A kwanan baya, shugaban dandalin tattauna harkokin tattalin arzikin duniya (WEF), mista Borge Brende, ya zanta da wakilin kafar CMG, inda ya yi tsokaci kan rawar da kasar Sin ke takawa a fannin kare ra’ayin kasancewar bangarori masu fada-a-ji da yawa a duniya, da sa kaimi ga hadin gwiwar kasashe daban daban. A cewarsa, kasar Sin har kullum tana jaddada muhimmancin neman ci gaban hadin gwiwarta tare da sauran kasashe.
Mista Brende ya ce, zai fi sauki ga wata babbar kasa ta dauki mataki na kashin kai, amma a nata bangare kasar Sin ta fi son karfafa hadin gwiwa tare da sauran kasashe. A ganin Mista Brende, wannan manufa ta kasar Sin tana da ma’ana sosai, saboda dimbin kalubalolin da dan Adam ke fuskantar yanzu, ba za a iya daidaita su ba, idan aka gaza tabbatar da hadin kan kasashe daban daban.
Ban da haka, Borge Brende ya tabo batu kan jawabin da shugaba Xi Jinping na kasar Sin ya gabatar, a yayin bikin kaddamar da taron shekara-shekara na WEF na shekarar 2017, inda ya ce jawabin mai muhimmanci, ya nuna niyyar kasar Sin ta magance daukar matakin kashin kai. Maimakon haka, kasar Sin ta fi son samar da nagartaccen tasiri a duniya, ta hanyar hadin gwiwar kasa da kasa.
Haka zalika, Mista Brende ya ce kasar Sin tana da kwarewa a fannin raba albarkatu, da kudi tsakanin sassanta daban daban, ta hanyar tsara shirin raya kasa na shekaru biyar-biyar, abin da ya ba ta damar zuba karin kudi a bangaren nazarin kimiyya da fasaha, da raya jami’o’i, da dai sauransu. Ya ce hakan ne ya sa kasar samun karin fifiko, yayin da take takara da sauran kasashe. (Bello Wang)















Discussion about this post