ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Saturday, July 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Aure Ba Ya Ruƙuwa Sai Da Sana’a

by Ibrahim Bala
5 months ago
Aure

Assalamu Alaikum Wa Rahmatullahi Ta’ala Wa Barakatuhu.

Jama’a barkanmu da kasancewa tare da wannan fili mai albarka, filin da ya saba zaƙulo muku batutuwan da suke ci wa al’umma tuwo a kwarya.

Kamar kowane mako a yau ina so nayi magana akan iyaye da samari, sannan kuma zan yi magana akan aure gabaɗayansa.

ADVERTISEMENT

A ‘yan lokutan nan ko na ce a ‘yan shekarun nan, za a ga yara ne ƙanana suke ta yin aure, magana ta gaskiya aure ba magana ce ta wasa ba. Ya kamata a riƙa lura, shi ya sa za a ga zawarawa yara ƙanana suna da yawa, ba don komai ba sai don akwai wasu abubuwa da ba ma iya kulawa a auren.

  • Ɓata-gari Sun Kashe Matar Aure Da ’Ya’yanta 3 A Kano
  • Yadda Takaddama Ta Kaure Bayan Ceto Daliban Neja 130

Na farko iyaye wasu kawai sun damu ‘yarsu ta yi aure, ko kuma yaron yana yawan kashe mata kuɗi, ko yayi lefe masu kyau, ko ya biya kuɗin na gani ina so da kyau, ko dan gidan su wasu ne. Na biyu kuma, yaran auren a baki kawai suke jin shi, ‘yar budurwa ta ɗan yi kyau, ta ɗan fara shekaru, fara ce sai na aure ta. 

LABARAI MASU NASABA

Akwai Barazanar Ƙaruwar Yunwa A Arewacin Nijeriya – Peter Obi

Pakistan Ta Kashe Mutum 36 A Hare-haren Da Ta Kai Kan Iyakarta Da Afghanistan

Su kuma iyaye wani lokacin yana ɗan yin sana’arsa, magana ta gaskiya kuma, ba ma son mu vata masa rai, idan ba a yi masa aure ba. Duk waɗan nan abubuwan ba su ne abun lurar ba, dole aure baya ruƙuwa sai da sana’a, sana’ar ma mai ƙwari wacce ba wai kai kaɗai za ka ci da kanka ba, shin za ka iya riƙe wani? shi ne abun lura.

Idan aiki kake yi, aikin da kake yi albashin zai iya isar ka bayan ka ciyar da matarka har a samu ɗan wani abun?. Saboda mu’malata rayuwa, kuɗin haya, rashin lafiya ko wata irin larura, dole sai muna iya kallon abun.

Magana ta gaskiya aure ba zai ruƙu ba sai da sana’a, duk gatanka ba zai ruƙu ba sai da sana’a. Aure wani lokacin tamkar doguwar mota ce dole kullum za ka sha mai. Ko kai kanka kasan da wahala ba a ɗan tsaya a gareji ba, ko kuma wani abun.

To, aure na buƙatar kulawa, ba zai ruƙu ba sai da kuɗi, kuma kuɗi ba zai ruƙu ba sai da sana’a. Duk mtumin da za a ce kullum zai ɗauko zai baka sai ya gaji, amma aka ce kai kake da hanyar samu da za ka riƙe gidanka to, sai ka yi wannan. Shi hankali ba a yarinta yake ba, daman duk mutumin da zai mayar da hankali akan sana’a to, yana da hankali kenan.

Ba maganar a yi sauri bane, ko shi yaro ya matsa yana son iyali duk ba wannan abun bane ba. Duk mijin da ka gani a duniya akwai matarsa, duk matar da ka gani akwai mijinta. Sai mun tsaya mun nutsu ba don komai ba, sai don yanayi na rayuwa, zawarawa sun yi yawa.

Sannan za ka ga wani yaron ɗan ƙanƙani ‘yar sana’ar sana’ar da yake yi ma daƙyar ake ci da matar, amma ya zo ƙara neman aure. Dan Allah mu nutsu duk mu kiyaye dokokin Allah, ba kai za ka aurar da ita ba, ikon Allah ne da yardar sa.

Amma mu kawai da an zo neman aure, an kawo kuɗi, za a yi caraf a karve, babu bincike, wani ma ƙarya yake yi. Idan ka buncike shi ma, sana’ar ta ƙarya ce.

Allah ya sa mu dace, Allah ubangiji ya zaunar da yaranmu, ƙannenmu da matanmu lafiya. Amin. 

Wassalamu Alaikum

Aure
Ibrahim Bala
+ postsBio
  • Ibrahim Bala
    https://hausa.leadership.ng/author/ibrahim-bala/
    A Duba Halin Da Masu Buƙata Ta Musamman Ke Ciki
  • Ibrahim Bala
    https://hausa.leadership.ng/author/ibrahim-bala/
    Matsalar Ƙwacen Waya: Ina Mafita?
  • Ibrahim Bala
    https://hausa.leadership.ng/author/ibrahim-bala/
    Falalar Goman Farko Na Zul-hajji 
  • Ibrahim Bala
    https://hausa.leadership.ng/author/ibrahim-bala/
    Bukatar Kulawa Da Marayu Da Masu Karamin Karfi

MASU ALAKA

Akwai Barazanar Ƙaruwar Yunwa A Arewacin Nijeriya – Peter Obi
Labarai

Akwai Barazanar Ƙaruwar Yunwa A Arewacin Nijeriya – Peter Obi

July 4, 2026
Pakistan Ta Kashe Mutum 36 A Hare-haren Da Ta Kai Kan Iyakarta Da Afghanistan
Labarai

Pakistan Ta Kashe Mutum 36 A Hare-haren Da Ta Kai Kan Iyakarta Da Afghanistan

July 4, 2026
Kwankwasiyya Ta Buƙaci A Binciki Zargin Kasafin Kuɗin PFIPC
Manyan Labarai

Kwankwasiyya Ta Buƙaci A Binciki Zargin Kasafin Kuɗin PFIPC

July 4, 2026
Next Post
Sin Za Ta Ci Gaba Da Taka Muhimmiyar Rawa A Ayyukan Hukumar IMO

Sin Za Ta Ci Gaba Da Taka Muhimmiyar Rawa A Ayyukan Hukumar IMO

LABARAI MASU NASABA

Babban Dan Majalissar Dokokin Kasar Sin Ya Halarci Jana’izar Marigayi Jagoran Addini Na Iran

Babban Dan Majalissar Dokokin Kasar Sin Ya Halarci Jana’izar Marigayi Jagoran Addini Na Iran

July 4, 2026
Akwai Barazanar Ƙaruwar Yunwa A Arewacin Nijeriya – Peter Obi

Akwai Barazanar Ƙaruwar Yunwa A Arewacin Nijeriya – Peter Obi

July 4, 2026
Pakistan Ta Kashe Mutum 36 A Hare-haren Da Ta Kai Kan Iyakarta Da Afghanistan

Pakistan Ta Kashe Mutum 36 A Hare-haren Da Ta Kai Kan Iyakarta Da Afghanistan

July 4, 2026
Kwankwasiyya Ta Buƙaci A Binciki Zargin Kasafin Kuɗin PFIPC

Kwankwasiyya Ta Buƙaci A Binciki Zargin Kasafin Kuɗin PFIPC

July 4, 2026
Matsalar Tsaro: Gwamnatin Tarayya Ta Nemi Taimakon Ƙasashen Waje

Gwamnatin Tarayya Ta Bayyana Dalilanta Na Sake Fasalin Hukumar NYSC

July 4, 2026
Gwamnan Katsina Ya Kai Ziyarar Duba Aikin Cibiyar Gyaran Motoci Mai Amfani Da Hasken Rana

Gwamnan Katsina Ya Kai Ziyarar Duba Aikin Cibiyar Gyaran Motoci Mai Amfani Da Hasken Rana

July 4, 2026
Yadda Ayyukan Titunan Gwamnan Kaduna Suka Farfaɗo Da Ilimi Da Kiwon Lafiya Da Noma A Sabon Gari

Yadda Ayyukan Titunan Gwamnan Kaduna Suka Farfaɗo Da Ilimi Da Kiwon Lafiya Da Noma A Sabon Gari

July 4, 2026
Matsalar Tsaro: Gwamnatin Tarayya Ta Nemi Taimakon Ƙasashen Waje

Uwargidan Shugaban Ƙasa Ta Ƙaddamar Da Muhimman Ayyukan Ci Gaba A Jihar Jigawa

July 4, 2026
Matsalar Tsaro: Gwamnatin Tarayya Ta Nemi Taimakon Ƙasashen Waje

NPA Ta Ɗaura Ɗamarar Magance Matsalolin Kasuwanci Da Ƙasashen Waje

July 4, 2026
Me Ya Sa Har Yanzu Manoma A Arewa Suka Gwammace Yin Noma Da Galmar Shanu

Me Ya Sa Har Yanzu Manoma A Arewa Suka Gwammace Yin Noma Da Galmar Shanu

July 4, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.