ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Tuesday, July 14, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Arewa Maso Gabashin Jigawa: Abokan Babandede Sun Dauki Harama

by Yusuf Shuaibu
5 months ago
Jigawa

LABARAI MASU NASABA

Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

Kotu Ta Tsare Shugaban Makaranta Da Malami Kan Zargin Lalata Da Ɗaliba Mai Shekara 6 A Gombe

Kungiyar abokan tsohon shugaban hukumar shige da fice ta kasa (NIS), CGI Babandede mai ritaya (FOMB) da ke yakin ganin ya zaman sanata a yankin arewa maso gabashin Jigawa sun dauki harama wajen ganin hakarsu ta cimma ruwa.

Kungiya ta kasance ta abokai da magoya baya da abokan aiki da kuma ma’aikatan da suka taba aiki karkashin jagorancin tsohon shugaban hukumar NIS), CGI Babandede mai ritaya, wanda shi ne shugaban hukumar na 16 wanda ya zamanatar da aiki hukumar a karkashin jagorancinsa.

  • 2027: Dole Dattawan Arewa Su Hada Kai Domin Samar Wa Yankin Mafita —Alhaji Babangida Aliyu
  • Ronaldo Ba Shi Da Ikon Yanke Hukunci A Gasar Saudi Pro League – Mahukunta

Me ya sa Muhammad Babandede yake da muhimmanci na musamman?

A tsakanin shekarun 2017 zuwa 2021, ya sauya tsarin aiki da gudanarwa na hukumar shige da fice ta Nijeriya ta hanyar fasahar zamani, har ta zama hukuma mai kima da ake misali da ita a duk fadin Afirka.

Nijeriya ta zama kasa ta farko a Afirka da ta kaddamar da amfani da ingantaccen tsarin yin fasfo na zamani, inda aka fara ba wa tsohon shugaban kasa, Marigayi Muhammadu Buhari da mataimakinsa, Farfesa Yemi Osinbajo (SAN), fasfo dinsu a fadar shugaban kasa da ke Abuja. Wannan ya nuna kaddamar da ingantaccen fasfo nazamani shi ne irinsa na farko a Afirka a shekarar 2019.

Haka kuma, an samar da tsarin nan na e-bisa da biyan kudi ta intanet (online payment) don fasfo da sauran ayyukan da hukumar ke bayarwa ga jama’a a zamanance kuma a saukake.

An kuma gabatar da na’urar auto-gate a wasu manyan filayen jiragen sama na kasa da kasa, tare da tsarin sa ido da gudanarwa ta intanet kan shigowa da hana shigowa ga matafiya na kasashen waje gwargwadon hali.

Wannan ya taimaka wajen inganta matsayin tsaron shige da fice na Nijeriya a idon duniya, ta hanyar kama mutane da suka karya doka da hana tafiye-tafiye ba bisa ka’ida ba da hana shigowa kasar barkatai da kwace fasfo na manyan mutane masu matsayi a siyasa da iyalansu bisa ka’idojin hukumar da kuma yarjejeniyar fahimtar juna (MOU) da sauran hukumomin tsaro da ma’aikatun gwamnati ciki har da ONSA, NPF, EFCC, ICPC, DFIU, Sojoji, DSS, NIA, DIA da sauransu, domin kare muradun kasar nan.

An kuma gabatar da tsarin gudanar da kundaye ta lantarki a hukumance domin adanawa da karba da sarrafawa da amincewa da wasiku ta hanyar lantarki.

Wannan ya rage bata lokaci da karfin aiki, tare da kawar da jinkiri da bacewar wasu kundaye da aka adana su yayin da aka yi kokarin tabbatar da gaskiya da rikon amana da ingantaccen aiki.

Haka kuma ana samar da rahoton shekara-shekara tare da raba shi ga fadar shugaban kasa da sauran ma’aikartu da hukumomin gwamnati da rundunar sojoji da hukumomi da masu gudanarwa domin tantancewa da bitar ayyukan hukumar a kowacce shekara.

Baya ga wadannan kuma, ana fitar da mujallar hukumar mai taken “Gatekeepers” kowane wata, ana raba wa fadar shugaban kasa da ma’aikatun gwamnati da ofisoshin jakadanci da sojoji da hukumomi da masu samar da hidima da kuma jama’a, domin wayar da kai da bayar da bayanai kan ayyukan hukumar shige da fice ta Nijeriya.

Muhammad Babandede ya zamanantar da hukumar shige da fice ta karni na 21, tare da gina ginin fasaha irinsa na farko a hedikwatar hukumar da ke kan titin zuwa filin jirgin saman a kasa da kasa da ke Abuja.

Haka kuma, ya bar kwararrun jami’ai da ma’aikata masu kwazo da jajircewa da ke aiki da jami’an tsaron hadin gwiwa (JTF) da masu lura da kan iyakokin kasa da shingayen binciken ababen hawa da muhimman wuraren tsallaka iyaka.

Sannan kuma Muhammad Babandede ya kafa cibiyar kula da tsaro mai inganci a hedikwatar hukumar kula da shige da fice ta kasa domin sa ido kan ayyukan jami’ai da zirga-zirgar iyaka a kokarin amfani da sabbin fasahohi domin sintiri da kula da iyakokin Nijeriya.

Kamar yadda tsohon mai magana da yawun hukumar NIS kuma shugaban kafar sadarwa ta Hallbibe, James Sunday, FCAI, MNIIA ya rubuta.

Jigawa
Yusuf Shuaibu
+ postsBio
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Amurka Ta Yi Alƙawarin Sa Ido Sosai A Zaɓen Nijeriya Na 2027
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Sautin Muryar Da Aka Fallasa Kan El-Rufai Ya Haifar Da Zazzafar Muhawara
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Ci-ma-zaunen Ƴan Siyasa Ne Ke Tunanin Yin Maguɗi A Zaɓen 2027 – Makarfi
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    An Samu Ruɗani Kan Rashin Bayyana Jerin Ƴan Takarar Jam’iyyun Siyasa Na Zaɓen 2027
ADVERTISEMENT

MASU ALAKA

Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu
Labarai

Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

July 14, 2026
Katsina: Kotu Ta Yanke Wa Hauwa’u Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya Kan Taimaka Wa ’Yan Bindiga
Manyan Labarai

Kotu Ta Tsare Shugaban Makaranta Da Malami Kan Zargin Lalata Da Ɗaliba Mai Shekara 6 A Gombe

July 14, 2026
Nijeriya da Masar Sun Ƙulla Haɗin Gwiwa Domin Yaƙi da Miyagun Ƙwayoyi
Labarai

Nijeriya da Masar Sun Ƙulla Haɗin Gwiwa Domin Yaƙi da Miyagun Ƙwayoyi

July 14, 2026
Next Post
Sojoji Sun Kashe Ɗan Fashi, Sun Kama Ɓarayin Shanu A Binuwe Da Nasarawa

Sojoji Sun Kashe Ɗan Fashi, Sun Kama Ɓarayin Shanu A Binuwe Da Nasarawa

LABARAI MASU NASABA

Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

July 14, 2026
Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

July 14, 2026
Katsina: Kotu Ta Yanke Wa Hauwa’u Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya Kan Taimaka Wa ’Yan Bindiga

Kotu Ta Tsare Shugaban Makaranta Da Malami Kan Zargin Lalata Da Ɗaliba Mai Shekara 6 A Gombe

July 14, 2026
An Bankado Muguwar Aniyar Japan Ta Haifar Da Tashin Hankali A Tekun Kudancin Sin

An Bankado Muguwar Aniyar Japan Ta Haifar Da Tashin Hankali A Tekun Kudancin Sin

July 14, 2026
Layin Dogo Tsakanin Tanzaniya Da Zambiya Ya Zama Shaidar Abota Tsakanin Sin Da Afirka

Layin Dogo Tsakanin Tanzaniya Da Zambiya Ya Zama Shaidar Abota Tsakanin Sin Da Afirka

July 14, 2026
Nijeriya da Masar Sun Ƙulla Haɗin Gwiwa Domin Yaƙi da Miyagun Ƙwayoyi

Nijeriya da Masar Sun Ƙulla Haɗin Gwiwa Domin Yaƙi da Miyagun Ƙwayoyi

July 14, 2026
CMG Ya Gudanar Da Babban Taron Masu Kirkirar Manyan Shirye-Shirye Da Fina-Finai

CMG Ya Gudanar Da Babban Taron Masu Kirkirar Manyan Shirye-Shirye Da Fina-Finai

July 14, 2026
Tsohon Sanatan Gombe, Bayero Nafada, Ya Fice Daga PDP Bayan Ganawa da Shugabannin APC

Tsohon Sanatan Gombe, Bayero Nafada, Ya Fice Daga PDP Bayan Ganawa da Shugabannin APC

July 14, 2026
ADC Ta Nemi A Binciki Nafiu Bala Bayan INEC Ta Ƙaryata Iƙirarinsa

ADC Ta Nemi A Binciki Nafiu Bala Bayan INEC Ta Ƙaryata Iƙirarinsa

July 14, 2026
Sojoji Sun Kashe ’Yan Ta’adda 3, Sun Ƙwato Makamai A Sakkwato

Sojoji Sun Daƙile Harin ISWAP A Borno

July 14, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.