ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Borno Da Kano Sun Zama Zakaru A Gasar Karatun Alƙur’ani Ta Ƙasa Ta 2025

by Abubakar Sulaiman
6 months ago
Kano

Jihohin Borno da Kano sun lashe matsayi na gaba ɗaya a bangaren maza da mata a Gasar Karatun Alƙur’ani ta Ƙasa ta 2025 da aka gudanar a jihar Borno. Daraktan Cibiyar Nazarin Musulunci ta Jami’ar Usman Dan Fodio da ke Sakkwato, Farfesa Abubakar Yelwa, ne ya sanar da Musa Ahmed Musa daga Borno a matsayin zakaran maza, yayin da Hafsat Muhammad Sada daga Kano ta lashe matsayi na gaba ɗaya a bangaren mata.

Gasar, wadda ta ɗauki tsawon mako guda kuma ita ce ta 40 a jerin, ta haɗa mahalarta 296 daga jihohi 30, inda suka fafata a rukuni shida na karatun Alƙur’ani. Wannan gagarumar gasa ta jawo manyan malamai, mahaddata da baƙi daga sassa daban-daban na ƙasar.

  • Jami’an Hisbah Sun Kama Katon-katon Na Giya A Kano
  • Ƴansanda Sun Tsaurara MatakanTsaro A Borno Gabanin Ziyarar Tinubu

Gwamnan Jihar Borno, Farfesa Babagana Umara Zulum, ya ce nasarar karɓar bakuncin gasar ta 2025 alama ce ta dawowar zaman lafiya a jihar. Ya bayyana cewa gasar ta nuna ƙudurin al’ummar Borno na zaman lafiya, ilimi da neman sani, musamman hikimar Ubangiji da ke cikin Alƙur’ani Mai Girma.

ADVERTISEMENT

Zulum ya taya zakarun murna tare da yabawa duk mahalarta, yana mai cewa nasarar ba wai cin kofi kawai ba ce, illa sakamakon jajircewa, ladabi da girmama Kalmar Allah. Ya ƙara da cewa dukkan matasa maza da mata da suka halarci gasar su ma zakaru ne saboda jajircewarsu wajen neman ilimi da shiga wannan gasa mai albarka.

Gwamnan ya kuma nuna godiya ga Mataimakin Shugaban Ƙasa Kashim Shettima da uwargidansa Hajiya Nana Kashim Shettima, gwamnonin jihohi da mataimakansu, sarakunan gargajiya, Jami’ar Usman Dan Fodio da sauran manyan baƙi. Taron ya samu halartar uwargidan Mataimakin Shugaban Ƙasa, Gwamnan Katsina Dikko Umaru Radda, Shehun Borno, Alhaji Abubakar Ibn Umar Garbai El-Kanemi, ’yan majalisa, malamai da sauran fitattun jama’a.

LABARAI MASU NASABA

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

Kano
Abubakar Sulaiman
Website |  + postsBio
  • Abubakar Sulaiman
    Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi
  • Abubakar Sulaiman
    Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 2, Sun Yi Garkuwa Da 30 A Kogi
  • Abubakar Sulaiman
    Gwamnatina Za Ta Mayar Da Hankali Kan Buƙatun Al’ummar Nasarawa – Wadada
  • Abubakar Sulaiman
    Ƴan Bindiga Sun Kai Hari Masallaci, Sun Kashe Wani Yaro A Kaduna

MASU ALAKA

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi
Labarai

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi
Manyan Labarai

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

June 4, 2026
Mun Kaɗu Matuƙa Kan Labarin Mutuwar ‘Yan Mauludi A Hanyar Saminaka – Gwamnan Kaduna
Labarai

Gwamna Sani Ya Kashe Sama Da Naira Biliyan Ɗaya Kan Tallafin Ɗalibai A Kaduna – Kwamishina

June 4, 2026
Next Post
Ban Dogara Da Harkar Fim Shi Kadai A Rayuwata Ba — Maryam Usman(2)

Ban Dogara Da Harkar Fim Shi Kadai A Rayuwata Ba — Maryam Usman(2)

LABARAI MASU NASABA

Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

June 4, 2026
Mun Kaɗu Matuƙa Kan Labarin Mutuwar ‘Yan Mauludi A Hanyar Saminaka – Gwamnan Kaduna

Gwamna Sani Ya Kashe Sama Da Naira Biliyan Ɗaya Kan Tallafin Ɗalibai A Kaduna – Kwamishina

June 4, 2026
Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

June 4, 2026
Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

June 4, 2026
Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

June 4, 2026
Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

June 4, 2026
Ana Gudanar Da Taron Masana Ilmin Harkokin Kasar Sin Karo Na Uku

Ana Gudanar Da Taron Masana Ilmin Harkokin Kasar Sin Karo Na Uku

June 4, 2026
Sin: Ya Kamata Tarayyar Turai Ta Dubi Huldar Tattalin Arziki Da Ciniki Tsakaninta Da Sin Bisa Daidaito

Sin: Ya Kamata Tarayyar Turai Ta Dubi Huldar Tattalin Arziki Da Ciniki Tsakaninta Da Sin Bisa Daidaito

June 4, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.