ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Borno Da Kano Sun Zama Zakaru A Gasar Karatun Alƙur’ani Ta Ƙasa Ta 2025

by Abubakar Sulaiman
9 months ago
Kano

Jihohin Borno da Kano sun lashe matsayi na gaba ɗaya a bangaren maza da mata a Gasar Karatun Alƙur’ani ta Ƙasa ta 2025 da aka gudanar a jihar Borno. Daraktan Cibiyar Nazarin Musulunci ta Jami’ar Usman Dan Fodio da ke Sakkwato, Farfesa Abubakar Yelwa, ne ya sanar da Musa Ahmed Musa daga Borno a matsayin zakaran maza, yayin da Hafsat Muhammad Sada daga Kano ta lashe matsayi na gaba ɗaya a bangaren mata.

Gasar, wadda ta ɗauki tsawon mako guda kuma ita ce ta 40 a jerin, ta haɗa mahalarta 296 daga jihohi 30, inda suka fafata a rukuni shida na karatun Alƙur’ani. Wannan gagarumar gasa ta jawo manyan malamai, mahaddata da baƙi daga sassa daban-daban na ƙasar.

  • Jami’an Hisbah Sun Kama Katon-katon Na Giya A Kano
  • Ƴansanda Sun Tsaurara MatakanTsaro A Borno Gabanin Ziyarar Tinubu

Gwamnan Jihar Borno, Farfesa Babagana Umara Zulum, ya ce nasarar karɓar bakuncin gasar ta 2025 alama ce ta dawowar zaman lafiya a jihar. Ya bayyana cewa gasar ta nuna ƙudurin al’ummar Borno na zaman lafiya, ilimi da neman sani, musamman hikimar Ubangiji da ke cikin Alƙur’ani Mai Girma.

ADVERTISEMENT

Zulum ya taya zakarun murna tare da yabawa duk mahalarta, yana mai cewa nasarar ba wai cin kofi kawai ba ce, illa sakamakon jajircewa, ladabi da girmama Kalmar Allah. Ya ƙara da cewa dukkan matasa maza da mata da suka halarci gasar su ma zakaru ne saboda jajircewarsu wajen neman ilimi da shiga wannan gasa mai albarka.

Gwamnan ya kuma nuna godiya ga Mataimakin Shugaban Ƙasa Kashim Shettima da uwargidansa Hajiya Nana Kashim Shettima, gwamnonin jihohi da mataimakansu, sarakunan gargajiya, Jami’ar Usman Dan Fodio da sauran manyan baƙi. Taron ya samu halartar uwargidan Mataimakin Shugaban Ƙasa, Gwamnan Katsina Dikko Umaru Radda, Shehun Borno, Alhaji Abubakar Ibn Umar Garbai El-Kanemi, ’yan majalisa, malamai da sauran fitattun jama’a.

LABARAI MASU NASABA

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

Kano
Abubakar Sulaiman
Website |  + postsBio
  • Abubakar Sulaiman
    Iyalin El-Rufai Sun Bai Ministan Tsaro Wa’adin Kwana 7 Kan Zargin Rikicin Kudancin Kaduna
  • Abubakar Sulaiman
    Atiku Ya Zargi Gwamnatin Tarayya Da Cin Bashi Kamar Mashayin Da Kuɗi Ya Ƙarewa
  • Abubakar Sulaiman
    Boko Haram Ta Kai Hari Adamawa, Ana Fargabar Mutuwar Mutane 11
  • Abubakar Sulaiman
    Ƴan Bindiga Sun Kai Hari Sokoto, Sun Kashe Mutane 7, Sun Yi Garkuwa Da 12

MASU ALAKA

Sojoji
Manyan Labarai

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

September 9, 2026
'Yan Bindiga
Labarai

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina
Labarai

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Next Post
Ban Dogara Da Harkar Fim Shi Kadai A Rayuwata Ba — Maryam Usman(2)

Ban Dogara Da Harkar Fim Shi Kadai A Rayuwata Ba — Maryam Usman(2)

LABARAI MASU NASABA

Sojoji

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

September 9, 2026
Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026
Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.