ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, June 24, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gaskiya Daya Ce

by CGTN Hausa and Sulaiman
2 months ago
Gaskiya

Aboki na gaske shi ne wanda zai lura da moriyarka. To, a bisa wannan sharadi, za mu san cewa, ba shakka kasar Sin wata abokiya ce ta gaske ga kasashen Afirka.Daga yau Juma’a, kasar Sin ta kaddamar da manufar yafe harajin kwastam kan kayayyakin da kasashe 53 dake nahiyar Afirka, wadanda suka kulla huldar diflomasiyya da ita, ke fitarwa zuwa kasuwanninta.

Ta haka, za a biya bukatun kasashen Afirka na fitar da karin kayayyaki zuwa karin wurare daban daban, tare da samun karin kudin shiga.Mene ne ainihin tasirin manufar nan ta yafe wa kasashen Afirka harajin kwastam? Za a samu amsa ta hanyar nazari kan misalin kasar Habasha.

Kasar Sin ta fara yafe wa kasar Habasha harajin kwastam tun daga karshen shekarar 2024, bisa la’akari da matsayin kasar na daya daga cikin kasashe mafi fama da koma bayan tattalin arziki a duniya.

ADVERTISEMENT

Daga baya, tsakanin shekarar 2024 da ta 2025, kasar Habasha ta fitar da waken gahawa (‘ya’yan kofi) fiye da tan dubu 34 zuwa kasar Sin, adadin da ya karu da kaso 27%, bisa jimillar lokacin da ya gabace shi.Haka zalika, dimbin bukatun da ake samu daga kasuwannin kasar Sin, ya sa kamfanoni masu samar da gahawa na kasar Habasha iya mai da hankali wajen raya bangaren sarrafa waken gahawa, ta yadda aka inganta tsare-tsaren bangaren samar da gahawa na kasar Habasha sosai.

Manufar kasar Sin ta yafe wa kasashen Afirka harajin kwastam tana cike da sahihanci, saboda tana haifar wa kasashen Afirka da fa’ida, kana maimakon ta kasance wani nau’in tallafi mai dauke da sharadi, ita ce manufar da take tabbatar da moriyar dukkan bangarorin Afirka da Sin, da makomarsu ta samun ci gaba na bai daya.Za mu iya ci gaba da daukar gahawa a matsayin misali.

LABARAI MASU NASABA

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Sin Na Daukar hakikanan Matakan Gina Kyakkaywar Makomar Al’ummun Sin Da Afirka Ta Bai Daya

Ta hanyar yafe harajin kwastam da ake karba kan waken gahawa da ake shigar da su kasuwannin kasar Sin daga kasashen Afirka, to, mutanen kasar Sin za su iya sayen waken da farashi mai araha, kana su kamfanonin Sin da Afirka za su kara nuna niyyar zuba jari don habaka masana’antun sarrafa waken gahawa, tare da samar da karin guraben aikin yi a Afirka.

To, wannan misali ya nuna yadda ake tabbatar da moriyar dukkan bangarorin Sin da Afirka ta manufar nan ta yafe harajin kwastam.Ban da haka, za mu iya fahimtar sahihanci da manufar nan ta kunsa, ta hanyar kwatanta ta da manufofi na sauran kasashe.

A lokacin da wasu kasashe ke daukar matakan kashin kai don cin zarafin sauran kasashe, da kwace dukiyoyinsu, manufar da kasar Sin ta dauka ta zama mai samar da alfanu ga kasashen Afirka, wadda za ta tabbatar da kyakkyawar makomar hadin gwiwar bangarorin Sin da Afirka.

“A wannan lokacin da muke ciki, na fama da yanayin rashin tabbas a duniya, manufar nan da kasar Sin ta dauka tallafi ne da aka bayar kan lokaci, wanda ya kansace nau’in tallafin da ake samu daga ‘yan uwa”, in ji shugaban kwamitin gudanarwa na kungiyar kasashen Afirka ta AU, Mahamoud Ali Youssouf. (Bello Wang)

Gaskiya
CGTN Hausa
+ posts Bio
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje
Gaskiya
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”
  • Sulaiman
    Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi
  • Sulaiman
    Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba
  • Sulaiman
    Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

MASU ALAKA

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”
Ra'ayi Riga

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Sin Na Daukar hakikanan Matakan Gina Kyakkaywar Makomar Al’ummun Sin Da Afirka Ta Bai Daya
Ra'ayi Riga

Sin Na Daukar hakikanan Matakan Gina Kyakkaywar Makomar Al’ummun Sin Da Afirka Ta Bai Daya

June 19, 2026
A Yi Watsi Da Wannan “Mummunan Teburi”
Ra'ayi Riga

A Yi Watsi Da Wannan “Mummunan Teburi”

June 18, 2026
Next Post
Albishir Ga Iyayen Da Suka Karantar Da ‘Ya’yansu Alkur’ani (2)

Albishir Ga Iyayen Da Suka Karantar Da 'Ya'yansu Alkur'ani (2)

LABARAI MASU NASABA

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026
Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

June 24, 2026
Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

June 24, 2026
Yadda Na Sayar Da Kadarori Na Don Ɗaukar Nauyin Ɗalibai A Ƙasashen Waje – Kwankwaso

Zargin Ɓata Suna: Kwankwaso Ya Yi Barazanar Neman Diyyar Naira Biliyan 10 Kan Wani Malamin Coci

June 24, 2026
Li Qiang Ya Halarci Bikin Bude Dandalin Tattalin Arzikin Duniya Na Davos Na Shekarar 2026

Li Qiang Ya Halarci Bikin Bude Dandalin Tattalin Arzikin Duniya Na Davos Na Shekarar 2026

June 24, 2026
Xi Ya Yi Kiran Daukar Matakan Zamanantar Da Aikin Gona Da Yankunan Karkara

Xi Ya Yi Kiran Daukar Matakan Zamanantar Da Aikin Gona Da Yankunan Karkara

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.