Gwamnatin Jihar Kano ta sanar da ware tsabar kuɗi har naira miliyan 300 domin biyan sadaki da kuma samar da jarin dogaro da kai ga amare 1,500 da ke cikin shirin auren gata na jihar na wannan shekara.
Gwamna Abba Kabir Yusuf ya bayyana wannan mataki ne yayin wani taron faɗakarwa na kwana ɗaya da Hukumar Hisbah ta shirya wa ma’auratan a ɗakin taro na Coronashet Hall da ke Fadar Gwamnati, ta bakin Babban Komandan Hukumar, Sheikh Aminu Ibrahim Daurawa.
A ƙarkashin wannan tsari, kowace amarya za ta samu kyautar tsabar kuɗi naira dubu 200 wanda ya ƙunshi kuɗin sadaki da jarin fara ƙananan sana’o’i, tare da samun kayan ɗaki da suka haɗa da gado, katifa, tufafi da sauran kayayyakin amfanin gida.
Haka zalika, an tsara tallafi na musamman ga ango kowannensu, wanda zai haɗa da yaduddukan shadda, da hula, da buhun shinkafa da kuma mai girki domin taimakawa sabbin ma’auratan wajen gina tushen zaman takewa mai ɗorewa.
Taron faɗakarwar ya sami halartar malamai da masana daban-daban waɗanda suka gabatar da lakcocin sanin haƙƙoƙi da kiyaye zaman lafiya a aure, yayin da aka tsara gudanar da ɗaurin auren a masallatai daban-daban a fadin ƙananan hukumomi 44 na jihar.














