Aboki na gaske shi ne wanda zai lura da moriyarka. To, a bisa wannan sharadi, za mu san cewa, ba shakka kasar Sin wata abokiya ce ta gaske ga kasashen Afirka.Daga yau Juma’a, kasar Sin ta kaddamar da manufar yafe harajin kwastam kan kayayyakin da kasashe 53 dake nahiyar Afirka, wadanda suka kulla huldar diflomasiyya da ita, ke fitarwa zuwa kasuwanninta.
Ta haka, za a biya bukatun kasashen Afirka na fitar da karin kayayyaki zuwa karin wurare daban daban, tare da samun karin kudin shiga.Mene ne ainihin tasirin manufar nan ta yafe wa kasashen Afirka harajin kwastam? Za a samu amsa ta hanyar nazari kan misalin kasar Habasha.
Kasar Sin ta fara yafe wa kasar Habasha harajin kwastam tun daga karshen shekarar 2024, bisa la’akari da matsayin kasar na daya daga cikin kasashe mafi fama da koma bayan tattalin arziki a duniya.
Daga baya, tsakanin shekarar 2024 da ta 2025, kasar Habasha ta fitar da waken gahawa (‘ya’yan kofi) fiye da tan dubu 34 zuwa kasar Sin, adadin da ya karu da kaso 27%, bisa jimillar lokacin da ya gabace shi.Haka zalika, dimbin bukatun da ake samu daga kasuwannin kasar Sin, ya sa kamfanoni masu samar da gahawa na kasar Habasha iya mai da hankali wajen raya bangaren sarrafa waken gahawa, ta yadda aka inganta tsare-tsaren bangaren samar da gahawa na kasar Habasha sosai.
Manufar kasar Sin ta yafe wa kasashen Afirka harajin kwastam tana cike da sahihanci, saboda tana haifar wa kasashen Afirka da fa’ida, kana maimakon ta kasance wani nau’in tallafi mai dauke da sharadi, ita ce manufar da take tabbatar da moriyar dukkan bangarorin Afirka da Sin, da makomarsu ta samun ci gaba na bai daya.Za mu iya ci gaba da daukar gahawa a matsayin misali.
Ta hanyar yafe harajin kwastam da ake karba kan waken gahawa da ake shigar da su kasuwannin kasar Sin daga kasashen Afirka, to, mutanen kasar Sin za su iya sayen waken da farashi mai araha, kana su kamfanonin Sin da Afirka za su kara nuna niyyar zuba jari don habaka masana’antun sarrafa waken gahawa, tare da samar da karin guraben aikin yi a Afirka.
To, wannan misali ya nuna yadda ake tabbatar da moriyar dukkan bangarorin Sin da Afirka ta manufar nan ta yafe harajin kwastam.Ban da haka, za mu iya fahimtar sahihanci da manufar nan ta kunsa, ta hanyar kwatanta ta da manufofi na sauran kasashe.
A lokacin da wasu kasashe ke daukar matakan kashin kai don cin zarafin sauran kasashe, da kwace dukiyoyinsu, manufar da kasar Sin ta dauka ta zama mai samar da alfanu ga kasashen Afirka, wadda za ta tabbatar da kyakkyawar makomar hadin gwiwar bangarorin Sin da Afirka.
“A wannan lokacin da muke ciki, na fama da yanayin rashin tabbas a duniya, manufar nan da kasar Sin ta dauka tallafi ne da aka bayar kan lokaci, wanda ya kansace nau’in tallafin da ake samu daga ‘yan uwa”, in ji shugaban kwamitin gudanarwa na kungiyar kasashen Afirka ta AU, Mahamoud Ali Youssouf. (Bello Wang)















Discussion about this post