ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Saturday, July 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Aure Ba Ya Ruƙuwa Sai Da Sana’a

by Ibrahim Bala
6 months ago
Aure

Assalamu Alaikum Wa Rahmatullahi Ta’ala Wa Barakatuhu.

Jama’a barkanmu da kasancewa tare da wannan fili mai albarka, filin da ya saba zaƙulo muku batutuwan da suke ci wa al’umma tuwo a kwarya.

Kamar kowane mako a yau ina so nayi magana akan iyaye da samari, sannan kuma zan yi magana akan aure gabaɗayansa.

ADVERTISEMENT

A ‘yan lokutan nan ko na ce a ‘yan shekarun nan, za a ga yara ne ƙanana suke ta yin aure, magana ta gaskiya aure ba magana ce ta wasa ba. Ya kamata a riƙa lura, shi ya sa za a ga zawarawa yara ƙanana suna da yawa, ba don komai ba sai don akwai wasu abubuwa da ba ma iya kulawa a auren.

  • Ɓata-gari Sun Kashe Matar Aure Da ’Ya’yanta 3 A Kano
  • Yadda Takaddama Ta Kaure Bayan Ceto Daliban Neja 130

Na farko iyaye wasu kawai sun damu ‘yarsu ta yi aure, ko kuma yaron yana yawan kashe mata kuɗi, ko yayi lefe masu kyau, ko ya biya kuɗin na gani ina so da kyau, ko dan gidan su wasu ne. Na biyu kuma, yaran auren a baki kawai suke jin shi, ‘yar budurwa ta ɗan yi kyau, ta ɗan fara shekaru, fara ce sai na aure ta. 

LABARAI MASU NASABA

Kyamar Baki: Shettima Ya Ja Kunnen Gwamnatin Afirka Ta Kudu

Yadda Kasar Sin Ta Samar Da Ci Gaba Na Bai Daya

Su kuma iyaye wani lokacin yana ɗan yin sana’arsa, magana ta gaskiya kuma, ba ma son mu vata masa rai, idan ba a yi masa aure ba. Duk waɗan nan abubuwan ba su ne abun lurar ba, dole aure baya ruƙuwa sai da sana’a, sana’ar ma mai ƙwari wacce ba wai kai kaɗai za ka ci da kanka ba, shin za ka iya riƙe wani? shi ne abun lura.

Idan aiki kake yi, aikin da kake yi albashin zai iya isar ka bayan ka ciyar da matarka har a samu ɗan wani abun?. Saboda mu’malata rayuwa, kuɗin haya, rashin lafiya ko wata irin larura, dole sai muna iya kallon abun.

Magana ta gaskiya aure ba zai ruƙu ba sai da sana’a, duk gatanka ba zai ruƙu ba sai da sana’a. Aure wani lokacin tamkar doguwar mota ce dole kullum za ka sha mai. Ko kai kanka kasan da wahala ba a ɗan tsaya a gareji ba, ko kuma wani abun.

To, aure na buƙatar kulawa, ba zai ruƙu ba sai da kuɗi, kuma kuɗi ba zai ruƙu ba sai da sana’a. Duk mtumin da za a ce kullum zai ɗauko zai baka sai ya gaji, amma aka ce kai kake da hanyar samu da za ka riƙe gidanka to, sai ka yi wannan. Shi hankali ba a yarinta yake ba, daman duk mutumin da zai mayar da hankali akan sana’a to, yana da hankali kenan.

Ba maganar a yi sauri bane, ko shi yaro ya matsa yana son iyali duk ba wannan abun bane ba. Duk mijin da ka gani a duniya akwai matarsa, duk matar da ka gani akwai mijinta. Sai mun tsaya mun nutsu ba don komai ba, sai don yanayi na rayuwa, zawarawa sun yi yawa.

Sannan za ka ga wani yaron ɗan ƙanƙani ‘yar sana’ar sana’ar da yake yi ma daƙyar ake ci da matar, amma ya zo ƙara neman aure. Dan Allah mu nutsu duk mu kiyaye dokokin Allah, ba kai za ka aurar da ita ba, ikon Allah ne da yardar sa.

Amma mu kawai da an zo neman aure, an kawo kuɗi, za a yi caraf a karve, babu bincike, wani ma ƙarya yake yi. Idan ka buncike shi ma, sana’ar ta ƙarya ce.

Allah ya sa mu dace, Allah ubangiji ya zaunar da yaranmu, ƙannenmu da matanmu lafiya. Amin. 

Wassalamu Alaikum

Aure
Ibrahim Bala
+ postsBio
  • Ibrahim Bala
    https://hausa.leadership.ng/author/ibrahim-bala/
    Hanyoyin Da Za A Bi A Rage Yawan Zawarawa
  • Ibrahim Bala
    https://hausa.leadership.ng/author/ibrahim-bala/
    A Duba Halin Da Masu Buƙata Ta Musamman Ke Ciki
  • Ibrahim Bala
    https://hausa.leadership.ng/author/ibrahim-bala/
    Matsalar Ƙwacen Waya: Ina Mafita?
  • Ibrahim Bala
    https://hausa.leadership.ng/author/ibrahim-bala/
    Falalar Goman Farko Na Zul-hajji 

MASU ALAKA

Kashim Shettima Ya Mayar Da Martani Kan Tsadar Rayuwa
Labarai

Kyamar Baki: Shettima Ya Ja Kunnen Gwamnatin Afirka Ta Kudu

July 24, 2026
Yadda Kasar Sin Ta Samar Da Ci Gaba Na Bai Daya
Ra'ayi Riga

Yadda Kasar Sin Ta Samar Da Ci Gaba Na Bai Daya

July 24, 2026
NLC Ta Yi Barazanar Daukar Matakin Yajin Aiki Kan Albashi Mafi Karanci
Rahotonni

NLC Ta Yi Barazanar Daukar Matakin Yajin Aiki Kan Albashi Mafi Karanci

July 24, 2026
Next Post
Sin Za Ta Ci Gaba Da Taka Muhimmiyar Rawa A Ayyukan Hukumar IMO

Sin Za Ta Ci Gaba Da Taka Muhimmiyar Rawa A Ayyukan Hukumar IMO

LABARAI MASU NASABA

An Karrama Masana Ilimin Lissafi Na Kasar Sin Da Lambobin Yabo Na Fields Medal

An Karrama Masana Ilimin Lissafi Na Kasar Sin Da Lambobin Yabo Na Fields Medal

July 24, 2026
Ta Da Zaune Tsaye Da Philippines Ta Yi A Teku Ba Zai Lalata Dangantakar Hadin Gwiwar Sin Da ASEAN Ba

Ta Da Zaune Tsaye Da Philippines Ta Yi A Teku Ba Zai Lalata Dangantakar Hadin Gwiwar Sin Da ASEAN Ba

July 24, 2026
Jadawalin INEC:Kotun Daukaka Kara Ta Kassara Fatan Jam’iyyu Da ‘Yan Siyasa

Jadawalin INEC:Kotun Daukaka Kara Ta Kassara Fatan Jam’iyyu Da ‘Yan Siyasa

July 24, 2026
An Zartas Da Sanarwar Chengdu A Taron Ministocin Kungiyar APEC Kan Harkar Raya Fasahohin Dijital Da AI

An Zartas Da Sanarwar Chengdu A Taron Ministocin Kungiyar APEC Kan Harkar Raya Fasahohin Dijital Da AI

July 24, 2026
NNPP Za Ta Kwace Mulki A Jihar Imo – Kwankwaso

Jam’iyyar NDC Ta Shirya Tsaf Domin Kafa Gwamnati A 2027 —Kwankwaso

July 24, 2026
Sin Ta Kara Kamfanoni 14 Na Tarayyar Turai Cikin Jerin Wadanda Aka Hana Fitar Masu Da Kaya

Sin Ta Kara Kamfanoni 14 Na Tarayyar Turai Cikin Jerin Wadanda Aka Hana Fitar Masu Da Kaya

July 24, 2026
Kashim Shettima Ya Mayar Da Martani Kan Tsadar Rayuwa

Kyamar Baki: Shettima Ya Ja Kunnen Gwamnatin Afirka Ta Kudu

July 24, 2026
Yadda Kasar Sin Ta Samar Da Ci Gaba Na Bai Daya

Yadda Kasar Sin Ta Samar Da Ci Gaba Na Bai Daya

July 24, 2026
Hatsin Da Kasar Sin Ta Girbe Da Lokacin Zafin Bana Ya Zarce Tan Miliyan 150

Hatsin Da Kasar Sin Ta Girbe Da Lokacin Zafin Bana Ya Zarce Tan Miliyan 150

July 24, 2026
Wani Dalilin Da Ya Sa Al’Ummar Afirka Ke Kaunar Kasar Sin Shi Ne Yadda Take Kokarin Zuba Musu Jari

Wani Dalilin Da Ya Sa Al’Ummar Afirka Ke Kaunar Kasar Sin Shi Ne Yadda Take Kokarin Zuba Musu Jari

July 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.