ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, June 24, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Asiri Ya Tonu: Yadda Aka Kashe Uwa da Ƴaƴanta Shida A Kano

by Abubakar Sulaiman
5 months ago
Kano

Mazauna unguwar Dorayi Chiranchi a birnin Kano sun bayyana yadda aka aikata mummunan kisan da ya yi sanadiyyar mutuwar wata mata, Fatima Abubakar mai shekara 35, da ƴaƴanta shida. An ce maharan sun kutsa cikin gidansu a Dorayi Gidan Kwari, suka kulle gidan kafin su kashe su, sannan suka yi ƙoƙarin ƙona gawarwakinsu. Mazauna sun ce Fatima ta kira ƴan uwanta tana neman taimako kafin harin, yayin da wayoyinta daga baya aka ce an same su tare da wani ɗan uwanta, Umar Auwalu.

Rundunar ƴansandan Jihar Kano ta ce ta cafke mutane uku, ciki har da Umar Auwalu mai shekara 23, wanda ake zargin shi ne jagoran tawagar kuma ɗan uwan marigayiyar ne.

  • Atiku Ya Yi Allah-Wadai Da Kisan Uwa Da Ƴaƴanta Shida A Kano
  • ‘Yansanda Sun Kama Mutane 3 Da Ake Zargi Da Kisan Wata Mata Da ‘Ya’yanta 6 A Kano

A cewar mai magana da yawun ƴansanda, Abdullahi Haruna Kiyawa, an kama su ne a wani aikin sirri da aka gudanar tsakanin daren 17 zuwa safiyar 18 ga Janairu, 2026. Abubuwan da aka ƙwato sun haɗa da wani tufafi da ya jiƙe da jini, da wayoyin marigayiyar biyu, da adda, da kulake da kuɗi. Binciken farko ya nuna Umar ya amsa laifin shiga kisan, tare da zargin tawagar tasu na da hannu a wasu hare-hare makamancin wannan a baya.

ADVERTISEMENT

Mijin Fatima, Bashir, ya ce wannan lamari ya tayar masa da hankali matuƙa kuma ba zai taɓa mantawa da shi ba. Ya bayyana cewa yana kasuwa ne lokacin da aka kira shi aka shaida masa abin da ya faru. “Da na dawo, na tarar an kashe su da adduna da ƙarafuna masu nauyi kamar Keken ɗinki,” in ji shi cikin kuka, yana mai roƙon Allah Ya gafarta wa iyalansa tare da haɗa su a Aljanna.

Gwamnan Jihar Kano, Abba Yusuf, ya yi Allah-wadai da harin, yana mai kiran sa da mummuna kuma abin da ba za a lamunta da shi ba, tare da umartar hukumomin tsaro su kamo duk masu hannu a ciki su gurfanar da su don fuskantar hukunci.

LABARAI MASU NASABA

Zargin Ɓata Suna: Kwankwaso Ya Yi Barazanar Neman Diyyar Naira Biliyan 10 Kan Wani Malamin Coci

Atiku Ya Soki Tsare El-Rufai, Ya Ce Sharuɗan Belinsa Sun Yi Tsauri

Tsohon Mataimakin Shugaban Ƙasa, Atiku Abubakar, da Mataimakin Shugaban Majalisar Dattawa, Barau Jibrin, su ma sun yi tir da lamarin, suna kira da a hanzarta bincike da shari’a domin tabbatar da adalci da kare rayuka da dukiyoyin al’umma.

Kano
Abubakar Sulaiman
Website |  + postsBio
  • Abubakar Sulaiman
    Jam’iyyar APC Ta Tafka Asarar Mabiya A Gombe, Sun Bi Pantami PDP
  • Abubakar Sulaiman
    Gwamnatin Tarayya Ta Gargaɗi Masu Ɓoye Gas Ɗin Girki
  • Abubakar Sulaiman
    Kotu Ta Bayar Da Umarnin Tsare Sowore A Gidan Yarin Kuje
  • Abubakar Sulaiman
    Yanzu-Yanzu: An Kashe Manoma 18 Da Raunata Wasu A Wani Sabon Hari A Filato

MASU ALAKA

Yadda Na Sayar Da Kadarori Na Don Ɗaukar Nauyin Ɗalibai A Ƙasashen Waje – Kwankwaso
Manyan Labarai

Zargin Ɓata Suna: Kwankwaso Ya Yi Barazanar Neman Diyyar Naira Biliyan 10 Kan Wani Malamin Coci

June 24, 2026
Tinubu Ya Gaza Wajen Magance Matsalar Tsaro A Nijeriya — Atiku
Manyan Labarai

Atiku Ya Soki Tsare El-Rufai, Ya Ce Sharuɗan Belinsa Sun Yi Tsauri

June 24, 2026
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta
Manyan Labarai

’Yansanda Sun Kama Wani Mutum da Harsasai 174 A Nasarawa

June 24, 2026
Next Post
Jerin Kyaututtukan Da Aka Bayar Bayan Kammala Gasar AFCON 2025

Jerin Kyaututtukan Da Aka Bayar Bayan Kammala Gasar AFCON 2025

LABARAI MASU NASABA

Yadda Na Sayar Da Kadarori Na Don Ɗaukar Nauyin Ɗalibai A Ƙasashen Waje – Kwankwaso

Zargin Ɓata Suna: Kwankwaso Ya Yi Barazanar Neman Diyyar Naira Biliyan 10 Kan Wani Malamin Coci

June 24, 2026
Li Qiang Ya Halarci Bikin Bude Dandalin Tattalin Arzikin Duniya Na Davos Na Shekarar 2026

Li Qiang Ya Halarci Bikin Bude Dandalin Tattalin Arzikin Duniya Na Davos Na Shekarar 2026

June 24, 2026
Xi Ya Yi Kiran Daukar Matakan Zamanantar Da Aikin Gona Da Yankunan Karkara

Xi Ya Yi Kiran Daukar Matakan Zamanantar Da Aikin Gona Da Yankunan Karkara

June 24, 2026
Tinubu Ya Gaza Wajen Magance Matsalar Tsaro A Nijeriya — Atiku

Atiku Ya Soki Tsare El-Rufai, Ya Ce Sharuɗan Belinsa Sun Yi Tsauri

June 24, 2026
Trump Ne Zai Jagoranci Bayar Da Kofin Duniya A Wasan Ƙarshe – Infantino

Trump Ne Zai Jagoranci Bayar Da Kofin Duniya A Wasan Ƙarshe – Infantino

June 24, 2026
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

’Yansanda Sun Kama Wani Mutum da Harsasai 174 A Nasarawa

June 24, 2026
Sojoji Sun Kama Ɗan Fashi Da Makami A Taraba

Sojoji Sun Kama Ɗan Fashi Da Makami A Taraba

June 24, 2026
An Kashe Mutum 2, 8 Sun Jikkata Yayin Rikici A Bauchi

An Kashe Mutum 2, 8 Sun Jikkata Yayin Rikici A Bauchi

June 24, 2026
Tsohon Shugaban APC Na Kebbi Ya Rasu A Hannun ’Yan Bindiga

Tsohon Shugaban APC Na Kebbi Ya Rasu A Hannun ’Yan Bindiga

June 24, 2026
Ya Kamata Sin Da Birtaniya Su Yi Aiki Tare Don Ci Gaba Da Inganta Dangantakarsu

Ya Kamata Sin Da Birtaniya Su Yi Aiki Tare Don Ci Gaba Da Inganta Dangantakarsu

June 23, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.