ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Buƙatar Magance Kisan Kiyashi Da Ƴan Bindiga Suka Yi A Kasuwar Neja

by Ra'ayinmu
5 months ago
Neja

A watan Janairun 2026 ne, wasu ƴan bindiga, suka kutsa cikin babbar kasuwar Daji, da ke a jihar Neja, inda suka yiwa mutane, sama da 40, kisan gilla.

Wannan mummunan ta’addacin dai, ya nuna a zahiri, irin yanayin lamarin ƙalubalen rashin tsaro, da ƙasar ke ci gaba da fuskanta.

Duk da yawan shelar da gwamnati ke ci gaba da yi na cewa, tana ci gaba da ɗaukar matakai, domin lalubo da mafita kan wannan matsalar, amma ana kuma, ƴan bindiga da kuma ƴan ta’adda, na ci gaba da ɗaukar rayukan alummar, da ba su ji, ba su kuma gani ba.

ADVERTISEMENT
  • AFCON 2025: Zan Taimaka Wa Uganda Ta Doke Super Eagles Duk Da Mahaifina Ɗan Nijeriya Ne – Ikpeazu
  • Kafa Kamfanin Sarrafa Gwal A Legas: Ƙungiyar Dattawan Arewa Ta Ƙalubalanci Tinubu

Lamarin ka hallaka mutane, ba gari ba sabat, kusan za a iya cewa, sai ƙara zamowa yake yi runwan dare, a ƙasar, inda hakan ke ci gaba da yin hannun riga, na iƙirarin gwamnatin, na shawo kan matsalar.

Akasarin ƴan Nijeriya dai, na da yaƙin cewa, batun ƙoƙarin na gwamnati kan shawo kan matsalar, a fatar baki ne kawai.

LABARAI MASU NASABA

Kotu Ta Ɗege Shari’ar Ganduje Da Wasu Mutum 7 Zuwa 14 Ga Oktoba 2026

Ndume Ya Bayyana Dalilin Da Ya Sa Yake Goyon Bayan Ƙudirin Kafa ‘Yansandan Jihohi

Babban abin takaicin shi, da tsakiyar rana ne, ƴan bindigar, suka kutsa cikin kasuwar, suka ƙaddamar da aika-aikar tasu, ta hanyar yin amfani da muggan makamai.

Harin na jihar Neja, ya dai kasance, tamkar a cikin film ɗin ban tsaro, inda maharani, suka ɗaure waɗanda lamarin ya rutsa da su, suka kuma yiwa aƙalla ƴan kasuwa 30, yankan Rago, suka kuma shiga cikin wasu yankuna suka buɗe wuta suka kashe wasu a yankin, tare da cinnawa wasu gidaje wuta.

Shin ya za a ce, waɗannan marasa imanin har suka kammala aikata ta’asarsu, ba tare da jami’an tsaro, sun kawo ɗauki ba?

Kazalika, shin wasu daga cikin mazuna yankin sun yi gaggawar kai rahoton haring a ofishin ƴansanda mafi kusa?

Ya ya matsayin batun tura jami’an tsaro zuwa yankin, tun bayan aukuwar harin da ƴanbinda suka kai a makarantar Papiri?

Duk da cewa, ƙasar nan, ba wai tana a cikin yanayi na yaƙi bane, amma mai ya sa, mutane ba su iya yawo salin alin a cikin ƙasar ko kuma zuwa kasuwa, amma sai sun fuskanci matsalar tsaro?

Daga cikin waɗanda maharani suka hallaka, har da yara, ba tare da sun akita wani laifi ba.

Wasu mazauna yankin sun ce, maharan, sun yiwa kasuwar ƙawanya ne biyan sun fito daga mavoyarsu da ke a jejin  Kainji National Park, inda hakan, nuna cewa, mavoyar ta su, dama can sananniya ce.

Idan har malafar ta su, a cikin jama’a take, shin me ya haɗa jami’an tsaron tarwatsa su, daga sansannin na su?

Nisan da ke daga kasuwar zuwa yankin  Papiri na ƙaramar hukumar  Agwara, inda aka sace ɗalibai sama da 200, a ranar 21 ga watan Nuwambar 2025, na makarantar St. Mary’s Catholic , bai da wata nisa.

Hakan dai, ya nuna irin gazawar gwamnati na magance ƙalubalen rashin tsaro a jihar.

Lamarin dai, na ci gaba da haifar da shakku a zukatan jama’a, duba da yadda maharan, suka kutsa cikin kasuwar suka kuma kci Karensu, babu babbaka, tare da satar kayan abinci da kaya masu tsada,

Jihar dai, ta jima tana fusknatan hare-haren ƴan bindiga, inda akasari, gwamnati kawai ke fitar da sanarwar, yin tir da duk wani hari da aka kai.

Bugu da ƙari, bayan kai harin na kasuwar Dajin shugaba Bola Tinubu, ya fitar da sanawar tin tir, da kai harin, tare da umartar jami’an tsaro da su kamo maharani da kuma kuvutar da waɗanda maharani suka sace.

Mun dai faɗa cewa, akwai buƙatar gwamnati, ta ƙara ƙarfafa magance matsalar ta rashin tsaro, a ɗaukacin faɗin ƙasar.

Idan da za tambayi ƴan Nijeriya me suka fi buƙata a tsakanin samar masu da ababen more rayuwa da tsaro, tabbas, za su ce, sun fi buƙatar a samar masu da tsaro.

Wannan Jaridar, na jajatanwa iyalai da kuma ƴan uwan waɗanda lamarin, ya rutsa da su, a harin na kasuwar, inda kuma waɗanda suka samu raunuka, muke masu fatan Allah ya ba su lafiya Ya zama wajibi, gwamatin ta tashi haiƙan domin samar da tsaro a ɗaukacin faɗin ƙasar, tun kafin lokaci ya ƙure.

Neja
Ra'ayinmu
+ postsBio
  • Ra'ayinmu
    https://hausa.leadership.ng/author/raayinmu/
    Shin Nijeriya Ta Shirya Tunkarar Dawowar Annobar Ebola?
  • Ra'ayinmu
    https://hausa.leadership.ng/author/raayinmu/
    Buƙatar Samar Da Alƙibla Ta Musamman Ga Gidajen Gyaran Hali Na Ƙasar Nan
  • Ra'ayinmu
    https://hausa.leadership.ng/author/raayinmu/
    Ce-ce-ku-ce Kan Batun Biyan Bashin Naira Tiriliyan 3.3 Na Kuɗin Lantarki
  • Ra'ayinmu
    https://hausa.leadership.ng/author/raayinmu/
    Matsalar Ɓacewar Gandun Dazukan Nijeriya

MASU ALAKA

Kotu Ta Ɗege Shari’ar Ganduje Da Wasu Mutum 7 Zuwa 14 Ga Oktoba 2026
Manyan Labarai

Kotu Ta Ɗege Shari’ar Ganduje Da Wasu Mutum 7 Zuwa 14 Ga Oktoba 2026

June 25, 2026
Ndume Ya Bayyana Dalilin Da Ya Sa Yake Goyon Bayan Ƙudirin Kafa ‘Yansandan Jihohi
Manyan Labarai

Ndume Ya Bayyana Dalilin Da Ya Sa Yake Goyon Bayan Ƙudirin Kafa ‘Yansandan Jihohi

June 25, 2026
EFCC Za Ta Gurfanar Da Shugaban Miyetti Allah Kan Zargin Almundahanar Dala Miliyan 2.53
Manyan Labarai

EFCC Za Ta Gurfanar Da Shugaban Miyetti Allah Kan Zargin Almundahanar Dala Miliyan 2.53

June 25, 2026
Next Post
Yadda Gwamnatin Tarayya Ta Yi Watsi Da Ginin Ma’aikatar Noma Da Ya Laƙume Naira Biliyan 7

Yadda Gwamnatin Tarayya Ta Yi Watsi Da Ginin Ma’aikatar Noma Da Ya Laƙume Naira Biliyan 7

LABARAI MASU NASABA

Ƙungiyar NPCF Ta Yi Barazanar Janye Goyon Bayanta Ga Tinubu

Ƙungiyar NPCF Ta Yi Barazanar Janye Goyon Bayanta Ga Tinubu

June 25, 2026
Firaministan Sin Ya Halarci Taron Tattaunawa Da Wakilan ‘Yan Kasuwa Mahalarta Dandalin Tattalin Arzikin Duniya Na DAVOS

Firaministan Sin Ya Halarci Taron Tattaunawa Da Wakilan ‘Yan Kasuwa Mahalarta Dandalin Tattalin Arzikin Duniya Na DAVOS

June 25, 2026
Sojoji Sun Kama Mai Kai Wa Ƴan Ta’adda Kayan Aiki A Zamfara

Sojoji Sun Kama Mai Kai Wa Ƴan Ta’adda Kayan Aiki A Zamfara

June 25, 2026
Kotu Ta Ɗege Shari’ar Ganduje Da Wasu Mutum 7 Zuwa 14 Ga Oktoba 2026

Kotu Ta Ɗege Shari’ar Ganduje Da Wasu Mutum 7 Zuwa 14 Ga Oktoba 2026

June 25, 2026
An Fara Gasar Tseren Dawakai Ta ‘Renewed Hope’ da Sabon Salo A Kano

An Fara Gasar Tseren Dawakai Ta ‘Renewed Hope’ da Sabon Salo A Kano

June 25, 2026
APC Ta Dage Yakin Zaben Shugaban Kasarta A Kano

An Dakatar Da Shugaban APC Na Kebbi Da Kwamishina Kan Zaɓen Cike Gurbin Zuru

June 25, 2026
Ndume Ya Bayyana Dalilin Da Ya Sa Yake Goyon Bayan Ƙudirin Kafa ‘Yansandan Jihohi

Ndume Ya Bayyana Dalilin Da Ya Sa Yake Goyon Bayan Ƙudirin Kafa ‘Yansandan Jihohi

June 25, 2026
EFCC Za Ta Gurfanar Da Shugaban Miyetti Allah Kan Zargin Almundahanar Dala Miliyan 2.53

EFCC Za Ta Gurfanar Da Shugaban Miyetti Allah Kan Zargin Almundahanar Dala Miliyan 2.53

June 25, 2026
Maroko Ta Zama Ƙasa Ta Farko Daga Afirka Da Ta Tsallaka Zuwa Zagaye Na 32 A Gasar Kofin Duniya

Maroko Ta Zama Ƙasa Ta Farko Daga Afirka Da Ta Tsallaka Zuwa Zagaye Na 32 A Gasar Kofin Duniya

June 25, 2026
Zan Ware 10bn Don Inganta Ilimin Matasa Idan Na Ci Zabe – Atiku

‘Yan Nijeriya Ba Sa Bukatar ‘Yan Jarida Su Faɗa Musu Suna Jin Yunwa — Atiku

June 25, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.