ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Saturday, July 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Buƙatar Magance Kisan Kiyashi Da Ƴan Bindiga Suka Yi A Kasuwar Neja

by Ra'ayinmu
6 months ago
Neja

A watan Janairun 2026 ne, wasu ƴan bindiga, suka kutsa cikin babbar kasuwar Daji, da ke a jihar Neja, inda suka yiwa mutane, sama da 40, kisan gilla.

Wannan mummunan ta’addacin dai, ya nuna a zahiri, irin yanayin lamarin ƙalubalen rashin tsaro, da ƙasar ke ci gaba da fuskanta.

Duk da yawan shelar da gwamnati ke ci gaba da yi na cewa, tana ci gaba da ɗaukar matakai, domin lalubo da mafita kan wannan matsalar, amma ana kuma, ƴan bindiga da kuma ƴan ta’adda, na ci gaba da ɗaukar rayukan alummar, da ba su ji, ba su kuma gani ba.

ADVERTISEMENT
  • AFCON 2025: Zan Taimaka Wa Uganda Ta Doke Super Eagles Duk Da Mahaifina Ɗan Nijeriya Ne – Ikpeazu
  • Kafa Kamfanin Sarrafa Gwal A Legas: Ƙungiyar Dattawan Arewa Ta Ƙalubalanci Tinubu

Lamarin ka hallaka mutane, ba gari ba sabat, kusan za a iya cewa, sai ƙara zamowa yake yi runwan dare, a ƙasar, inda hakan ke ci gaba da yin hannun riga, na iƙirarin gwamnatin, na shawo kan matsalar.

Akasarin ƴan Nijeriya dai, na da yaƙin cewa, batun ƙoƙarin na gwamnati kan shawo kan matsalar, a fatar baki ne kawai.

LABARAI MASU NASABA

Sojoji Sun Kamata Ƴan Bindiga 5 Da Ake Zargi Da Garkuwa Da Mutane A Yobe

Obasanjo Da Atiku Sun Sake Musayar Zafafan Kalaman Zargin Juna

Babban abin takaicin shi, da tsakiyar rana ne, ƴan bindigar, suka kutsa cikin kasuwar, suka ƙaddamar da aika-aikar tasu, ta hanyar yin amfani da muggan makamai.

Harin na jihar Neja, ya dai kasance, tamkar a cikin film ɗin ban tsaro, inda maharani, suka ɗaure waɗanda lamarin ya rutsa da su, suka kuma yiwa aƙalla ƴan kasuwa 30, yankan Rago, suka kuma shiga cikin wasu yankuna suka buɗe wuta suka kashe wasu a yankin, tare da cinnawa wasu gidaje wuta.

Shin ya za a ce, waɗannan marasa imanin har suka kammala aikata ta’asarsu, ba tare da jami’an tsaro, sun kawo ɗauki ba?

Kazalika, shin wasu daga cikin mazuna yankin sun yi gaggawar kai rahoton haring a ofishin ƴansanda mafi kusa?

Ya ya matsayin batun tura jami’an tsaro zuwa yankin, tun bayan aukuwar harin da ƴanbinda suka kai a makarantar Papiri?

Duk da cewa, ƙasar nan, ba wai tana a cikin yanayi na yaƙi bane, amma mai ya sa, mutane ba su iya yawo salin alin a cikin ƙasar ko kuma zuwa kasuwa, amma sai sun fuskanci matsalar tsaro?

Daga cikin waɗanda maharani suka hallaka, har da yara, ba tare da sun akita wani laifi ba.

Wasu mazauna yankin sun ce, maharan, sun yiwa kasuwar ƙawanya ne biyan sun fito daga mavoyarsu da ke a jejin  Kainji National Park, inda hakan, nuna cewa, mavoyar ta su, dama can sananniya ce.

Idan har malafar ta su, a cikin jama’a take, shin me ya haɗa jami’an tsaron tarwatsa su, daga sansannin na su?

Nisan da ke daga kasuwar zuwa yankin  Papiri na ƙaramar hukumar  Agwara, inda aka sace ɗalibai sama da 200, a ranar 21 ga watan Nuwambar 2025, na makarantar St. Mary’s Catholic , bai da wata nisa.

Hakan dai, ya nuna irin gazawar gwamnati na magance ƙalubalen rashin tsaro a jihar.

Lamarin dai, na ci gaba da haifar da shakku a zukatan jama’a, duba da yadda maharan, suka kutsa cikin kasuwar suka kuma kci Karensu, babu babbaka, tare da satar kayan abinci da kaya masu tsada,

Jihar dai, ta jima tana fusknatan hare-haren ƴan bindiga, inda akasari, gwamnati kawai ke fitar da sanarwar, yin tir da duk wani hari da aka kai.

Bugu da ƙari, bayan kai harin na kasuwar Dajin shugaba Bola Tinubu, ya fitar da sanawar tin tir, da kai harin, tare da umartar jami’an tsaro da su kamo maharani da kuma kuvutar da waɗanda maharani suka sace.

Mun dai faɗa cewa, akwai buƙatar gwamnati, ta ƙara ƙarfafa magance matsalar ta rashin tsaro, a ɗaukacin faɗin ƙasar.

Idan da za tambayi ƴan Nijeriya me suka fi buƙata a tsakanin samar masu da ababen more rayuwa da tsaro, tabbas, za su ce, sun fi buƙatar a samar masu da tsaro.

Wannan Jaridar, na jajatanwa iyalai da kuma ƴan uwan waɗanda lamarin, ya rutsa da su, a harin na kasuwar, inda kuma waɗanda suka samu raunuka, muke masu fatan Allah ya ba su lafiya Ya zama wajibi, gwamatin ta tashi haiƙan domin samar da tsaro a ɗaukacin faɗin ƙasar, tun kafin lokaci ya ƙure.

Neja
Ra'ayinmu
+ postsBio
  • Ra'ayinmu
    https://hausa.leadership.ng/author/raayinmu/
    Ana Ci Gaba Da Tafka Muhawara Kan Shirin Gwamnati Na Haramta Masana’atun Sarrafa Robobi
  • Ra'ayinmu
    https://hausa.leadership.ng/author/raayinmu/
    Kisan Gillar Marabar Jos: Bai Kamata Jinin Malama Ummulkhairi Ya Tafi A Banza Ba
  • Ra'ayinmu
    https://hausa.leadership.ng/author/raayinmu/
    Shin Nijeriya Ta Shirya Tunkarar Dawowar Annobar Ebola?
  • Ra'ayinmu
    https://hausa.leadership.ng/author/raayinmu/
    Buƙatar Samar Da Alƙibla Ta Musamman Ga Gidajen Gyaran Hali Na Ƙasar Nan

MASU ALAKA

Neja
Manyan Labarai

Sojoji Sun Kamata Ƴan Bindiga 5 Da Ake Zargi Da Garkuwa Da Mutane A Yobe

July 25, 2026
Neja
Manyan Labarai

Obasanjo Da Atiku Sun Sake Musayar Zafafan Kalaman Zargin Juna

July 25, 2026
Sana’ar Kilishi:Yadda Ta Bunkasa Daga Jihar Katsina Zuwa Wasu Sassan Nijeriya
Manyan Labarai

Sana’ar Kilishi:Yadda Ta Bunkasa Daga Jihar Katsina Zuwa Wasu Sassan Nijeriya

July 24, 2026
Next Post
Yadda Gwamnatin Tarayya Ta Yi Watsi Da Ginin Ma’aikatar Noma Da Ya Laƙume Naira Biliyan 7

Yadda Gwamnatin Tarayya Ta Yi Watsi Da Ginin Ma’aikatar Noma Da Ya Laƙume Naira Biliyan 7

LABARAI MASU NASABA

Neja

Sojoji Sun Kamata Ƴan Bindiga 5 Da Ake Zargi Da Garkuwa Da Mutane A Yobe

July 25, 2026
Gwamnatin Jihar Kano Za Ta Fara Aiwatar Da Shirin Inshorar Lafiya Ga Jaruman Kannywood

Gwamnatin Jihar Kano Za Ta Fara Aiwatar Da Shirin Inshorar Lafiya Ga Jaruman Kannywood

July 25, 2026
Neja

Ku Buɗe Wuta Kan Duk Wanda Kuka Gani Ɗauke Da Bindiga – IGP

July 25, 2026
Idan Aka Cire Bangaren Man Fetur Kannywood Ce Ta Fi Samar Da Aikin Yi Ga Matasa —Hamisu Iyantama

Idan Aka Cire Bangaren Man Fetur Kannywood Ce Ta Fi Samar Da Aikin Yi Ga Matasa —Hamisu Iyantama

July 25, 2026
Kogin Kumadugu Ya Yi Ambaliya Karon Farko Cikin Shekara 100 A Yobe

Jihohi 28 Da Abuja Na Fuskantar Hadarin Ambaliyar Ruwa —Rahoto

July 25, 2026
Neja

Ƴan Bindiga Sun Sace Shugaban Ƙaramar Hukumar Bungudu

July 25, 2026
Yadda Jami’an Tsaro Suka Fatattaki ’Yan Ta’adda A Wasu Jihohin Nijeriya, Sun Kama ‘Yan Kasar Pakistan Bakwai

Yadda Jami’an Tsaro Suka Fatattaki ’Yan Ta’adda A Wasu Jihohin Nijeriya, Sun Kama ‘Yan Kasar Pakistan Bakwai

July 25, 2026
Neja

Obasanjo Da Atiku Sun Sake Musayar Zafafan Kalaman Zargin Juna

July 25, 2026
Manufofin Tattalin Arzikin Gwamnatin Tinubu Sun Lalata Rayukan Al’ummar Nijeriya —ADC

Manufofin Tattalin Arzikin Gwamnatin Tinubu Sun Lalata Rayukan Al’ummar Nijeriya —ADC

July 25, 2026
An Karrama Masana Ilimin Lissafi Na Kasar Sin Da Lambobin Yabo Na Fields Medal

An Karrama Masana Ilimin Lissafi Na Kasar Sin Da Lambobin Yabo Na Fields Medal

July 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.