ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Anya, Guguwar Tsige Shugabannin Jam’iyya Ba Za Ta Ci Adamu Da Ayu Ba?

by Yusuf Shuaibu
4 years ago
Ayu

A yanzu abun da ke bayyana a bangaren siyasa shi ne yadda rigingimu suka dabaibaye shugabancin jam’iyyun APC da PDP, duk da cewa wadanda ake rigima a kansu sun kai shekara daya a kan karagar mulkin da suke kai, shugaban jam’iyyar APC ta kasa, Sanata Abdullahi Adamu da takwaransa na PDP Ayiochia Ayu suna fusakantar kalubale.

Jam’iyyar PDP ta gudanar da babban taronta na kasa a watan Oktoba da ya gabata, wanda taron ya bata wa wasu da dama rai don ba su sami abun da suke bukata ba. Bayan watanni kadan, wannann abu na rashin jituwa ta kai da korar tsohon shugaban jam’iyyar na kasa, Uche Sencondus daga jam’iyyar.

  • Wani Makusancin Gwwamna Wike, Prince Nwiyor, Ya Fice Daga PDP Ya Koma APC

Ayu ya zama shugaban jam’iyyar PDP na kasa ta hanyar tsohuwar al’adar jam’iyyar na yin masalaha a tsakanin ‘ya’yan jam’iyyar.

ADVERTISEMENT

Ayu da manyan jami’an jam’iyyar 19 daga cikin 21 duk suna kan wannan matsayin da suke ne ta hanyar maslaha. Babban abun da ya kamata jam’iyyar adawa ta kasance ta samu shi ne, samun hadin kai a tsakanin ‘ya’yata wanda hakan zai ba ta damar iya fuskanbtar kalubalen da ke gabansu, amma akasin haka za ta kasance cikin mawuyacin hali.

Watanni kadan bayan gudanar da zaben fid da gwani na shugaban kasa, jam’iyyar ta kara fadawa rikicin cikin gida na rarrabuwan kawuna tsakanin dan takarar shugaban kasa Atiku Abubakar da Gwamnan Jihar Ribas, Nyesom Wike, wanda har lamarin ya bijiro da batun tsige shugaban jam’iyyar na kasa, a matsayin hanya daya da zai zaunar da shi tare da magoya bayansa daga cikin jam’iyyar.

LABARAI MASU NASABA

Yadda Matsin Lamba Ta Sa Amaechi Ya Amince Ya Zama Abokin Takarar Atiku

2027: Kallo Ya Koma Kan Yadda APC, ADC Da PDP Ke Neman Abokan Takarar Mataimakin Shugaban Kasa

Idan har za a bijiro da batun tsige shugaban jam’iyya tun yanzu, wannan yana nuna cewa jam’iyyar tana iya samun nasarar cire dukkan masu rige da mukamai kafin wa’adin mulkinsu ya kare.
Magabatan shugabannin jam’iyyar PDP kamar irinsu Solomon Lar, Barnabas Gemade, Audu Ogbeh, Ahmadu Ali, Bincent Ogubulafor, Okwesilieze Nwodo, Bamanga Tukur, Ahmodu Sheriff da kuma Secondus, shugaban jam’iyyar PDP guda daya ne kacal ya samu nasarar kammala wa’adin mulkinsa shi ne Ali.

Tun daga lokacinsa har zuwa yau shekaru 24 da suka gabata babu wanda ya samu nasarar kammala wa’adin mulkinsa.

Tun daga lokacin da aka gudanar da zaben fid da gwani a cikin jam’iyyar, abubuwa ba sa tafiya yadda ya kamata, inda jam’iyyar ta mayar da hankali wajen sasanta Atiku da Wike, ganin yadda Wike ya fusata.

Wakazalika, ita ma jam’iyya mai mulki ta APC tana fuskantar kalubale a kan takarar Musulmi da Musulmi, lamarin da ya haddasa rarrabuwar kawuna da rashin bayayya ga shugaban jam’iyyar da dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar Asiwaju Bola Tinubu, wanda yake kokarin girgiza kujerar shugaban jam’iyyar na kasa, Sanata Abdullahi Adamu.

A cikin shekaru takwas, jam’iyyar APC ta yi shugabanni har guda biyar wadanda suka hada da Bisi Akande, John Oyegun, Adams Oshiomhole, Mai Buni da kuma Adamu.

A makon da ya gabata ne, alamu sun nana cewa gwamnonin jam’iyyar APC da wasu masu ruwa da tsaki suka zargi Adamu da rashin yin adalci tun lokacin da ya zama shugaban jam’iyyar.

An dai zabi Adamu a matsayin shugaban jam’iyyar APC ne a watan Maris duk da irin babban adawar da yake da shi a wurin gwamnonin jam’iyyar.

Adamu dai ya samu goyon bayan Shugaban kasa Muhammadu Buhari wajen doke abokin takararsa Tanko Al-Makura, tsohon gwamnan Jihar Nasarawa kuma a yanzu ya kasance sanata, wanda shi ne gwamnonin APC da manyan masu ruwa da tsaki suka mara wa baya.

APC tana ta kokarin dawo da lamara daidai tun bayan zaben fid da gwani na shugaban kasa, amma kuma a yanzu haka an samu sabuwar rarrabuwan kawuna a cikin jam’iyyar na tsige Adamu daga kan mukaminsa kafin gudanar da babban zabe a shekara mai zuwa.

A bangaren jam’iyyar PDP, dan takarar shugaban kasa Atiku Abubakar da Gwamnan Jihar Ribas, Nyesom Wike sun kasance manyan masu jayayya a tsakani.

Wike wanda ya tsaya takarar shugaban kasa a karkashin jam’iyyar PDP, wanda ya samu rashin narasa daga wajen Atiku a watan Afrilu a zaben fid da gwani.

Ya bayyana cewa Atiku ya yi masa alkawarin zai ba shi gurbin takarar mataimakin shugaban kasa saboda kokarin da ya gudanar. Mafi yawancin manyan shugabannin jam’iyyar sun goyi bayan hakan ciki har da gwamnonin jam’iyyar.

Amma kwatsam sai Atiku ya bai wa Gwamnan Jihar Delta, Ifeanyi Okowa mataimakinsa, lamarin da ya haddasa rabuwan kai tsakaninsa da Wike.
A cewar Gwamnan Jihar Benuwe, Samuel Ortom, a cikin mambobin kwamitin PDP mai mutum 17, 14 daga ciki sun amince a bai wa Wike mataimakin shugaban kasa.

Ortom ya bayyana hakan ne a wata zantawa da gidan talabijin ta yi da shi, inda ya ce an zantar da shawarar cewa gwamnan Jihar Ribas ne mataimakin kafin lokacin da aka fitar da sunan Okowa.

Tun daga wannan lokacin ne Wike ya fara mu’amula da gwamnonin jam’iyyar APC da wasu masu ruwa da tsaki da ke cikin jam’iyyar, musamman wajen kaddamar da ayyukansa a Jihar Ribas.

A yanzu haka akwai kalubale a kan Ayu na ya sauka daga mukaminsa bisa yarjejeniyar cewa idan aka samu dan takarar shugaban kasa daga yankin arewa.

Magoya bayan Wike sun dage a kan sai Ayu ya sauka daga mukaminsa a matsayin matakin da zai goyi bayan Atiku a zaben shugaban kasa na 2023.

Sai dai kuma a cewar mai taimaka wa Ayu kan fannin yada labarai, Simon Imobo-Tswam, ya bayyana cewa shugaban jam’iyyar PDP, Iyiochia Ayu ba zai sauka daga kan mukaminsa ba, kuma babu wani shiri na ya sauka, domin an zabe shi ne na tsawan shekaru hudu.

Haka ma lamarin yake a bangaren APC na sai shugaban jam’iyyar na kasa, Abdullahi Adamu ya sauka daga kan mukaminsa. Jam’iyyar ta yi burus kan rahoton karaye-kiraye na cire Abdullahi Adamu daga mukaminsa.

Sakataren yada labarai na jam’iyyar, Felid Morka ya bayyana cewa jam’iyyun adawa ne suke daukan nauyin rahotonnin da ke cewa dole sai shugaban ya sauka daga kan mukaminsa.

Adamu kamar dai Ayu wanda ya karya tsarin karba-karba na dan takarar shugaban kasa a PDP da ya fito daga arewa maimakon kudu, wanda mutanen yankin suke ganin su ne ya kamata su fitar da shugaban kasa, suna fuskantar kalubale a dukkan bangarorin jam’iyyun wanda ake ganin da wahala su kai babban zabe na watan Fabrairun 2023 a kan mukamansu.

Hakika jam’iyyun APC da PDP suna cikin hatsari wanda komi zai iya faruwa da dukkan jam’iyyun guda, wanda lokaci ne kadai zai iya tabbatar da hakan.

Ayu
Yusuf Shuaibu
+ postsBio
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Rashin Tsaro Na Barazana Ga Zaben 2027 —Rahotanni
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Yadda Matsin Lamba Ta Sa Amaechi Ya Amince Ya Zama Abokin Takarar Atiku
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    2027: Kallo Ya Koma Kan Yadda APC, ADC Da PDP Ke Neman Abokan Takarar Mataimakin Shugaban Kasa
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Ko INEC Na Da Hannu A Rikice-rikicen Jam’iyyun Siyasa A Nijeriya?

MASU ALAKA

Yadda Matsin Lamba Ta Sa Amaechi Ya Amince Ya Zama Abokin Takarar Atiku
Tambarin Dimokuradiyya

Yadda Matsin Lamba Ta Sa Amaechi Ya Amince Ya Zama Abokin Takarar Atiku

June 19, 2026
2027: Kallo Ya Koma Kan Yadda APC, ADC Da PDP Ke Neman Abokan Takarar Mataimakin Shugaban Kasa
Tambarin Dimokuradiyya

2027: Kallo Ya Koma Kan Yadda APC, ADC Da PDP Ke Neman Abokan Takarar Mataimakin Shugaban Kasa

June 12, 2026
Ko INEC Na Da Hannu A Rikice-rikicen Jam’iyyun Siyasa A Nijeriya?
Tambarin Dimokuradiyya

Ko INEC Na Da Hannu A Rikice-rikicen Jam’iyyun Siyasa A Nijeriya?

June 12, 2026
Next Post
Xi Ya Karfafa Gwiwar Kwararrun Kasashen Waje Da Su Kara Ba Da Gudummawa Wajen Inganta Mu’amala Tsakanin Sin Da Sauran Kasashe

Xi Ya Karfafa Gwiwar Kwararrun Kasashen Waje Da Su Kara Ba Da Gudummawa Wajen Inganta Mu'amala Tsakanin Sin Da Sauran Kasashe

LABARAI MASU NASABA

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026
Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026
Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

June 24, 2026
Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.