ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Barkewar Cutar Sankarau Ta Yi Sanadin Mutuwar Mutane Da Dama A Jihar Sokoto

by Rabi'u Ali Indabawa
2 months ago
Sankarau

Mazauna Kauyen Kurawa da ke Karamar Hukumar Sabon Birni a Jihar Sokoto sun bayyana fargaba kan barkewar cutar sankarau da ake zargin ta hallaka mutane da dama, galibi yara da matasa.

A cewar rahoton Daily Trust, majiyoyi daga cibiyar lafiya ta kauyen sun ce lamarin ya tsananta a ‘yan kwanakin nan, inda ake samun mutuwar mutane kimanin biyu zuwa uku a kowace rana, musamman wadanda shekarunsu ke tsakanin biyu zuwa 20.

Barkewar cutar ta haifar da firgici a cikin al’umma, yayin da mutane ke ta tururuwar zuwa asibiti suna neman magani kan abin da suka kira “cutar da ba a sani ba”.

ADVERTISEMENT

Wani ma’aikacin lafiya, wanda ya nemi a sakaya sunansa, ya ce cibiyar lafiya ta cika makil da marasa lafiya.

“Mutane na zuwa asibiti da yawa kowace rana domin neman magani. Mun cika sosai kuma ba mu san ainihin cutar da ke kashe mana mutane kusan kullum ba,” in ji shi.

LABARAI MASU NASABA

Sojoji Sun Kama Mai Kai Wa Ƴan Ta’adda Kayan Aiki A Zamfara

Kotu Ta Ɗege Shari’ar Ganduje Da Wasu Mutum 7 Zuwa 14 Ga Oktoba 2026

Bayanan sun nuna cewa yawancin wadanda suka kamu da cutar sun mutu kafin a yi cikakken gwaji. Daga baya an shawarci mazauna yankin da su guji kwana a cikin dakuna a kulle saboda tsananin zafi da ake ganin na taimakawa wajen yaduwar cutar.

Mazauna yankin sun bayyana alamomi kamar suma, tsananin ciwon wuya, amai, gudawa, zazzabi mai tsanani, da kuma kumfa a baki a wasu lokuta, alamomin da suka yi kama da na cutar sankarau.

Wani mazaunin yankin ya bayyana yadda cutar ke saurin tsananta:

“A wasu lokuta, yaro zai fara korafin ciwon wuya kafin daga bisani ya suma.”

Duk da matakan jinya na farko, mazauna yankin sun nuna damuwa cewa cutar na ci gaba da yaduwa, wanda ya sa wasu ke zargin ko ba sankarau ba ce kawai.

“An gaya mana cewa sankarau ce, amma cutar ba ta tsaya ba. Shi ya sa mutane ke fara zargin ko wata cuta ce daban,” in ji su.

Sai dai wani jami’in asibiti ya ce mutuwar mutane uku kacal aka tabbatar a cibiyar, yana mai cewa yawancin wadanda suka mutu sun rasu ne a gida. Ya kara da cewa yawancin marasa lafiyar na mutuwa cikin awanni 24 bayan fara alamun cutar.

Dagacin Kauyen, Mudassir Abdullahi Kurawa, ya tabbatar da barkewar cutar, inda ya ce an samu mutuwar mutane tsakanin 10 zuwa 15 a cikin al’umma kadai, ba tare da hada da kauyukan da ke makotaka ba.

Ya ce yawancin wadanda suka kamu yara ne masu shekaru tsakanin biyu zuwa 10, kuma alamun cutar sun fara bayyana kimanin makonni uku da suka gabata.

Ya kara da cewa a ranar Asabar kadai an kwantar da marasa lafiya 15, inda uku daga cikinsu suka rasu jim kadan bayan isarsu asibiti.

A bangaren gwamnati, Kwamishinan Lafiya na Jihar Sokoto, Faruk Abubakar Wurno, ya tabbatar da cewa gwamnati ta fara bincike kan lamarin.

Ya ce an tura ma’aikatan lafiya yankin tare da samar da magunguna kyauta domin dakile cutar.

Sai dai ya bayyana cewa har yanzu ba a tabbatar da adadin wadanda suka mutu ba yayin da ake ci gaba da kokarin shawo kan lamarin da gano ainihin cutar.

Sankarau
Rabi'u Ali Indabawa
+ postsBio
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Nijar Ta Rattaba Hannu A Kan Dokar Haramta Auren Jinsi
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Za Mu Iya Sayar Da Manmu Ba Tare Da Wata Matsala Ba -Iran
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Dattawan Arewa Sun Buƙaci Tinubu Ya Ayyana Dokar Ta-baci Kan Tabarbarewar Tsaro
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Nijeriya Ta Karbi Ƴan Nijeriya 268 Da Suka Tsero Daga Afirka Ta Kudu

MASU ALAKA

Sojoji Sun Kama Mai Kai Wa Ƴan Ta’adda Kayan Aiki A Zamfara
Tsaro

Sojoji Sun Kama Mai Kai Wa Ƴan Ta’adda Kayan Aiki A Zamfara

June 25, 2026
Kotu Ta Ɗege Shari’ar Ganduje Da Wasu Mutum 7 Zuwa 14 Ga Oktoba 2026
Manyan Labarai

Kotu Ta Ɗege Shari’ar Ganduje Da Wasu Mutum 7 Zuwa 14 Ga Oktoba 2026

June 25, 2026
An Fara Gasar Tseren Dawakai Ta ‘Renewed Hope’ da Sabon Salo A Kano
Labarai

An Fara Gasar Tseren Dawakai Ta ‘Renewed Hope’ da Sabon Salo A Kano

June 25, 2026
Next Post
Gaskiya Daya Ce

Gaskiya Daya Ce

LABARAI MASU NASABA

Ƙungiyar NPCF Ta Yi Barazanar Janye Goyon Bayanta Ga Tinubu

Ƙungiyar NPCF Ta Yi Barazanar Janye Goyon Bayanta Ga Tinubu

June 25, 2026
Firaministan Sin Ya Halarci Taron Tattaunawa Da Wakilan ‘Yan Kasuwa Mahalarta Dandalin Tattalin Arzikin Duniya Na DAVOS

Firaministan Sin Ya Halarci Taron Tattaunawa Da Wakilan ‘Yan Kasuwa Mahalarta Dandalin Tattalin Arzikin Duniya Na DAVOS

June 25, 2026
Sojoji Sun Kama Mai Kai Wa Ƴan Ta’adda Kayan Aiki A Zamfara

Sojoji Sun Kama Mai Kai Wa Ƴan Ta’adda Kayan Aiki A Zamfara

June 25, 2026
Kotu Ta Ɗege Shari’ar Ganduje Da Wasu Mutum 7 Zuwa 14 Ga Oktoba 2026

Kotu Ta Ɗege Shari’ar Ganduje Da Wasu Mutum 7 Zuwa 14 Ga Oktoba 2026

June 25, 2026
An Fara Gasar Tseren Dawakai Ta ‘Renewed Hope’ da Sabon Salo A Kano

An Fara Gasar Tseren Dawakai Ta ‘Renewed Hope’ da Sabon Salo A Kano

June 25, 2026
APC Ta Dage Yakin Zaben Shugaban Kasarta A Kano

An Dakatar Da Shugaban APC Na Kebbi Da Kwamishina Kan Zaɓen Cike Gurbin Zuru

June 25, 2026
Ndume Ya Bayyana Dalilin Da Ya Sa Yake Goyon Bayan Ƙudirin Kafa ‘Yansandan Jihohi

Ndume Ya Bayyana Dalilin Da Ya Sa Yake Goyon Bayan Ƙudirin Kafa ‘Yansandan Jihohi

June 25, 2026
EFCC Za Ta Gurfanar Da Shugaban Miyetti Allah Kan Zargin Almundahanar Dala Miliyan 2.53

EFCC Za Ta Gurfanar Da Shugaban Miyetti Allah Kan Zargin Almundahanar Dala Miliyan 2.53

June 25, 2026
Maroko Ta Zama Ƙasa Ta Farko Daga Afirka Da Ta Tsallaka Zuwa Zagaye Na 32 A Gasar Kofin Duniya

Maroko Ta Zama Ƙasa Ta Farko Daga Afirka Da Ta Tsallaka Zuwa Zagaye Na 32 A Gasar Kofin Duniya

June 25, 2026
Zan Ware 10bn Don Inganta Ilimin Matasa Idan Na Ci Zabe – Atiku

‘Yan Nijeriya Ba Sa Bukatar ‘Yan Jarida Su Faɗa Musu Suna Jin Yunwa — Atiku

June 25, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.