Rundunar ‘Yansandan Jihar Kano ta sanar da kama miyagun mutane uku da ake zargi da kisan gillar wata mata da ‘ya’yanta shida a unguwar Dorayi Chiranchi, cikin birnin Kano a ranar Asabar.
A cikin wata sanarwa da Jami’in Hulda da Jama’a na ‘Yansanda (PPRO), CSP Abdullahi Haruna Kiyawa ya fitar a ranar Lahadi, rundunar ta ce an kama wadanda ake zargin ne a karkashin kulawar Kwamishinan ‘Yansanda na Jihar, CP Ibrahim Adamu Bakori.
- Gwamna Yahaya Ya Yi Maraba Da Ƴan Majalisa 2 Na PDP Da Suka Sauya Sheƙa Zuwa APC
- Mutum 10 Sun Shiga Hannu Bisa Zargin Fashi Da Safarar Miyagun Ƙwayoyi A Jigawa
“Rundunar ‘Yansanda ta Jihar Kano ta yi amfani da jami’an leken asiri don kama wasu mutane uku da ake zargi da kisan gillar wata mata da ‘ya’yanta shida a unguwar Dorayi Chiranchi, Kano a ranar 17 ga Janairu, 2026,” in ji sanarwar.
Wadanda ake zargin sun hada da Umar Auwalu, mai shekaru 23, na unguwar Sabuwar Gandu; Isyaku Yakubu, wanda aka fi sani da Chebe, mai shekaru 40, na unguwar Sagagi, da Yakubu Abdulaziz, wanda aka fi sani da Wawo, mai shekaru 21, na unguwar Sabon Gida Sharada. An kama su ne a wani samame da aka kai tsakanin karfe 10 na dare a ranar Asabar, 17 ga Janairu zuwa karfe 4 na safe a ranar Lahadi, 18 ga Janairu, 2026.
‘Yansanda sun bayyana cewa, Umar Auwalu, wanda ake zargi da jagorantar tawagar maharan, dan uwan matar da aka kashe ne, kuma ya amsa laifin kisan gillar da suka yi a unguwar Dorayi Chiranchi yayin da ake yi musu tambayoyi.
Abubuwan da aka samu daga wadanda ake zargin sun hada da tufafi guda hudu masu jini, wayoyin hannu guda biyu na mamatan, adda, sanda, da kuma wani kudade.
‘Yansanda sun ce ana ci gaba da bincike kuma sun tabbatar wa mazauna yankin cewa za a gurfanar da duk wadanda ke da hannu a cikin laifukan.















Discussion about this post