ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yadda Gwamnatin Tarayya Ta Yi Watsi Da Ginin Ma’aikatar Noma Da Ya Laƙume Naira Biliyan 7

by Abubakar Abba
4 months ago
Gwamnati

A shekarar 1966 ne, aka ƙirƙiro da ma’aikatar aikin noma da samar da wadataccen abinci ta tarayya, wacce kuma ta fuskanci sauye-sauyen suna da dama tare da garanbawul da gwamnatocin baya suka yi.

Sai dai, shekara 30 da ta gabata, bayan sauya wa ma’aikatar matsuguni daga Jihar Legas zuwa babban birnin tarayya Abuja, ba tava samun wata shalkwata tata ta kanta ba.

A halin yanzu dai, ma’aikatar ta kasance ne a ginin hukumar tafiyar da birnin na Abuja, wadda ta kasance tana da bene mai hawa uku kacal tare da kuma rashin samar mata da wadatattun sassan gudanar da ayyuakanta.

ADVERTISEMENT
  • Yawan Hatsin Da Kasar Sin Ta Noma Ya Kai Wani Sabon Matsayi Na Koli A 2025
  • Dalilin Manoma Na Rungumar Irin Farin Wake A Jihar Benuwe

Ma’aikatar, wadda a 2018 ƙarƙashin tsohon ministanta, Cif Audu Ogbeh, ana kiranta ne da ma’aikatar bunƙasa aikin noma da raya karkara, inda a wancan lokacin aka sayi wani gini da ke  cibiyar kasuwanci a Abuja, kan naira biliyan 7 a matsayin shalkwatar ma’aikatar, wanda ginin ya kasance mai bene hawa takwas.

shalkwatar, wanda aka saya a lokacin tsohowar shugabar ma’aikata ta tarayya, Dakta Folasade Yemi-Esan, ya haifar da ƙura da ke ƙunshe a cikin wata takardar gargaɗi da aka miƙa wa babban sakataren ma’aikatar, Dakta Mohammed Bello, wanda ya sanya ido wajen sayen ginin.

LABARAI MASU NASABA

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

An dai miƙa masa takardar gargaɗin ce, a ranar 11 ga watan Mayun 2020, wadda aka umarce shi ya yi bayani a cikin sa’o’i 72, kan batun sayen ginin a matsayin shalkwatar ma’aikatar.

Takardar gargaɗin dai, ta tuhumi babban sakataren kan sanya ido wajen sayen ginin, ba tare da abin ƙa’ida ba.

Sai dai, bayan sayen shalkwatar, an gano cewa; gini ne da ba a riga an kammala shi ba.

Amma, a martanin da Dakta Bello ya bayar kan batun sayen shalkwatar ya sanar da cewa, an gabatar da buƙatar sayen ginin ne, wanda kuma tsohon ministan Cif Ogbeh, ya gabatar wa da wani kamfani, inda kuma ya gabatar da batun a zaman da majalisar zartawa ta yi, kan buƙatar amincewa da sayen ginin.

Tun bayan tsawon waɗannan shekaru, ginin ya kasance a matsayin wanda aka yi watsi da shi, wanda kuma aka mayar da shi wajen ajiye motocin ma’aikatar.

Sake Amincewar Gwamnatin Tarayya Na Sayen Wani Ginin:

A watan Afirilun 2023, majalisar zartarwa ta sake amincewa da yi wa shalkwatar ma’aikatar kwaskwarima, duk a matsugunin na ma’aikatar.

Tsohon ministan da ke sanya ido kan tafiyar da ma’aikatar, Mohammad Abubakar, a wata hira da manema labarai, ya shaida musu cewa; majalisar zartarwar ta amince da kashe naira biliyan 6, domin fara yi wa sabuwar shalkwatar ma’aikatar kwaskwarima.

A cewar Abubakar, sabuwar shalkwatar, za ta kasance tana da bene mai hawa 10, wadda aka sanya wa suna ‘Agriculture House.’

Abubakar ya ƙara da cewa, mahukuntan birnin na Abuja, sun samar da wani gini a yankin ‘Cadastral’, wanda ke da faɗin hekta guda 1.84.

Ya ci gaba da cewa, dalilin da ya sanya aka yi watsi da ginin na kimanin naira biliyan 7 shi ne, an gano cewa; wajen ya yi kaɗan, sannan kuma ba zai ɗauki sauran sassa na ma’aikatan ba.

Ya ƙara da cewa,  an tsara za a sayar da ita, domin a zuba kuɗin a cikn kasafin kuɗi na tsakanin  2022 zuwa  2023, a kan naira biliyan 6, domin a fara gudanar da sabon aikin shalkwwatar.

An Keve Sama Da Naira Biliyan 5 A Kasafin Kuɗi Na 2026:

A cikin kasafin kuɗi na 2026, an keve naira biliyan 5.67, domin gyaran shalkwatar ma’aikatar.

Wannan adadin, ya kai jimillar naira biliyan 11.67, da aka amince, domin sayen sabuwar shalkwatar ma’aikatar.

Shekaru takwas bayan yunƙuri na farko, har zuwa yanzu, ma’aiaktar ba ta kai matakin shalkwata ba.

Ma’aikatar Ta Kashe Naira Biliyan 2026:

Duk da naira tiriliyan 58.18 da gwamnatin tarayya ta zuba a cikin kasafin kuɗi na 2026, ma’aiktar da kuma hukumomin aikin noma da ke ƙarƙashinta, sun samu jimillar naira tirliyan 1.44 ne kacal.

Idan aka yi duba kan jeren ayyuakan da kuma irin ɗimbin kuɗaɗen da aka keve wa ma’aikatar, a cikin kasafin kuɗi na 2026, ƙididdiga ta nuna cewa, yarjejeniyar da aka ƙulla ta ƙasa da ƙasa da ke cikin bashin shiri na musamman na bunƙasa aikin noma a shiyyoyi shida na ƙasar, wato SAPZ, za su laƙume kimanin naira biliyan 126.02.

Gwamnati
Abubakar Abba
+ postsBio
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Abin Da Ya Sa Gwamnatin Taraba Ta Sayo Sabbin Kayan Noma Na Zamani
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Kamfanin Simintin Ɗangote Ya Ƙaddamar Da Shirye-shiryen Tallafa Wa Mazauna Jihar Biniwe
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Dalilin Gwamnatin Kwara Na Zuba Dala Biliyan 70 A Fannin Kiwon Dabbobi
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Cibiyar IAR Ta Gudanar Da Ayyukan Bincike 140 Kan Sabbin Amfanin Gona 

MASU ALAKA

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili
Manyan Labarai

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro
Manyan Labarai

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026
Gwamnatin Zamfara Ta Shirya Tallafa Wa Mata Da Masu Ƙaramin Ƙarfi Fiye Da Miliyan Ɗaya
Manyan Labarai

Gwamnatin Zamfara Ta Shirya Tallafa Wa Mata Da Masu Ƙaramin Ƙarfi Fiye Da Miliyan Ɗaya

June 3, 2026
Next Post
Sojoji Sun Hallaka Kwamandojin Boko Haram 2, Sun Kama Wasu 8 A Borno

Sojoji Sun Hallaka Kwamandojin Boko Haram 2, Sun Kama Wasu 8 A Borno

Discussion about this post

LABARAI MASU NASABA

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026
Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

June 3, 2026
Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

June 3, 2026
Hada Kai Da ’Yan Awaren Yankin Taiwan Ba Zai Haifar Da Ɗa Mai Ido Ba

Hada Kai Da ’Yan Awaren Yankin Taiwan Ba Zai Haifar Da Ɗa Mai Ido Ba

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.