ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Buƙatar Kawo Ƙarshen Dogon Layi A Tashoshin Sayen Iskar CNG

by Leadership Hausa and Sulaiman
1 month ago

Tun bayan da gwamnatin tarayya ta ƙirƙiro tare da kuma ƙaddamar da shirin yin amfani da Iskar Gas na CNG, musamman, masu ababen hawa da dama a ƙasar sun yi maraba lale, da shirin.

Sun kalli, shirin a matsayin abinda suka shafe lokaci suna tsimayi, domin samar masu da sauƙi, musamman duba da irin tsawon lokacin da suke shafewa, na bin layi, a gidajen da ake sayar Iskar Gas ɗin.

Gwamnain Shugaba Bola Ahmed Tinubu mai ci, ta ƙirƙiro tare da kuma ƙaddamar da shirin bayan cire tallafin Man Fetur, musamman domin ƙarfafa wa masu ababen hawa, rungumar yin amfani da Isar ta CNG, a bisa burinta na ƙara bunƙasa fannin makamashi a ƙasar.

ADVERTISEMENT

Kazalika, burin na gwamnatin shi ne, domin masu ababen hawan, su sayi Iskar Gas ɗin ta CNG, a farashi mai rahusa.

Kamar dai tunain sauran ƴan ƙasar, ita ma wannan Jaridar, na kallon shirin a matsayin na CNG a matsayin babban abu na ci gaba, ga fannin sufurin ƙasar.

LABARAI MASU NASABA

Batun Shayar Da Jarirai Nonon Uwa Da Ƙalubalen Abinci Mai Gina Jiki

Ana Ci Gaba Da Tafka Muhawara Kan Shirin Gwamnati Na Haramta Masana’atun Sarrafa Robobi

Wani ƙarin abin la’akari da shirin shi ne, ba wai kawai za a samar da makamashi a farashi mai rahusa bane, ko rage tsadar sufuri, amma shirin, zai ƙara bunƙa tattalin arzikin ƙasar, kamar zuwa matki, irin na duniya.

Tuni dai, ƙasashen da suka ci gaba a duniya, ke ta faman kai gauro da mari, wajen ganin sun rage fitar da sanaran hayaƙin da ke gurbata muhalli, wanda kuma bai kamata, a bar Nijeriya a baya, wajen shiga cikin irin wannan sahun ba.

A bisa wannan hujjar, ita ma wannan Jaridar na goyon bayan, rungumar yin amfani da Iskar ta CNG.

Kazalika, Jaridar ta yi ammana da cewa, rungumar shirin zai taimaka, wajen rage fitar hayaƙin da ke gurɓata muhalli, tare da samar da ingantacciyar Iskar da ƴan Adam, za su iya shaƙa.

Shirin zai kuma rage yawan kuɗaɗen da masu ababen hawa a ƙasar ke kashewa, wajen ci gaba da gyaran ababen hawansu.

Duk da sukar da shirin ya ci karo da ita a baya daga wasu ƴan Nijeriya, musamman kan jinkirin fara gudanar da shi, amma masu ababen hawa da dama, sun karɓi shirin tare da ci gaba da yin amfani da shi, hannu bi-biyu.

Sai dai, inda Gizon ke saƙa a yanzu shi ne, murnar na masu ababen hawan kan shirin na zai samar masu da sauƙi, ta koma ciki, duba da yadda suke shafe awanni a gidajen da ake sayar da Iskar ta CNG.

Ƙarin wata matsalar shi ne, wasu masu ababen hawan musamman motoci, sun kai ga suna yin barci a gidajen sayar da shi, domin su samu damar saye.

Haka zalika, ana kuma ci gaba da fuskantar ƙarancinsa, musamman a mayan biranen ƙasar, ciki har da Abuja da jihar Legas, inda hakan, ya haifar da dogayen layuka, a gidajen da ake sayar da shi.

Ci gaba da ƙarancin na sa, tuni ya jefa shakku da kuma mayar da hannun Agogo baya, ga masu masu ababen hawan, domin a kafin zuwa shirin, sun yi imanin, shirin zai samar da sauƙi.

Tuni dai, wasu masu ababen hawan saboda ƙarancinsa, suka fara yin damar sauyawa, zuwa yin amfani da Iskar Gas ɗin.

Tambayoyin da suke ci gaba da yi ita ce, shin su ne, me ya janyo ƙarancin, mai gwamnatin ƙasar key i kan batun?Da alamu, akwai babban giɓi a ɓangaren gwamnatin na gazawar samar da manyan kayan aiki ga shirin, kafin a fara wanzar da shi.

Misali, rashin samar da tashoshi masu yawa, da masu ababen hawan, za su rinƙa zuwa, domin sayensa, inda kamar a Abuja da Legas, za a iya ƙirga adadin gidajen da ake sayar da shi, inda kuma a wasu manyan biranen ƙasar, ba a iya samu.

Wannan ya nuna cewa, ƴar ƙaramar nasara kwai, aka iya cimma a ƙarƙashin gwamnatin ta Bola Tinubu.Idan har ba a lalubo da mafita kan ƙarancin ba, masu ababen hawan da dama, za su koma yin amfani da Man Fetur, kamar yadda suka saba yi, a baya.

Gwamnatin ƙasar, ta san dabarun da ya kamata ta ɗauka domin kawo ƙarshen ƙarancin.Zuwan shirin, masu ababen hawan sun ɗauka ƙarashen kwanan su a gidajen Mai ta zo ke nan, saboda zuwa na CNG, amma sai gashi, sun sake komawa gidan jiya.

Ya zama wajbi, gwamnatin ta tabbatar da ta ƙara inganta shirin, musamman domin ta kawo ƴan ƙasar sauƙin sufuri.

Kazalika, ya kamata ta fafaɗa shirin domin janyo masu zuba jari daga kamfanonin masu zaman kansu, na cikin gida tare da kuma ɗaukar wasu matakan da suka wajaba, musamamin a kawo ƙarshen dogayen layukan da ske samu na sayen Iskar Gas ɗin.

Leadership Hausa
Website |  + posts Bio
  • Leadership Hausa
    Karuwar Farin Jinin Gwamna Umaru Bago A Siyasar Jihar Neja
  • Leadership Hausa
    Kyakkyawan Tsarin Laken Asiri Zai Dakile Shirin Magudin Zabe A Nijeriya —Mohammed
  • Leadership Hausa
    Batun Dawo Da Tallafin Mai Da Atiku Ya Yi Na Ci Gaba Da Tayar Da Kura
  • Leadership Hausa
    Batun Guguwar Kakar Yakin Neman Zabukan 2027 A Nijeriya
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5
  • Sulaiman
    Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana
  • Sulaiman
    ‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna
  • Sulaiman
    Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

MASU ALAKA

Ra'ayinmu

Batun Shayar Da Jarirai Nonon Uwa Da Ƙalubalen Abinci Mai Gina Jiki

August 14, 2026
Ana Ci Gaba Da Tafka Muhawara Kan Shirin Gwamnati Na Haramta Masana’atun Sarrafa Robobi
Ra'ayinmu

Ana Ci Gaba Da Tafka Muhawara Kan Shirin Gwamnati Na Haramta Masana’atun Sarrafa Robobi

July 10, 2026
Kisan Gillar Marabar Jos: Bai Kamata Jinin Malama Ummulkhairi Ya Tafi A Banza Ba
Ra'ayinmu

Kisan Gillar Marabar Jos: Bai Kamata Jinin Malama Ummulkhairi Ya Tafi A Banza Ba

July 3, 2026
Next Post
Ko Ya Halatta A Yi Kasuwanci Da Kudin Adashi? (Fatawa)

Yadda Jita-jitar Ƙayyade Sadaki Ta Tada Ƙura A Bauchi, Gwamanti Ta Yi Zazzafan Gargaɗi

LABARAI MASU NASABA

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026
Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

September 8, 2026
Wani Soja Ya Kashe Kansa Bayan Kashe Matarsa A Jihar Neja

Kano Za Ta Kafa Sansanonin Sojoji A Ƙananan Hukumomin Da Ke Fuskantar Barazanar Tsaro

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.