Iran ta zargi Amurka da karya yarjejeniyar tsagaita wuta bayan sabbin hare-haren sama da Amurka ta kai kan wuraren makamai masu linzami da wasu jiragen ruwa a kudancin ƙasar.
Iran ta ce hare-haren sun faru ne cikin kwanaki biyu kacal bayan fara tsagaita wutar, tare da gargaɗin cewa za ta mayar da martani.
Kafafen yaɗa labaran gwamnati na Iran sun kuma ce an ji fashe-fashe a Bandar Abbas da ke kusa da mashigar ruwa ta Hormuz.
Sojojin Amurka sun ce sun kai harin ne domin kare dakarunsu daga barazanar da suke fuskanta daga sojojin Iran.
Sabbin hare-haren sun sa farashin mai ya ɗaga a kasuwannin duniya, yayin da ƙasar China ta buƙaci ɓangarorin biyu su mutunta yarjejeniyar tsagaita wuta tare da warware matsalolinsu cikin lumana.
Sakataren Harkokin Wajen Amurka, Marco Rubio, ya ce har yanzu ana ci gaba da tattaunawa a Qatar kuma akwai yiwuwar cimma yarjejeniyar zaman lafiya.
Iran ta kuma bayyana cewa tana aiki kan wata yarjejeniya mai matakai 14 domin kawo ƙarshen rikicin da ya fara bayan hare-haren Amurka da Isra’ila a watan Fabrairu.
A gefe guda kuma, an fara dawo da Intanet a wasu sassan Iran bayan watanni ana fama da katsewar sadarwa a faɗin ƙasar.















Discussion about this post