ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Friday, June 5, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Bankwana Da 2023: A Farfado Da Bangaren Kiwon Lafiya

by Leadership Hausa
2 years ago
2023

Bangaren kiwon lafiya a Nijeriya ya dade yana bukatar a kawo mashi dauki, a ‘yan shekarun nan gwamanatin Nijeriya ba ta samar da isasasun kudade ba ga harkar kiwon lafiya a Nijeriya, gwamnati ta kasa cika alkawarin da ta dauka a taron kasashen Afirka da aka yi a Abuja na ware kashi 15 na kasafin kudin kasa ga bangaren kiwon lafiya.

Yana da matukar muhimmanci a gane cewa, kusan shekara biyu da suka wuce kungiyar Tarayyar Afirka (AU) ta yi wani gangamin yaki da wasu manyan cututtuka da suka addabi al’umma, cuttukan sun hada da cutar Kanjamau,Tarin Fuka, Maleriya da sauran cututtukan da za a iya kare al’umma daga kamuwa da su a nahiyar gaba daya.

  • Hukumomin Sin Na Adawa Da Munanan Tanade-tanade Dake Da Alaka Da Sin A Cikin Dokar Ba Da Izinin Tsaron Amurka
  • Jirgin Ruwa Mai Binciken Teku Na Farko Na Kasar Sin Ya Gwada Yin Aiki Cikin Nasara

A taron da ya gudana a ranar 27 ga watan Afrilu 2001, an yi alkawura da dama da suka hada da alkawarin da Nijeriya ta yi na ware kashi 15 na kasafin kudinta a duk shekara ga bangaren samar da cikakkiyar kula da lafiyar al’umma, kasashen sun kuma yi alkawarin samar da issasun kudade don bunkasa harkar samar da kiwon lafiya a fadin nahiyar Afirka gaba daya.

ADVERTISEMENT

A wani rahoto da wata kungiya mai zaman kanta mai suna PACFaH @Scale ta wallafa inda ta yi nazarin kasafin kudin kasashen Afirka na tsawon shekara 10, ta gano cewa Nijeriya ta kasa cika alkawarin da ta yi na bayar da issasun kudi ga bangaren kiwon lafiya, inda a wasu lokutta ma kasafin kudin kiwon lafiya ba ya kaiwa kashi 3 a cikin kasafin kudin shekarar.

Wannan watsin da aka yi da bangaren kiwon lafiya ya sa bangaren ya yi tabarbarewar da ba a taba gani ba a tarihin kiwon lafiya a Afirka.

LABARAI MASU NASABA

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

Idan za a iya tunawa, ministan lafiya na gwamnatin tsohon Shugaba Kasa Muhammadu Buhari, Olorunnimbe Mamora ya bayyana cewa, kashi 3 cikin dari na cibiyoyin kiwon lafiya 30,000 da ake da su a Nijeriya ne kawai ake tafiyarwa yadda ya kamata.

Sakamakon wannan barakar a bayyane yake cewa, ‘yan Nijeriya na kashe fiye da Dala biliyan 2 a duk shekara wajen neman lafiya a kasashen waje yayin da kuma a gida a ke fafatawa da cututtukan da za a iya kare al’umma daga kamuwa da su amma kuma sai ga shi suna zama sanadiyar mutuwar mutane da dama.

Sai dai kuma an samu kwarin gwiwa a wannan makon yayin da Shugaban Kasa Bola Tinubu ya dauki wasu mihimman matakai na ware makudan kudade ga bangaren kiwon lafiya a Nijeriya.

A bikin ranar samar da lafiya ga al’ummar duniya, gwamnatin Bola Tinubu ta fito da wasu shirye-shirye da suka hada da gaggarumin zuba jari a bangaren kiwon lafiyar al’umma da kuma abin da ya shafi gine-ginen sabbin asibitoci da gyara wadanda ake dasu, haka nan kuma gwamnati ta bayar da tabbacin hakan zai dore na  shekaru masu zuwa. Wannan ya kuma hada da alkawarin tabbatar da cibiyoyin samar da lafiya da dama a sassan kasar nan suna tafiya yadda ya kamata. Gwamnatin ta kuma shirya sake fasalin tsarin bayar da tallafin kiwon lafiya ga al’ummar Nijeriya don mutane da dama su amfana kamar yadda dokar samar da kiwon lafiya ta kasa ta tanada (National Health Act).

Wannan jaridar ta yi imanin cewa, ya kamata a ce tuntuni aka samar da wadannan dokoki amma duk da haka muna maraba da gabatar da su da aka yi a wannan lokacin.

Yanzu da aka dawo da martabar harkar kiwon lafiya, gwammnatin Tinubu na da damar samar da ingantaccen kiwon lafiya na dukkan al’ummar Nijeriya kamar yadda ake fata, ba wai ya zama tamkar irin bayanan da ‘yan siyasa ke yi ba don samun kuri’un al’umma.

Dole ne a yaba wa wannan gwamnatin a kan yadda ta tsara wa kanta abubuwan da take son cimmawa a nan gaba, wadanda suka hada da samar da karin biliyoyin nairori ga bangaren kiwon lafiya, da kuma samar da hanyoyin sa idon don ganin ana kashe kudaden kamar yadda ya kamata.

Sai dai kuma shi tsarin, samar da tsare-tsare masu kyau ga bangaren kiwon lafiya kawai ba zai isa ba har sai gwamnatin ta  yi maganin matsaloli da tarnakin da bangaren lafiya a Nieriya yake fuskanta wadanda su ne suka kawo wa bangaren cikas a shekarun baya.

Ba za a amince da masu karkatar da kudaden da aka ware wa bangaren kiwon lafiya ba, ya kamata a samar da masu bincike akai-akai don ganin yadda ake kashe kudaden.

Idan har ana son tabbatar da canje-canjen da ake bukata, dole a samu hadin kai a tsakanin gwamnatocin tarayya da na jihohi, a kuma kawar da bambance-bambancen siyasa don samun cikakiyyar nasarar da ake bukata.

Dole gwamnonin jihohi su sauke nasu hakkokin da suka rataya a kansu, sun kuma hada da tabbatar da kiwon laifiya ya isa ga kowa, sayo magunguna da kuma horar da kananan ma’aikatan kiwon lafiya, domin gwamnatin tarayya ba zai yiwu ta sa hannunta a cikin komai ba.

Haka kuma bangaren masu zaman kansu na da muhimmiyar gudunmawar da za su iya bayarwa, wadanda suka hada da kafa kamfanonin harhada magunguna da kuma samar da magungunan rigakafin cututtukan kananan yara.

Tabbas ‘yan Nijeriya na da hakkin neman a samar masu da ingantaccen kiwon lafiya musamman ma ganin yadda bangaren ya tabarbare a ‘yan shekarun nan.Ya kamata kungiyoyi masu zaman kansu su dauki nauyin sa ido a kan yadda ake kashe kudaden da aka ware wa bangaren lafiya a cikin kasafin kudin duk shekara,da kuma irin ci gaban da ake samu a aikace-aikacen da aka bayyana za a yi.

Gidajen yada labarai kuma su bayar da labarun irin nasarorin da aka samu a bangaren, su kuma fallasa munanan ayyukan da ake yi duk a bangaren.

Tabbas Shugaba Tinubu ya bude kofar farfado da bangaren kiwon lafiya a Nijeriya wanda aka yi watsi da shi na tsawon shekaru masu yawa. Amma kuma nasarar wannan aikin ta ta’allaka ce a hannun dukkan masu ruwa da tsaki a bangaren, samar da issassun kudade da kuma sa ido a kan yadda ake kashe kudaden da aka ware.

2023
Leadership Hausa
Website |  + postsBio
  • Leadership Hausa
    Yadda Arsenal Ta Lashe Gasar Firimiya Bayan Shekara 22
  • Leadership Hausa
    Bukatar Kawo Karshen Akidar Kyamar Baki A Kasar Afirka Ta Kudu
  • Leadership Hausa
    Ikirarin Cewa Sanata Abdul’aziz Yari Abubakar, Marafan Sokoto, Nauyi Ne Ga Jihar Zamfara Da Jam’iyyar APC Ba Ta Da Tushe
  • Leadership Hausa
    Nazarin Kisan Gillar Da ‘Yan Kato Da Gora Suka Yi Wa Wani Matashi A Biniwe

MASU ALAKA

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi
Manyan Labarai

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

June 4, 2026
Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City
Wasanni

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili
Manyan Labarai

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Next Post
Bankwana Da 2023: Yamutsin Siyasa Da Zabubbuka

Bankwana Da 2023: Yamutsin Siyasa Da Zabubbuka

LABARAI MASU NASABA

Matatar Dangote Ta Ƙara Yawan Man Da Take Tacewa Zuwa Ganga 700,000

Matatar Dangote Ta Ƙara Yawan Man Da Take Tacewa Zuwa Ganga 700,000

June 4, 2026
Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

June 4, 2026
Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

June 4, 2026
Mun Kaɗu Matuƙa Kan Labarin Mutuwar ‘Yan Mauludi A Hanyar Saminaka – Gwamnan Kaduna

Gwamna Sani Ya Kashe Sama Da Naira Biliyan Ɗaya Kan Tallafin Ɗalibai A Kaduna – Kwamishina

June 4, 2026
Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

June 4, 2026
Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

June 4, 2026
Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

June 4, 2026
Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

June 4, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.