Tsohon Shugaban Majalisar Dattawa, David Mark, a ranar Laraba ya yi ƙoƙarin kwantar da hankulan ‘ya’yan jam’iyyar ADC, inda ya jaddada rikicin cikin gida ba zai kawo cikas ga haɗin kan jam’iyyar ko makomarta ba.
Jawabin nasa ya zo ne a daidai lokacin da ake fama da rikice-rikicen bangarori da kuma takaddama kan shugabanci, lamarin da ya haifar da rashin tabbas kan shirin jam’iyyar na tunkarar zaɓen 2027.
- An Cafke Yan Sudan Da Chadi 20 A Kano Bisa Shigo Wa Nijeria Ba Bisa Ka’ida Ba
- Hukumar Kashe Gobara Ta Kano Ta Ceto Rayuka 4, Dukiyar Naira Biliyan 1 A Watan Maris
Yayin da yake jawabi a wani bikin ibada a coci da aka gudanar domin cika shekaru 78 da haihuwarsa, Mark, wanda kuma shi ne shugaban jam’iyyar na kasa, ya nuna cewa, wannan rikicin ba wani abu ba ne mai sarkakiya, yana mai bayyana shi a matsayin wani mataki na yau da kullum a ci gaban kowace jam’iyya mai tasowa.
“Babu wani abin tashin hankali,” in ji shi, yana mai tabbatar wa ‘ya’yan jam’iyyar da ‘yan Nijeriya cewa komai yana ƙarƙashin kulawa.
A cewarsa, irin waɗannan ƙalubale ba bakon abu ba ne a cikin ƙungiyoyi ko jam’iyyun siyasa, kuma ya kamata a ɗauke su a matsayin wani ɓangare na ƙoƙarin ƙarfafa tsarin jam’iyya.
“Kalubale wani ɓangare ne na kowace ƙungiya ko jam’iyya mai tasowa. Abin da ya fi muhimmanci shi ne ƙudurinmu na haɗin kai don shawo kansu,” in ji shi.















Discussion about this post