Mazauna Kauyen Kurawa da ke Karamar Hukumar Sabon Birni a Jihar Sokoto sun bayyana fargaba kan barkewar cutar sankarau da ake zargin ta hallaka mutane da dama, galibi yara da matasa.
A cewar rahoton Daily Trust, majiyoyi daga cibiyar lafiya ta kauyen sun ce lamarin ya tsananta a ‘yan kwanakin nan, inda ake samun mutuwar mutane kimanin biyu zuwa uku a kowace rana, musamman wadanda shekarunsu ke tsakanin biyu zuwa 20.
Barkewar cutar ta haifar da firgici a cikin al’umma, yayin da mutane ke ta tururuwar zuwa asibiti suna neman magani kan abin da suka kira “cutar da ba a sani ba”.
Wani ma’aikacin lafiya, wanda ya nemi a sakaya sunansa, ya ce cibiyar lafiya ta cika makil da marasa lafiya.
“Mutane na zuwa asibiti da yawa kowace rana domin neman magani. Mun cika sosai kuma ba mu san ainihin cutar da ke kashe mana mutane kusan kullum ba,” in ji shi.
Bayanan sun nuna cewa yawancin wadanda suka kamu da cutar sun mutu kafin a yi cikakken gwaji. Daga baya an shawarci mazauna yankin da su guji kwana a cikin dakuna a kulle saboda tsananin zafi da ake ganin na taimakawa wajen yaduwar cutar.
Mazauna yankin sun bayyana alamomi kamar suma, tsananin ciwon wuya, amai, gudawa, zazzabi mai tsanani, da kuma kumfa a baki a wasu lokuta, alamomin da suka yi kama da na cutar sankarau.
Wani mazaunin yankin ya bayyana yadda cutar ke saurin tsananta:
“A wasu lokuta, yaro zai fara korafin ciwon wuya kafin daga bisani ya suma.”
Duk da matakan jinya na farko, mazauna yankin sun nuna damuwa cewa cutar na ci gaba da yaduwa, wanda ya sa wasu ke zargin ko ba sankarau ba ce kawai.
“An gaya mana cewa sankarau ce, amma cutar ba ta tsaya ba. Shi ya sa mutane ke fara zargin ko wata cuta ce daban,” in ji su.
Sai dai wani jami’in asibiti ya ce mutuwar mutane uku kacal aka tabbatar a cibiyar, yana mai cewa yawancin wadanda suka mutu sun rasu ne a gida. Ya kara da cewa yawancin marasa lafiyar na mutuwa cikin awanni 24 bayan fara alamun cutar.
Dagacin Kauyen, Mudassir Abdullahi Kurawa, ya tabbatar da barkewar cutar, inda ya ce an samu mutuwar mutane tsakanin 10 zuwa 15 a cikin al’umma kadai, ba tare da hada da kauyukan da ke makotaka ba.
Ya ce yawancin wadanda suka kamu yara ne masu shekaru tsakanin biyu zuwa 10, kuma alamun cutar sun fara bayyana kimanin makonni uku da suka gabata.
Ya kara da cewa a ranar Asabar kadai an kwantar da marasa lafiya 15, inda uku daga cikinsu suka rasu jim kadan bayan isarsu asibiti.
A bangaren gwamnati, Kwamishinan Lafiya na Jihar Sokoto, Faruk Abubakar Wurno, ya tabbatar da cewa gwamnati ta fara bincike kan lamarin.
Ya ce an tura ma’aikatan lafiya yankin tare da samar da magunguna kyauta domin dakile cutar.
Sai dai ya bayyana cewa har yanzu ba a tabbatar da adadin wadanda suka mutu ba yayin da ake ci gaba da kokarin shawo kan lamarin da gano ainihin cutar.















Discussion about this post