ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Barkewar Cutar Sankarau Ta Yi Sanadin Mutuwar Mutane Da Dama A Jihar Sokoto

by Rabi'u Ali Indabawa
1 month ago
Sankarau

Mazauna Kauyen Kurawa da ke Karamar Hukumar Sabon Birni a Jihar Sokoto sun bayyana fargaba kan barkewar cutar sankarau da ake zargin ta hallaka mutane da dama, galibi yara da matasa.

A cewar rahoton Daily Trust, majiyoyi daga cibiyar lafiya ta kauyen sun ce lamarin ya tsananta a ‘yan kwanakin nan, inda ake samun mutuwar mutane kimanin biyu zuwa uku a kowace rana, musamman wadanda shekarunsu ke tsakanin biyu zuwa 20.

Barkewar cutar ta haifar da firgici a cikin al’umma, yayin da mutane ke ta tururuwar zuwa asibiti suna neman magani kan abin da suka kira “cutar da ba a sani ba”.

ADVERTISEMENT

Wani ma’aikacin lafiya, wanda ya nemi a sakaya sunansa, ya ce cibiyar lafiya ta cika makil da marasa lafiya.

“Mutane na zuwa asibiti da yawa kowace rana domin neman magani. Mun cika sosai kuma ba mu san ainihin cutar da ke kashe mana mutane kusan kullum ba,” in ji shi.

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

Bayanan sun nuna cewa yawancin wadanda suka kamu da cutar sun mutu kafin a yi cikakken gwaji. Daga baya an shawarci mazauna yankin da su guji kwana a cikin dakuna a kulle saboda tsananin zafi da ake ganin na taimakawa wajen yaduwar cutar.

Mazauna yankin sun bayyana alamomi kamar suma, tsananin ciwon wuya, amai, gudawa, zazzabi mai tsanani, da kuma kumfa a baki a wasu lokuta, alamomin da suka yi kama da na cutar sankarau.

Wani mazaunin yankin ya bayyana yadda cutar ke saurin tsananta:

“A wasu lokuta, yaro zai fara korafin ciwon wuya kafin daga bisani ya suma.”

Duk da matakan jinya na farko, mazauna yankin sun nuna damuwa cewa cutar na ci gaba da yaduwa, wanda ya sa wasu ke zargin ko ba sankarau ba ce kawai.

“An gaya mana cewa sankarau ce, amma cutar ba ta tsaya ba. Shi ya sa mutane ke fara zargin ko wata cuta ce daban,” in ji su.

Sai dai wani jami’in asibiti ya ce mutuwar mutane uku kacal aka tabbatar a cibiyar, yana mai cewa yawancin wadanda suka mutu sun rasu ne a gida. Ya kara da cewa yawancin marasa lafiyar na mutuwa cikin awanni 24 bayan fara alamun cutar.

Dagacin Kauyen, Mudassir Abdullahi Kurawa, ya tabbatar da barkewar cutar, inda ya ce an samu mutuwar mutane tsakanin 10 zuwa 15 a cikin al’umma kadai, ba tare da hada da kauyukan da ke makotaka ba.

Ya ce yawancin wadanda suka kamu yara ne masu shekaru tsakanin biyu zuwa 10, kuma alamun cutar sun fara bayyana kimanin makonni uku da suka gabata.

Ya kara da cewa a ranar Asabar kadai an kwantar da marasa lafiya 15, inda uku daga cikinsu suka rasu jim kadan bayan isarsu asibiti.

A bangaren gwamnati, Kwamishinan Lafiya na Jihar Sokoto, Faruk Abubakar Wurno, ya tabbatar da cewa gwamnati ta fara bincike kan lamarin.

Ya ce an tura ma’aikatan lafiya yankin tare da samar da magunguna kyauta domin dakile cutar.

Sai dai ya bayyana cewa har yanzu ba a tabbatar da adadin wadanda suka mutu ba yayin da ake ci gaba da kokarin shawo kan lamarin da gano ainihin cutar.

Sankarau
Rabi'u Ali Indabawa
+ postsBio
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    NSCDC Ta Cafke Mutum 10 Da Ake Zargi Da Satar Kayan Gwamnati Da Kuma Fashi A Kano
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Ƴansanda Su Ƙi Karɓar Cin Hancin Naira Miliyan 500 Daga Hannun Dillalin Miyagun Ƙwayoyi
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Ƙasashen DR Congo Uganda Da Sudan Sun Haɗa Kai Domin Yaƙar Ibola
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Zafin Rana Ya Yi Ajalin Mutum 16 A Indiya

MASU ALAKA

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada
Labarai

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa
Labarai

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili
Manyan Labarai

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Next Post
Gaskiya Daya Ce

Gaskiya Daya Ce

Discussion about this post

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026
Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.