ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Asirin Kwalejojin Ilimi 41 Da Ke Ba Da Shaidar NCE Ta Bogi Ya Tonu A Bauchi

by Khalid Idris Doya
4 years ago
Ilimi

Hukumar kula da Kwalejojin Ilimi a Nijeriya (NCCE) ta rufe tare da kulle cibiyoyin ilimi guda 41 da ke bada shaidar karatun ilimi ta NCE na bogi a jihar Bauchi.

A wata wasika da hukumar ta aike wa kwamishinan ilimi na jihar Bauchi Dakta Aliyu Usman Tilde mai dauke da kwanan wata 5 ga watan Satumba 2022 da wakilinmu ya ci karo da ita a ranar Laraba, na cewa dukkanin cibiyoyin ilimi da Kwalejojin ilimi da lamarin ya shafa an basu wata daya tak da su tabbatar sun kulle ko kuma su fuskanci shari’a.

  • Kotun Daukaka Kara Ta Umurci Kungiyar ASUU Da Ta Gaggauta Janye Yajin Aikin Da Take
  • Yaya Ake Gane Alamomin Mutum Ya Yi Kyakykyawan Karshe?

Wasikar wacce babban sakataren hukumar mai cikakken iko, Farfesa Paulinus Chijioke Okwelle ya sanya wa hannu, ya yi tilawar cewa a watan Oktoba da Nuwamban 2021 hukumar ta gudanar da wani atisayen zagayen kwalejoji a fadin kasar nan domin bankado makarantun da ke bada shaidar kamala karatun NCE na bogi, inda a bias hadin kai jihohi suka basu aka samu nasarar gudanar da aikin binciken cikin nasara.

ADVERTISEMENT

A cewar hukumar NCCE an tura wa ma’aikatar ilimi ta tarayya rahoton aikin binciken da aka gudanar sannan kuma aka bai wa hukumar umarninta gaggauta kulle dukkanin cibiyoyin da ta gano na bogi ne.

“Kan wannan, hukumar nan tana jawo hankalin Gwamnatin jihar Bauchi da ta taimaka mana wajen tabbatar da wadannan makarantun sun kasance a kulle da suke bayar da shaidar NCE na bogi,”Okwelle ya kara.

LABARAI MASU NASABA

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

NCCE ta jero sunan kwalejoji da cibiyoyin ilimin da wannan kullewar ta shafa da aka gano suna gudanuwa ta haramtacciyar hanya da cewa sune kwalejin ilimi Mayo Belwad a ke hadin guiwa da kwalejin ilimi ta Azare; kwalejin ilimita Abubakar Adamu Mu’azu da ke Boto; Al-Iman College of Education, Nasarawa. Nasarawa, Bauchi, da kwalejin ilimi ta Aped da ke Liman Katagun, Bauchi. Sauran sun kunshi kwalejin ilimi da ke Bununu a karamar hukumar Tafawa Balewa; kwalejin ilimi mai zurfi da ke Magama, Gumau, Toro; kwalejinkoyar da ilimin larabci da addini da ke Toro; kwalejin SACH da ke Bauchi, makarantar koyar da ilimin Kimiyyar lafiyar muhalli (EHS) da ke Bauchi; kwalejin ilimi ta ECWA da ke Bayarw da kuma cibiyar ilimi ta Garba Ibrahim.

Cibiyoyin ilimin da rufewarta shafa har da cibiyar koyar da ilimin addini da larabci ta Murkazul Islam da ke Azare; Azare Sahib Collegeof Education; kwalejin ilimi ta Sardauna da ke Bauchi; kwalejin ilimi ta Sheikh Adamu Abubakar da ke Azare; Sunnah Bauchi College of Education, Toro; Thomas Moor Institute, Bauchi; Urat Memorial Collegeof Education, Bauchi; Diamond Teachers Training College ofEducation, Bauchi da kuma kwalejin ilimi ta Ibrahim Bello da ke Magama Gumau.

Sauran sun hada da kwalejin ilimin addini da larabci ta Annur Kano da ke Bauchi; kwalejin ilimin addini da larabci ta Annur Kano da ke karamar hukumar Katagum; kwalejin ilimi da ke Burra Ningi; Annur Kano College of Education, Giade; kwalejin Sheikh Adam, Azare, Bauchi; Annur Kano College of Education da ke karamar hukumar Warji; Da’awa Bauchi College of Education, Darazo; Da’awa Bauchi College of Education, Kafin Kafin Madaki, Bauchi; Danyaya College of Education, Miya Ganjuwa Miya Ganjuwa LGA, Bauchi; Darazo College of Education, Akuyam; Gindiri College of Education, Warji LGA, da kwalejin ilimi ta Sa’adatu Rimi Kumbotso Gidan Marayu Katagum Zaki.

Farfesa Okwelle, “Dangane da wannan matakin, kwalejoji da cibiyoyin da lamarin nan ya shafa suna da zarafin wata daya da su kulle ko su fuskanci shari’a.”

LEADERSHIP Hausa ta yi tilawar cewa a watan Yuli 2021 Majalisar Dokokin Jihar Bauchi ta nuna damuwarta kan cibiyoyin da aka gano suna ba da shaidar kammala karatun NCE na bogi a jihar. A kudirin da mambar Majalisar mai wakiltar mazabar Hardawa, Hon. Mohammed Babayo ya gabatar, ya ce wannan lamarin na shafan harkar ilimi a jihar tare da gurbata sashin ilimi.

A cewarsa, cikin kwalejin ilimi masu zaman kansu guda 58 da ke ba da shaidar kammala NCE, guda 13 ne kacal suke da rijista da NCCE.

Majalisar ta bukaci Gwamnatin jihar Bauchi da ta tuntubi hukumar NCCE da hukumar NBTE domin lalubo bakin zaren dakile makarantun da suke ba da shaidar NCE na bogi a jihar.

A cewarsa, “Akwai bukatar cikin gaggawa a shawo kan wannan matsalar domin tsarkake harkokin ilimi.”Nan take, Kakakin Majalisar Dokokin Jihar, Abubakar Y Sulaiman ya umarci kwamitin Majalisar na ilimi da ya bincike lamarin sannan ya gabatar musu da rahoto cikin kwanaki 30.

Ilimi
Khalid Idris Doya
+ postsBio
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Ɗan Majalisar Dokokin Bauchi, Hon. Wanzam, Ya Rasu
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Tsohon Mataimakin Gwamnan Bauchi, Audu Sule Katagum Ya Rasu
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Kotu Ta Umarci DSS Ta Mutunta Umarninta Kan Shari’ar Filin Firo Na Bauchi
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Ana Zargin Jami’in Kwastam Da Kashe Kansa A Bauchi Saboda Damuwa

MASU ALAKA

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi
Labarai

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”
Ra'ayi Riga

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma
Labarai

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Next Post
Kasar Sin Ta Mika Dakin Adana Magunguna Na Zamani Ga Zimbabwe

Kasar Sin Ta Mika Dakin Adana Magunguna Na Zamani Ga Zimbabwe

LABARAI MASU NASABA

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026
Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026
Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

June 24, 2026
Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.