ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Asiri Ya Tonu: Yadda Aka Kashe Uwa da Ƴaƴanta Shida A Kano

by Abubakar Sulaiman
8 months ago
Kano

Mazauna unguwar Dorayi Chiranchi a birnin Kano sun bayyana yadda aka aikata mummunan kisan da ya yi sanadiyyar mutuwar wata mata, Fatima Abubakar mai shekara 35, da ƴaƴanta shida. An ce maharan sun kutsa cikin gidansu a Dorayi Gidan Kwari, suka kulle gidan kafin su kashe su, sannan suka yi ƙoƙarin ƙona gawarwakinsu. Mazauna sun ce Fatima ta kira ƴan uwanta tana neman taimako kafin harin, yayin da wayoyinta daga baya aka ce an same su tare da wani ɗan uwanta, Umar Auwalu.

Rundunar ƴansandan Jihar Kano ta ce ta cafke mutane uku, ciki har da Umar Auwalu mai shekara 23, wanda ake zargin shi ne jagoran tawagar kuma ɗan uwan marigayiyar ne.

  • Atiku Ya Yi Allah-Wadai Da Kisan Uwa Da Ƴaƴanta Shida A Kano
  • ‘Yansanda Sun Kama Mutane 3 Da Ake Zargi Da Kisan Wata Mata Da ‘Ya’yanta 6 A Kano

A cewar mai magana da yawun ƴansanda, Abdullahi Haruna Kiyawa, an kama su ne a wani aikin sirri da aka gudanar tsakanin daren 17 zuwa safiyar 18 ga Janairu, 2026. Abubuwan da aka ƙwato sun haɗa da wani tufafi da ya jiƙe da jini, da wayoyin marigayiyar biyu, da adda, da kulake da kuɗi. Binciken farko ya nuna Umar ya amsa laifin shiga kisan, tare da zargin tawagar tasu na da hannu a wasu hare-hare makamancin wannan a baya.

ADVERTISEMENT

Mijin Fatima, Bashir, ya ce wannan lamari ya tayar masa da hankali matuƙa kuma ba zai taɓa mantawa da shi ba. Ya bayyana cewa yana kasuwa ne lokacin da aka kira shi aka shaida masa abin da ya faru. “Da na dawo, na tarar an kashe su da adduna da ƙarafuna masu nauyi kamar Keken ɗinki,” in ji shi cikin kuka, yana mai roƙon Allah Ya gafarta wa iyalansa tare da haɗa su a Aljanna.

Gwamnan Jihar Kano, Abba Yusuf, ya yi Allah-wadai da harin, yana mai kiran sa da mummuna kuma abin da ba za a lamunta da shi ba, tare da umartar hukumomin tsaro su kamo duk masu hannu a ciki su gurfanar da su don fuskantar hukunci.

LABARAI MASU NASABA

Ballon d’Or: Messi, Yamal, Da Mane Na Cikin ‘Yan Wasa 30 Da Aka Zaɓo

Ɓata-gari Sun Kai Wa Ayarin Peter Obi Hari A Benue

Tsohon Mataimakin Shugaban Ƙasa, Atiku Abubakar, da Mataimakin Shugaban Majalisar Dattawa, Barau Jibrin, su ma sun yi tir da lamarin, suna kira da a hanzarta bincike da shari’a domin tabbatar da adalci da kare rayuka da dukiyoyin al’umma.

Kano
Abubakar Sulaiman
Website |  + postsBio
  • Abubakar Sulaiman
    Iyalin El-Rufai Sun Bai Ministan Tsaro Wa’adin Kwana 7 Kan Zargin Rikicin Kudancin Kaduna
  • Abubakar Sulaiman
    Atiku Ya Zargi Gwamnatin Tarayya Da Cin Bashi Kamar Mashayin Da Kuɗi Ya Ƙarewa
  • Abubakar Sulaiman
    Boko Haram Ta Kai Hari Adamawa, Ana Fargabar Mutuwar Mutane 11
  • Abubakar Sulaiman
    Ƴan Bindiga Sun Kai Hari Sokoto, Sun Kashe Mutane 7, Sun Yi Garkuwa Da 12

MASU ALAKA

Ballon D'or
Manyan Labarai

Ballon d’Or: Messi, Yamal, Da Mane Na Cikin ‘Yan Wasa 30 Da Aka Zaɓo

September 8, 2026
Ɓata-gari Sun Kai Wa Ayarin Peter Obi Hari A Benue
Manyan Labarai

Ɓata-gari Sun Kai Wa Ayarin Peter Obi Hari A Benue

September 8, 2026
2027: Atiku Na Amfani Da Tallafin Mai A Matsayin Dabarun Siyasa – Fayemi
Manyan Labarai

2027: Atiku Na Amfani Da Tallafin Mai A Matsayin Dabarun Siyasa – Fayemi

September 8, 2026
Next Post
Jerin Kyaututtukan Da Aka Bayar Bayan Kammala Gasar AFCON 2025

Jerin Kyaututtukan Da Aka Bayar Bayan Kammala Gasar AFCON 2025

LABARAI MASU NASABA

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026
Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

September 8, 2026
Wani Soja Ya Kashe Kansa Bayan Kashe Matarsa A Jihar Neja

Kano Za Ta Kafa Sansanonin Sojoji A Ƙananan Hukumomin Da Ke Fuskantar Barazanar Tsaro

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.