ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, September 10, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yadda Gwamnatin Tarayya Ta Yi Watsi Da Ginin Ma’aikatar Noma Da Ya Laƙume Naira Biliyan 7

by Abubakar Abba
8 months ago
Gwamnati

A shekarar 1966 ne, aka ƙirƙiro da ma’aikatar aikin noma da samar da wadataccen abinci ta tarayya, wacce kuma ta fuskanci sauye-sauyen suna da dama tare da garanbawul da gwamnatocin baya suka yi.

Sai dai, shekara 30 da ta gabata, bayan sauya wa ma’aikatar matsuguni daga Jihar Legas zuwa babban birnin tarayya Abuja, ba tava samun wata shalkwata tata ta kanta ba.

A halin yanzu dai, ma’aikatar ta kasance ne a ginin hukumar tafiyar da birnin na Abuja, wadda ta kasance tana da bene mai hawa uku kacal tare da kuma rashin samar mata da wadatattun sassan gudanar da ayyuakanta.

ADVERTISEMENT
  • Yawan Hatsin Da Kasar Sin Ta Noma Ya Kai Wani Sabon Matsayi Na Koli A 2025
  • Dalilin Manoma Na Rungumar Irin Farin Wake A Jihar Benuwe

Ma’aikatar, wadda a 2018 ƙarƙashin tsohon ministanta, Cif Audu Ogbeh, ana kiranta ne da ma’aikatar bunƙasa aikin noma da raya karkara, inda a wancan lokacin aka sayi wani gini da ke  cibiyar kasuwanci a Abuja, kan naira biliyan 7 a matsayin shalkwatar ma’aikatar, wanda ginin ya kasance mai bene hawa takwas.

shalkwatar, wanda aka saya a lokacin tsohowar shugabar ma’aikata ta tarayya, Dakta Folasade Yemi-Esan, ya haifar da ƙura da ke ƙunshe a cikin wata takardar gargaɗi da aka miƙa wa babban sakataren ma’aikatar, Dakta Mohammed Bello, wanda ya sanya ido wajen sayen ginin.

LABARAI MASU NASABA

Ku Daure Ku Sake Zaɓar Mijina A 2027 – Remi Tinubu

’Yansanda Sun Cafke Matar Da Ta Kwara Wa Maƙociyarta Tafasasshen Ruwan Zafi A Abuja

An dai miƙa masa takardar gargaɗin ce, a ranar 11 ga watan Mayun 2020, wadda aka umarce shi ya yi bayani a cikin sa’o’i 72, kan batun sayen ginin a matsayin shalkwatar ma’aikatar.

Takardar gargaɗin dai, ta tuhumi babban sakataren kan sanya ido wajen sayen ginin, ba tare da abin ƙa’ida ba.

Sai dai, bayan sayen shalkwatar, an gano cewa; gini ne da ba a riga an kammala shi ba.

Amma, a martanin da Dakta Bello ya bayar kan batun sayen shalkwatar ya sanar da cewa, an gabatar da buƙatar sayen ginin ne, wanda kuma tsohon ministan Cif Ogbeh, ya gabatar wa da wani kamfani, inda kuma ya gabatar da batun a zaman da majalisar zartawa ta yi, kan buƙatar amincewa da sayen ginin.

Tun bayan tsawon waɗannan shekaru, ginin ya kasance a matsayin wanda aka yi watsi da shi, wanda kuma aka mayar da shi wajen ajiye motocin ma’aikatar.

Sake Amincewar Gwamnatin Tarayya Na Sayen Wani Ginin:

A watan Afirilun 2023, majalisar zartarwa ta sake amincewa da yi wa shalkwatar ma’aikatar kwaskwarima, duk a matsugunin na ma’aikatar.

Tsohon ministan da ke sanya ido kan tafiyar da ma’aikatar, Mohammad Abubakar, a wata hira da manema labarai, ya shaida musu cewa; majalisar zartarwar ta amince da kashe naira biliyan 6, domin fara yi wa sabuwar shalkwatar ma’aikatar kwaskwarima.

A cewar Abubakar, sabuwar shalkwatar, za ta kasance tana da bene mai hawa 10, wadda aka sanya wa suna ‘Agriculture House.’

Abubakar ya ƙara da cewa, mahukuntan birnin na Abuja, sun samar da wani gini a yankin ‘Cadastral’, wanda ke da faɗin hekta guda 1.84.

Ya ci gaba da cewa, dalilin da ya sanya aka yi watsi da ginin na kimanin naira biliyan 7 shi ne, an gano cewa; wajen ya yi kaɗan, sannan kuma ba zai ɗauki sauran sassa na ma’aikatan ba.

Ya ƙara da cewa,  an tsara za a sayar da ita, domin a zuba kuɗin a cikn kasafin kuɗi na tsakanin  2022 zuwa  2023, a kan naira biliyan 6, domin a fara gudanar da sabon aikin shalkwwatar.

An Keve Sama Da Naira Biliyan 5 A Kasafin Kuɗi Na 2026:

A cikin kasafin kuɗi na 2026, an keve naira biliyan 5.67, domin gyaran shalkwatar ma’aikatar.

Wannan adadin, ya kai jimillar naira biliyan 11.67, da aka amince, domin sayen sabuwar shalkwatar ma’aikatar.

Shekaru takwas bayan yunƙuri na farko, har zuwa yanzu, ma’aiaktar ba ta kai matakin shalkwata ba.

Ma’aikatar Ta Kashe Naira Biliyan 2026:

Duk da naira tiriliyan 58.18 da gwamnatin tarayya ta zuba a cikin kasafin kuɗi na 2026, ma’aiktar da kuma hukumomin aikin noma da ke ƙarƙashinta, sun samu jimillar naira tirliyan 1.44 ne kacal.

Idan aka yi duba kan jeren ayyuakan da kuma irin ɗimbin kuɗaɗen da aka keve wa ma’aikatar, a cikin kasafin kuɗi na 2026, ƙididdiga ta nuna cewa, yarjejeniyar da aka ƙulla ta ƙasa da ƙasa da ke cikin bashin shiri na musamman na bunƙasa aikin noma a shiyyoyi shida na ƙasar, wato SAPZ, za su laƙume kimanin naira biliyan 126.02.

Gwamnati
Abubakar Abba
+ postsBio
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Tun Ina Karama Marigayi Tumbuleke Ke Sa Ni Dariya —Hannatu Musawa
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    NPA Ta Bayyana Cewa Kirkiro Da Sabuwar Hukumar NPERA Ba Zai Zame Mata Tarnaki Ba
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Yadda Bikin Girke-girke Ya Karfafa Alaka Tsakanin Musulmai Da Kiristoci A Kaduna
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Nazari Kan Wasu Dalilan Da Ke Haddasa Sabanin Abotakar Jarumi Ko Jaruma A Kannywood

MASU ALAKA

Ku Daure Ku Sake Zaɓar Mijina A 2027 – Remi Tinubu
Manyan Labarai

Ku Daure Ku Sake Zaɓar Mijina A 2027 – Remi Tinubu

September 9, 2026
’Yansanda Sun Cafke Matar Da Ta Kwara Wa Maƙociyarta Tafasasshen Ruwan Zafi A Abuja
Manyan Labarai

’Yansanda Sun Cafke Matar Da Ta Kwara Wa Maƙociyarta Tafasasshen Ruwan Zafi A Abuja

September 9, 2026
’Yan Takarar ADC A Arewa Maso Yamma Sun Yi Alƙawarin Biyan N110,000 A Matsayin Mafi Ƙarancin Albashi
Manyan Labarai

’Yan Takarar ADC A Arewa Maso Yamma Sun Yi Alƙawarin Biyan N110,000 A Matsayin Mafi Ƙarancin Albashi

September 9, 2026
Next Post
Sojoji Sun Hallaka Kwamandojin Boko Haram 2, Sun Kama Wasu 8 A Borno

Sojoji Sun Hallaka Kwamandojin Boko Haram 2, Sun Kama Wasu 8 A Borno

LABARAI MASU NASABA

Sin Na Fatan Amurka Za Ta Dakatar Da Furta Karairayi Da Nufin Bata Mata Suna

Sin Na Fatan Amurka Za Ta Dakatar Da Furta Karairayi Da Nufin Bata Mata Suna

September 9, 2026
An Kashe Shahararren Mai Sharhin Siyasar Kano, Ibrahim Dan Shagamu

An Kashe Shahararren Mai Sharhin Siyasar Kano, Ibrahim Dan Shagamu

September 9, 2026
Sin Ba Ta Taba Janyewa Wata Kasa Tsani Ba

Sin Ba Ta Taba Janyewa Wata Kasa Tsani Ba

September 9, 2026
Xi Ya Aike Da Gaisuwa Albarkacin Ranar Malamai Yana Mai Kira Da A Samar Da Matasa Masu Hazaka Domin Kara Farfado Da Kasa

Xi Ya Aike Da Gaisuwa Albarkacin Ranar Malamai Yana Mai Kira Da A Samar Da Matasa Masu Hazaka Domin Kara Farfado Da Kasa

September 9, 2026
Ku Daure Ku Sake Zaɓar Mijina A 2027 – Remi Tinubu

Ku Daure Ku Sake Zaɓar Mijina A 2027 – Remi Tinubu

September 9, 2026
Renon Matasa A Kan Kyakkyawar Turba Ginshiki Ne Na Gina KasaBy

Renon Matasa A Kan Kyakkyawar Turba Ginshiki Ne Na Gina KasaBy

September 9, 2026
Bikin CIFTIS Zai Ingiza Bude Kofa A Kasar Sin

Bikin CIFTIS Zai Ingiza Bude Kofa A Kasar Sin

September 9, 2026
“Ajin Tashar Sararin Samaniya Na Hong Kong Da Macau” Ya Kara Wa Matasa Sha’awar Kimiyya Da Karfafa Kishin Kasa

“Ajin Tashar Sararin Samaniya Na Hong Kong Da Macau” Ya Kara Wa Matasa Sha’awar Kimiyya Da Karfafa Kishin Kasa

September 9, 2026
’Yansanda Sun Cafke Matar Da Ta Kwara Wa Maƙociyarta Tafasasshen Ruwan Zafi A Abuja

’Yansanda Sun Cafke Matar Da Ta Kwara Wa Maƙociyarta Tafasasshen Ruwan Zafi A Abuja

September 9, 2026
Taron Kolin Urumqi Ya Mayar Da Hankali Kan Kwarewar Shugabanci A Xinjiang Da Muhimmancinta Ga Duniya

Taron Kolin Urumqi Ya Mayar Da Hankali Kan Kwarewar Shugabanci A Xinjiang Da Muhimmancinta Ga Duniya

September 9, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.