Jam’iyyar APC ta dakatar da sanatan da ke wakiltar mazabar Kogi ta Gabas, Jibrin Isah Echocho, bisa zargin aikata ayyukan da suka saɓawa muradun jam’iyyar.
Matakin ya biyo bayan ƙudirin kwamitin zartarwa na jam’iyyar a Odu Ward 2 da ke ƙaramar hukumar Dekina, wanda ya zargi sanatan da gudanar da abin da ya kira shafe dogon lokaci yana aiyukan adawa da jam’iyya domin cimma burin sake komawa majalisa karo na uku.
A cikin wasiƙar dakatarwar da shugaban mazaɓar, Shaibu Mohammed, da sakataren mazaɓar, Kabiru Mohammed, suka sanya wa hannu, jam’iyyar ta ce sanatan ya daɗe yana aiki da ya saɓa wa muradun APC duk da amfana da dandamalinta tsawon shekaru takwas.
Sai dai ƙungiyar Kogi East Progressive Forum ta yi watsi da dakatarwar, tana mai cewa haramtacciya ce. Kakakin kungiyar, Musa Ibrahim, ya ce babu wata hukuma ta mazaɓarsa da ke da ikon dakatar da sanata mai ci ba tare da bin matakan da kundin tsarin jam’iyya ya tanada ba.
Wannan na zuwa ne bayan da Jibrin Isah Echocho ya yi korafi kan yadda aka gudanar da zaɓen fidda gwani na APC a mazabar Kogi ta Gabas, inda ya ce an karya dokokin jam’iyyar da na zaɓe. Zaɓen dai ya bai wa Joseph Erico Ameh tikitin takarar sanata na jam’iyyar.















Discussion about this post