Jam’iyyar APC ta sauya shirye-shiryenta na shekarar 2026 tare da tsawaita rijistar membobinta ta yanar gizo zuwa ranar 8 ga watan Fabrairu, 2026, domin bai wa mutane da dama damar shiga jam’iyyar.
Haka kuma, jam’iyyar ta ɗage babban taronta na ƙasa zuwa ranakun 27 da 28 ga watan Maris, 2026
- Gobara Ta Hallaka Mutum 2, Ta Lalata Dukiya Ta Biliyan 1.59 A Bauchi
- Gudunmawar Shehu Ibrahim Inyass (RTA) Ga Musulunci A Wayewar Zamani (2)
Taron zaɓen shugabannin jam’iyyar zai gudana ne a ranar 18 ga watan Fabrairu, 2026, amma ba za a gudanar da shi a jihohin Ribas, Osun, Ekiti da kuma Babban Birnin Tarayya ba.
A cewar jam’iyyar, an cire Jihar Ribas ne saboda an riga an gudanar da irin waɗannan taruka a baya, kuma shugabannin da aka zaɓa har yanzu suna kan mulki.
An kuma cire Osun, Ekiti da Abuja ne saboda za su gudanar da zaɓe nan ba da jimawa ba.
Jam’iyyar na sa ran samun mambobi sama da miliyan 12 a faɗin ƙasar nan kafin a rufe rijistar.















Discussion about this post