Rundunar sojin juyin juya hali ta Iran, ta sanar da haramta wucewar duk wani jirgin ruwa ta mashigin Hormuz, muddun ya fito ko ya nufi tashoshin kasashe kawayen ko magoya bayan Amurka da Isra’ila, lamarin da ya kara ta’azzara rikicin na Iran.
Wani nazari da kafar CGTN ta gudanar ta intanet ya nuna cewa, kaso 89.6 na masu bayar da amsa na ganin rikicin Iran ya kara mayar da Amurka saniyar ware a duniya.
A cewar Poria Kolivand, mataimakin wakilin Iran na dindindin a hukumar kula da harkokin teku ta duniya (IMO), tun bayan da Amurka da Isra’ila suka kaddamar da hare-hare kan Iran, an kashe sama da mutane 1,700 da jikkata 22,800 kana kimanin miliyan 3.5 sun rasa matsugunansu, baya ga kayayyakin fararen hula 81,000 da aka lalata a kasar ta Iran.
Cikin nazarin, mutanen da suka bayar da amsa da yawansu ya kai kaso 92.4 sun amince cewa, matakan soji na Amurka da Isra’ila, sun keta dokokin kasa da kasa da ka’idojin dangantakar kasa da kasa.
Amfani da karfi bai taba zama daidaitacciyar hanyar warware rikice-rikice ba, sai dai kara kiyayya da fito-na-fito. Cikin nazarin, kaso 65 na masu bayar da amsa sun yarda cewa, abu mafi muhimmanci shi ne dakatar da bude wuta nan take, kuma dukkan bangarori su kauracewa furta kalamai ko aiwatar da abubuwan da ka iya rikita lamarin.
Kafar CGTN ta wallafa nazarin ne a dandalolinta na harsunan Turancin Inglishi da Sipaniyanci da Faransanci da Larabci da Rashanci, inda mutane 13,731 suka bayyana ra’ayoyinsu cikin sa’o’i 24. (Fa’iza Mustapha)















Discussion about this post