An tsaurara matakan tsaro a sakatariyar jam’iyyar APC da ke jihar Kaduna ranar Asabar yayin da jam’iyyar ta fara gudanar da zaɓen fidda gwani cikin yanayin zafin siyasar neman takara a zaben 2027.
Jami’an tsaro da aka jibge a ƙofar sakatariyar sun hana duk wanda ba a ba izini ba shiga harabar wajen, suna jaddada cewa babu wanda aka amince ya shiga cikin ginin a lokacin gudanar da zaɓen.
Lokacin da wakilinmu ya kai ziyara wurin, an ga jami’an tsaro masu ɗauke da makamai suna gudanar da tsauraran sintiri a kusa da sakatariyar, yayin da magoya bayan jam’iyyar da wasu mazauna yankin suka taru daga nesa suna kallon yadda abubuwa ke gudana.
Matakin hana shiga ya haifar da ruɗani a yankin, inda jami’an tsaro ke mayar da mutane da dama da suka yi ƙoƙarin shiga harabar wajen.
Wani jami’in tsaro da ke bakin ƙofar ya shaida wa manema labarai cewa an ɗauki matakin ne domin tabbatar da zaman lafiya da hana duk wata tarzoma yayin gudanar da zaɓen fidda gwanin, yayin da ake kuma sanya ido sosai kan zirga-zirgar ababen hawa a yankin.















Discussion about this post