ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Buƙatar Magance Kisan Kiyashi Da Ƴan Bindiga Suka Yi A Kasuwar Neja

by Ra'ayinmu
4 months ago
Neja

A watan Janairun 2026 ne, wasu ƴan bindiga, suka kutsa cikin babbar kasuwar Daji, da ke a jihar Neja, inda suka yiwa mutane, sama da 40, kisan gilla.

Wannan mummunan ta’addacin dai, ya nuna a zahiri, irin yanayin lamarin ƙalubalen rashin tsaro, da ƙasar ke ci gaba da fuskanta.

Duk da yawan shelar da gwamnati ke ci gaba da yi na cewa, tana ci gaba da ɗaukar matakai, domin lalubo da mafita kan wannan matsalar, amma ana kuma, ƴan bindiga da kuma ƴan ta’adda, na ci gaba da ɗaukar rayukan alummar, da ba su ji, ba su kuma gani ba.

ADVERTISEMENT
  • AFCON 2025: Zan Taimaka Wa Uganda Ta Doke Super Eagles Duk Da Mahaifina Ɗan Nijeriya Ne – Ikpeazu
  • Kafa Kamfanin Sarrafa Gwal A Legas: Ƙungiyar Dattawan Arewa Ta Ƙalubalanci Tinubu

Lamarin ka hallaka mutane, ba gari ba sabat, kusan za a iya cewa, sai ƙara zamowa yake yi runwan dare, a ƙasar, inda hakan ke ci gaba da yin hannun riga, na iƙirarin gwamnatin, na shawo kan matsalar.

Akasarin ƴan Nijeriya dai, na da yaƙin cewa, batun ƙoƙarin na gwamnati kan shawo kan matsalar, a fatar baki ne kawai.

LABARAI MASU NASABA

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Babban abin takaicin shi, da tsakiyar rana ne, ƴan bindigar, suka kutsa cikin kasuwar, suka ƙaddamar da aika-aikar tasu, ta hanyar yin amfani da muggan makamai.

Harin na jihar Neja, ya dai kasance, tamkar a cikin film ɗin ban tsaro, inda maharani, suka ɗaure waɗanda lamarin ya rutsa da su, suka kuma yiwa aƙalla ƴan kasuwa 30, yankan Rago, suka kuma shiga cikin wasu yankuna suka buɗe wuta suka kashe wasu a yankin, tare da cinnawa wasu gidaje wuta.

Shin ya za a ce, waɗannan marasa imanin har suka kammala aikata ta’asarsu, ba tare da jami’an tsaro, sun kawo ɗauki ba?

Kazalika, shin wasu daga cikin mazuna yankin sun yi gaggawar kai rahoton haring a ofishin ƴansanda mafi kusa?

Ya ya matsayin batun tura jami’an tsaro zuwa yankin, tun bayan aukuwar harin da ƴanbinda suka kai a makarantar Papiri?

Duk da cewa, ƙasar nan, ba wai tana a cikin yanayi na yaƙi bane, amma mai ya sa, mutane ba su iya yawo salin alin a cikin ƙasar ko kuma zuwa kasuwa, amma sai sun fuskanci matsalar tsaro?

Daga cikin waɗanda maharani suka hallaka, har da yara, ba tare da sun akita wani laifi ba.

Wasu mazauna yankin sun ce, maharan, sun yiwa kasuwar ƙawanya ne biyan sun fito daga mavoyarsu da ke a jejin  Kainji National Park, inda hakan, nuna cewa, mavoyar ta su, dama can sananniya ce.

Idan har malafar ta su, a cikin jama’a take, shin me ya haɗa jami’an tsaron tarwatsa su, daga sansannin na su?

Nisan da ke daga kasuwar zuwa yankin  Papiri na ƙaramar hukumar  Agwara, inda aka sace ɗalibai sama da 200, a ranar 21 ga watan Nuwambar 2025, na makarantar St. Mary’s Catholic , bai da wata nisa.

Hakan dai, ya nuna irin gazawar gwamnati na magance ƙalubalen rashin tsaro a jihar.

Lamarin dai, na ci gaba da haifar da shakku a zukatan jama’a, duba da yadda maharan, suka kutsa cikin kasuwar suka kuma kci Karensu, babu babbaka, tare da satar kayan abinci da kaya masu tsada,

Jihar dai, ta jima tana fusknatan hare-haren ƴan bindiga, inda akasari, gwamnati kawai ke fitar da sanarwar, yin tir da duk wani hari da aka kai.

Bugu da ƙari, bayan kai harin na kasuwar Dajin shugaba Bola Tinubu, ya fitar da sanawar tin tir, da kai harin, tare da umartar jami’an tsaro da su kamo maharani da kuma kuvutar da waɗanda maharani suka sace.

Mun dai faɗa cewa, akwai buƙatar gwamnati, ta ƙara ƙarfafa magance matsalar ta rashin tsaro, a ɗaukacin faɗin ƙasar.

Idan da za tambayi ƴan Nijeriya me suka fi buƙata a tsakanin samar masu da ababen more rayuwa da tsaro, tabbas, za su ce, sun fi buƙatar a samar masu da tsaro.

Wannan Jaridar, na jajatanwa iyalai da kuma ƴan uwan waɗanda lamarin, ya rutsa da su, a harin na kasuwar, inda kuma waɗanda suka samu raunuka, muke masu fatan Allah ya ba su lafiya Ya zama wajibi, gwamatin ta tashi haiƙan domin samar da tsaro a ɗaukacin faɗin ƙasar, tun kafin lokaci ya ƙure.

Neja
Ra'ayinmu
+ postsBio
  • Ra'ayinmu
    https://hausa.leadership.ng/author/raayinmu/
    Shin Nijeriya Ta Shirya Tunkarar Dawowar Annobar Ebola?
  • Ra'ayinmu
    https://hausa.leadership.ng/author/raayinmu/
    Buƙatar Samar Da Alƙibla Ta Musamman Ga Gidajen Gyaran Hali Na Ƙasar Nan
  • Ra'ayinmu
    https://hausa.leadership.ng/author/raayinmu/
    Ce-ce-ku-ce Kan Batun Biyan Bashin Naira Tiriliyan 3.3 Na Kuɗin Lantarki
  • Ra'ayinmu
    https://hausa.leadership.ng/author/raayinmu/
    Matsalar Ɓacewar Gandun Dazukan Nijeriya

MASU ALAKA

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili
Manyan Labarai

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro
Manyan Labarai

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026
Gwamnatin Zamfara Ta Shirya Tallafa Wa Mata Da Masu Ƙaramin Ƙarfi Fiye Da Miliyan Ɗaya
Manyan Labarai

Gwamnatin Zamfara Ta Shirya Tallafa Wa Mata Da Masu Ƙaramin Ƙarfi Fiye Da Miliyan Ɗaya

June 3, 2026
Next Post
Yadda Gwamnatin Tarayya Ta Yi Watsi Da Ginin Ma’aikatar Noma Da Ya Laƙume Naira Biliyan 7

Yadda Gwamnatin Tarayya Ta Yi Watsi Da Ginin Ma’aikatar Noma Da Ya Laƙume Naira Biliyan 7

Discussion about this post

LABARAI MASU NASABA

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026
Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

June 3, 2026
Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

June 3, 2026
Hada Kai Da ’Yan Awaren Yankin Taiwan Ba Zai Haifar Da Ɗa Mai Ido Ba

Hada Kai Da ’Yan Awaren Yankin Taiwan Ba Zai Haifar Da Ɗa Mai Ido Ba

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.