Bangarorin Sin da Birtaniya sun cimma yarjeniyoyi masu kyau yayin ziyarar firaministan Birtaniya Keir Starmer a nan kasar Sin.
Bangarorin biyu sun himmatu wajen bunkasa dangantakar abota mai dorewa bisa manyan tsare-tsare a duk fannoni a tsakaninsu. Inda suka amince da kulla huldar koli tsakanisu kan yanayi da muhalli yayin da suka amince da komawar gudanar da tattaunawar koli kan batun tsaro. Sannan za su gudanar da sabon zagaye na tattaunawar manyan tsare-tsare da na tattalin arziki da kudi, da kuma taron kwamitin hadin gwiwar kasuwanci da zamantakewa da sauran tattaunawar tsarin a wannan shekarar da muke ciki. Ban da wannan kuma, sun amince da maido da mu’ammalar al’ada tsakanin majalisar dokokin kasashen biyu. Bangaren Sin yana maraba da ‘yan majalisar dokokin Birtaniya masu burin ziyartar Sin, don fahimtar ainihin Sin. Za a gudanar da taron kwamitin ‘yan kasuwa na Sin da Birtaniya, inda kuma suka amince da kara karfafa hadin gwiwar ciniki da zuba jari ta bangarorin biyu. Bangaren Sin yana la’akari da matakin bai wa ‘yan kasar Birtaniya damar shigowa kasar ba tare da biza ba. Shugabannin kasashen biyu sun shaida rattaba hannu kan takardun hadin gwiwar gwamnatoci guda 12 a fannoni kamar ciniki da noma da abinci da al’adu da sa ido kan kasuwa, kana da hadin gwiwar bin doka. Bangarorin biyu sun kuma cimma takardun hadin gwiwa da yawa a fannoni kamar kudi, lafiya, watsa labarai, da ilimi. (Amina Xu)














Discussion about this post