baki Kan Rashin Biyan Fansho

by Sani Anwar and Sulaiman
3 months ago
tinubu

Kungiyar ’yan fansho ta Nijeriya (NUP), ta bukaci shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu, da ya tsawatar wa gwamnonin jihohin kasar, domin kawar da duk wani bashin da ‘yan fansho suke bin jihohin.

Kazalika, kungiyar ta ce; kiran nata ya zama wajibi, domin har yanzu ’yan fansho a matakin kasa da kasa, ba sa cin gajiyar sauye-sauyen da ake samu, duk da cewa; gwamnatin tarayya na ci gaba da kawo dauki ga wadanda suka yi ritaya.

  • Gwamna Uba Sani Ya Kulla Yarjejeniyar Naira Biliyan 15  Don  Inganta Wutar Lantarki  A  Kaduna
  • Sin Ta Fitar Da Mizanin Kasa Na Kyautata Nagartar Na’urar Adana Lantarki

Shugaban kungiyar na kasa, Kwamared Godwin Abumisi ne ya yi wannan kira a lokacin da yake taya shugaban kasar murnar cika shekara 74 a duniya.

ADVERTISEMENT

Sanarwar ta kara da cewa, “Kungiyar ‘yan Fansho ta Nijeriya (NUP), na taya mai girma shugaban kasa, Bola Ahmed Tinubu murnar cika shekara 74 da haihuwa.

Kungiyar ta yi nuni da cewa, a yayin da ‘yan fansho a fadin kasar nan ke taya shugaban kasar murna, saboda la’akari da manufofin da suka inganta jin dadi da martabar wadanda suka yi ritaya, hakan ba zai yiwu a jihohi ba.

LABARAI MASU NASABA

Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

Kotu Ta Tsare Shugaban Makaranta Da Malami Kan Zargin Lalata Da Ɗaliba Mai Shekara 6 A Gombe

Da yake yin karin haske kan muhimman nasarorin da aka samu a matakin tarayya, NUP ta yi nuni da amincewa da karin kudin fansho da kimanin naira 32,000 a duk wata ga masu karbar fansho, inda ta bayyana hakan a matsayin babban taimako a cikin kalubalen tattalin arzikin da ake fuskanta a halin yanzu.

Ya kara da cewa, karin “hukunci na nuna jajircewa da jin kai, wanda ya kawo saukin da ake bukata ga wadanda suka yi ritaya da suke kokawa da tsadar rayuwa,” ya kara da cewa; hakan ya sake farfado da fata a tsakanin ‘yan fansho a fadin kasar.

Kungiyar ta kuma yaba da amincewar da gwamnatin tarayya ta yi na kimanin naira biliyan 700, don kawar da wasu basukan da ake bin su a karkashin tsarin bayar da gudunmawar fansho (CPS) da kuma naira biliyan 57 ga ‘yan fansho a karkashin tsarin (DBS), tare da lura da cewa; matakin na magance basussukan da aka dade ana bin su.

Kungiyar ta NUP, ta kara amincewa da kokarin warware basussukan da ake bin ‘yan fansho, musamman ma wadanda ke cikin ma’aikatun gwamnati a karkashin tsarin fa’ida, inda ta ce; matakin ya taimaka wajen dawo da kwarin guiwar gwamnati na aiwatar da ayyukanta.

Ta kuma yaba da yadda ake ci gaba da biyan kudaden fansho na wata-wata da kuma yadda gwamnatin tarayya ta dauki matakin magance jinkiri.

“Muna kara yaba wa ci gaba da biyan kudaden fansho na wata-wata, da kuma sanya baki wajen biya a kan lokaci, wanda hakan ya nuna kyakkyawan jagoranci.”

Yayin da take yaba wa wannan kokari, NUP ta jaddada cewa; har yanzu ‘yan fansho da dama na jihohi, ba sa cin gajiyar irin wadannan sauye-sauye, don haka akwai bukatar shugaban kasa ya shiga tsakani.

“Muna kira ga girma shugaban kasa da ya yi amfani da damar da yake da ita, don samun galaba a kan gwamnonin jihohi wajen aiwatar da cikakken karin albashin da aka amince da shi ga ‘yan fansho na jihohi, ta yadda wadanda suka yi ritaya a matakin kasa baki-daya za su amfana da wadannan sauye-sauyen,” in ji sanarwar.

Kungiyar ta kuma nanata muhimmancin bin diddigin tsarin inshorar lafiya da ake shirin yi wa ‘yan fansho.

“Mun kuma sake nanata cewa, shirin Inshorar Lafiya da aka tsara na ‘yan fansho, ya na da matukar muhimmanci. Muna fatan amincewa da shi da kuma fitar da kudade, don gaggauta aiwatar da shi nan da dan wani lokaci,” in ji ta.

Fansho
Sani Anwar
+ posts Bio
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    Shugaban Rundunar Sojojin Nijeriya Ya Nemi Haɗin Kan Fararen Hula
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    Ƴan Ƙwadago Sun Buƙaci Naira 300,000 A Matsayin Mafi Ƙarancin Albashi
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    NiMet Ta Gargaɗi Jihohi 27 Kan Barazanar Ambaliyar Ruwa A Farkon Watan Yuli
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    2027: Masu Ruwa Da Tsaki Sun Amince Da Jamilu Gwamna A Matsayin Gwamnan Gombe
Fansho
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya
  • Sulaiman
    Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026
  • Sulaiman
    An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”
  • Sulaiman
    Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

MASU ALAKA

Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu
Labarai

Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

July 14, 2026
Katsina: Kotu Ta Yanke Wa Hauwa’u Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya Kan Taimaka Wa ’Yan Bindiga
Manyan Labarai

Kotu Ta Tsare Shugaban Makaranta Da Malami Kan Zargin Lalata Da Ɗaliba Mai Shekara 6 A Gombe

July 14, 2026
Nijeriya da Masar Sun Ƙulla Haɗin Gwiwa Domin Yaƙi da Miyagun Ƙwayoyi
Labarai

Nijeriya da Masar Sun Ƙulla Haɗin Gwiwa Domin Yaƙi da Miyagun Ƙwayoyi

July 14, 2026
Next Post
AU Ta Yi Maraba Da Shawarar Sin Da Pakistan Kan Dawo Da Zaman Lafiya A Gabas Ta Tsakiya

AU Ta Yi Maraba Da Shawarar Sin Da Pakistan Kan Dawo Da Zaman Lafiya A Gabas Ta Tsakiya

LABARAI MASU NASABA

Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

July 14, 2026
Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

July 14, 2026
An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

July 14, 2026
Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

July 14, 2026
Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

July 14, 2026
Katsina: Kotu Ta Yanke Wa Hauwa’u Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya Kan Taimaka Wa ’Yan Bindiga

Kotu Ta Tsare Shugaban Makaranta Da Malami Kan Zargin Lalata Da Ɗaliba Mai Shekara 6 A Gombe

July 14, 2026
An Bankado Muguwar Aniyar Japan Ta Haifar Da Tashin Hankali A Tekun Kudancin Sin

An Bankado Muguwar Aniyar Japan Ta Haifar Da Tashin Hankali A Tekun Kudancin Sin

July 14, 2026
Layin Dogo Tsakanin Tanzaniya Da Zambiya Ya Zama Shaidar Abota Tsakanin Sin Da Afirka

Layin Dogo Tsakanin Tanzaniya Da Zambiya Ya Zama Shaidar Abota Tsakanin Sin Da Afirka

July 14, 2026
Nijeriya da Masar Sun Ƙulla Haɗin Gwiwa Domin Yaƙi da Miyagun Ƙwayoyi

Nijeriya da Masar Sun Ƙulla Haɗin Gwiwa Domin Yaƙi da Miyagun Ƙwayoyi

July 14, 2026
CMG Ya Gudanar Da Babban Taron Masu Kirkirar Manyan Shirye-Shirye Da Fina-Finai

CMG Ya Gudanar Da Babban Taron Masu Kirkirar Manyan Shirye-Shirye Da Fina-Finai

July 14, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.