ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

An Nemi Tinubu Ya Sanya Baki Kan Rashin Biyan Fansho

by Sani Anwar and Sulaiman
3 months ago
tinubu

Kungiyar ’yan fansho ta Nijeriya (NUP), ta bukaci shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu, da ya tsawatar wa gwamnonin jihohin kasar, domin kawar da duk wani bashin da ‘yan fansho suke bin jihohin.

Kazalika, kungiyar ta ce; kiran nata ya zama wajibi, domin har yanzu ’yan fansho a matakin kasa da kasa, ba sa cin gajiyar sauye-sauyen da ake samu, duk da cewa; gwamnatin tarayya na ci gaba da kawo dauki ga wadanda suka yi ritaya.

  • Gwamna Uba Sani Ya Kulla Yarjejeniyar Naira Biliyan 15  Don  Inganta Wutar Lantarki  A  Kaduna
  • Sin Ta Fitar Da Mizanin Kasa Na Kyautata Nagartar Na’urar Adana Lantarki

Shugaban kungiyar na kasa, Kwamared Godwin Abumisi ne ya yi wannan kira a lokacin da yake taya shugaban kasar murnar cika shekara 74 a duniya.

ADVERTISEMENT

Sanarwar ta kara da cewa, “Kungiyar ‘yan Fansho ta Nijeriya (NUP), na taya mai girma shugaban kasa, Bola Ahmed Tinubu murnar cika shekara 74 da haihuwa.

Kungiyar ta yi nuni da cewa, a yayin da ‘yan fansho a fadin kasar nan ke taya shugaban kasar murna, saboda la’akari da manufofin da suka inganta jin dadi da martabar wadanda suka yi ritaya, hakan ba zai yiwu a jihohi ba.

LABARAI MASU NASABA

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Da yake yin karin haske kan muhimman nasarorin da aka samu a matakin tarayya, NUP ta yi nuni da amincewa da karin kudin fansho da kimanin naira 32,000 a duk wata ga masu karbar fansho, inda ta bayyana hakan a matsayin babban taimako a cikin kalubalen tattalin arzikin da ake fuskanta a halin yanzu.

Ya kara da cewa, karin “hukunci na nuna jajircewa da jin kai, wanda ya kawo saukin da ake bukata ga wadanda suka yi ritaya da suke kokawa da tsadar rayuwa,” ya kara da cewa; hakan ya sake farfado da fata a tsakanin ‘yan fansho a fadin kasar.

Kungiyar ta kuma yaba da amincewar da gwamnatin tarayya ta yi na kimanin naira biliyan 700, don kawar da wasu basukan da ake bin su a karkashin tsarin bayar da gudunmawar fansho (CPS) da kuma naira biliyan 57 ga ‘yan fansho a karkashin tsarin (DBS), tare da lura da cewa; matakin na magance basussukan da aka dade ana bin su.

Kungiyar ta NUP, ta kara amincewa da kokarin warware basussukan da ake bin ‘yan fansho, musamman ma wadanda ke cikin ma’aikatun gwamnati a karkashin tsarin fa’ida, inda ta ce; matakin ya taimaka wajen dawo da kwarin guiwar gwamnati na aiwatar da ayyukanta.

Ta kuma yaba da yadda ake ci gaba da biyan kudaden fansho na wata-wata da kuma yadda gwamnatin tarayya ta dauki matakin magance jinkiri.

“Muna kara yaba wa ci gaba da biyan kudaden fansho na wata-wata, da kuma sanya baki wajen biya a kan lokaci, wanda hakan ya nuna kyakkyawan jagoranci.”

Yayin da take yaba wa wannan kokari, NUP ta jaddada cewa; har yanzu ‘yan fansho da dama na jihohi, ba sa cin gajiyar irin wadannan sauye-sauye, don haka akwai bukatar shugaban kasa ya shiga tsakani.

“Muna kira ga girma shugaban kasa da ya yi amfani da damar da yake da ita, don samun galaba a kan gwamnonin jihohi wajen aiwatar da cikakken karin albashin da aka amince da shi ga ‘yan fansho na jihohi, ta yadda wadanda suka yi ritaya a matakin kasa baki-daya za su amfana da wadannan sauye-sauyen,” in ji sanarwar.

Kungiyar ta kuma nanata muhimmancin bin diddigin tsarin inshorar lafiya da ake shirin yi wa ‘yan fansho.

“Mun kuma sake nanata cewa, shirin Inshorar Lafiya da aka tsara na ‘yan fansho, ya na da matukar muhimmanci. Muna fatan amincewa da shi da kuma fitar da kudade, don gaggauta aiwatar da shi nan da dan wani lokaci,” in ji ta.

Fansho
Sani Anwar
+ posts Bio
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    Tattalin Arziƙin Ƙasa: Masana Sun Buƙaci Tinubu Ya Yi Hattara Da Shawarar IMF
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    Cututtukan Da Aka Fi Fama Da Su Lokacin Damina Da Yadda Za A Kauce Musu (2)
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    Cututtukan Da Aka Fi Fama Da Su Lokacin Damina Da Yadda Za A Kauce Musu (1)
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    Talauci Ya Sake Karuwa Da Kashi 63 Duk Da Sauye-sauyen Tattalin Arzikin Da Gwamnati Ta Yi – IMF
Fansho
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace
  • Sulaiman
    ’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin
  • Sulaiman
    Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi
  • Sulaiman
    Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

MASU ALAKA

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi
Labarai

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”
Ra'ayi Riga

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma
Labarai

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Next Post
AU Ta Yi Maraba Da Shawarar Sin Da Pakistan Kan Dawo Da Zaman Lafiya A Gabas Ta Tsakiya

AU Ta Yi Maraba Da Shawarar Sin Da Pakistan Kan Dawo Da Zaman Lafiya A Gabas Ta Tsakiya

LABARAI MASU NASABA

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026
Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026
Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

June 24, 2026
Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.