ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Arewa Maso Gabashin Jigawa: Abokan Babandede Sun Dauki Harama

by Yusuf Shuaibu
7 months ago
Jigawa

LABARAI MASU NASABA

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

Kungiyar abokan tsohon shugaban hukumar shige da fice ta kasa (NIS), CGI Babandede mai ritaya (FOMB) da ke yakin ganin ya zaman sanata a yankin arewa maso gabashin Jigawa sun dauki harama wajen ganin hakarsu ta cimma ruwa.

Kungiya ta kasance ta abokai da magoya baya da abokan aiki da kuma ma’aikatan da suka taba aiki karkashin jagorancin tsohon shugaban hukumar NIS), CGI Babandede mai ritaya, wanda shi ne shugaban hukumar na 16 wanda ya zamanatar da aiki hukumar a karkashin jagorancinsa.

  • 2027: Dole Dattawan Arewa Su Hada Kai Domin Samar Wa Yankin Mafita —Alhaji Babangida Aliyu
  • Ronaldo Ba Shi Da Ikon Yanke Hukunci A Gasar Saudi Pro League – Mahukunta

Me ya sa Muhammad Babandede yake da muhimmanci na musamman?

A tsakanin shekarun 2017 zuwa 2021, ya sauya tsarin aiki da gudanarwa na hukumar shige da fice ta Nijeriya ta hanyar fasahar zamani, har ta zama hukuma mai kima da ake misali da ita a duk fadin Afirka.

Nijeriya ta zama kasa ta farko a Afirka da ta kaddamar da amfani da ingantaccen tsarin yin fasfo na zamani, inda aka fara ba wa tsohon shugaban kasa, Marigayi Muhammadu Buhari da mataimakinsa, Farfesa Yemi Osinbajo (SAN), fasfo dinsu a fadar shugaban kasa da ke Abuja. Wannan ya nuna kaddamar da ingantaccen fasfo nazamani shi ne irinsa na farko a Afirka a shekarar 2019.

Haka kuma, an samar da tsarin nan na e-bisa da biyan kudi ta intanet (online payment) don fasfo da sauran ayyukan da hukumar ke bayarwa ga jama’a a zamanance kuma a saukake.

An kuma gabatar da na’urar auto-gate a wasu manyan filayen jiragen sama na kasa da kasa, tare da tsarin sa ido da gudanarwa ta intanet kan shigowa da hana shigowa ga matafiya na kasashen waje gwargwadon hali.

Wannan ya taimaka wajen inganta matsayin tsaron shige da fice na Nijeriya a idon duniya, ta hanyar kama mutane da suka karya doka da hana tafiye-tafiye ba bisa ka’ida ba da hana shigowa kasar barkatai da kwace fasfo na manyan mutane masu matsayi a siyasa da iyalansu bisa ka’idojin hukumar da kuma yarjejeniyar fahimtar juna (MOU) da sauran hukumomin tsaro da ma’aikatun gwamnati ciki har da ONSA, NPF, EFCC, ICPC, DFIU, Sojoji, DSS, NIA, DIA da sauransu, domin kare muradun kasar nan.

An kuma gabatar da tsarin gudanar da kundaye ta lantarki a hukumance domin adanawa da karba da sarrafawa da amincewa da wasiku ta hanyar lantarki.

Wannan ya rage bata lokaci da karfin aiki, tare da kawar da jinkiri da bacewar wasu kundaye da aka adana su yayin da aka yi kokarin tabbatar da gaskiya da rikon amana da ingantaccen aiki.

Haka kuma ana samar da rahoton shekara-shekara tare da raba shi ga fadar shugaban kasa da sauran ma’aikartu da hukumomin gwamnati da rundunar sojoji da hukumomi da masu gudanarwa domin tantancewa da bitar ayyukan hukumar a kowacce shekara.

Baya ga wadannan kuma, ana fitar da mujallar hukumar mai taken “Gatekeepers” kowane wata, ana raba wa fadar shugaban kasa da ma’aikatun gwamnati da ofisoshin jakadanci da sojoji da hukumomi da masu samar da hidima da kuma jama’a, domin wayar da kai da bayar da bayanai kan ayyukan hukumar shige da fice ta Nijeriya.

Muhammad Babandede ya zamanantar da hukumar shige da fice ta karni na 21, tare da gina ginin fasaha irinsa na farko a hedikwatar hukumar da ke kan titin zuwa filin jirgin saman a kasa da kasa da ke Abuja.

Haka kuma, ya bar kwararrun jami’ai da ma’aikata masu kwazo da jajircewa da ke aiki da jami’an tsaron hadin gwiwa (JTF) da masu lura da kan iyakokin kasa da shingayen binciken ababen hawa da muhimman wuraren tsallaka iyaka.

Sannan kuma Muhammad Babandede ya kafa cibiyar kula da tsaro mai inganci a hedikwatar hukumar kula da shige da fice ta kasa domin sa ido kan ayyukan jami’ai da zirga-zirgar iyaka a kokarin amfani da sabbin fasahohi domin sintiri da kula da iyakokin Nijeriya.

Kamar yadda tsohon mai magana da yawun hukumar NIS kuma shugaban kafar sadarwa ta Hallbibe, James Sunday, FCAI, MNIIA ya rubuta.

Jigawa
Yusuf Shuaibu
+ postsBio
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    2027: APC Na Fuskantar Matsin Lamba Kan Sake Fasalin Tawagar Yakin Neman Zabe
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Cacar Baki Ta Kaure Tsakanin APC Da ‘Yan Adawa Kan Tallafin Gwamnatin Tarayya Ga Magidanta
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    INEC Ta Zayyano Kalubalen Da Ke Iya Shafar Sahihancin Zaben 2027
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    2027:Kamun Ludayin Yakin Neman Zaben Manyan ‘Yan Takarar Shugaban Kasa
ADVERTISEMENT

MASU ALAKA

'Yan Bindiga
Labarai

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina
Labarai

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare
Labarai

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026
Next Post
Sojoji Sun Kashe Ɗan Fashi, Sun Kama Ɓarayin Shanu A Binuwe Da Nasarawa

Sojoji Sun Kashe Ɗan Fashi, Sun Kama Ɓarayin Shanu A Binuwe Da Nasarawa

LABARAI MASU NASABA

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026
Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

September 8, 2026
Wani Soja Ya Kashe Kansa Bayan Kashe Matarsa A Jihar Neja

Kano Za Ta Kafa Sansanonin Sojoji A Ƙananan Hukumomin Da Ke Fuskantar Barazanar Tsaro

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.