Shekaru 80 da suka gabata, kotun hukunta laifukan yakin duniya na II ya gudanar da jerin shari’o’i kan laifuffukan da Japan ta aikata yayin yakin, inda ta dora laifi kan rundunar sojan Japan bisa abubuwan da ta aikata. Sai dai abun takaicin shi ne, maimakon Japan ta girmama tarihi, sai ta gaggauta sassauta tsare-tsaren da suka jibanci ayyukan soji, da kalubalantar tarihin da kuma takala.
Wani nazarin da kafar CGTN ta gudanar ta intanet ya nuna cewa, kaso 81.8 na masu bayar da amsa sun yi imanin cewa, Japan na kara kalubalantar tarihi ta hanyar farfado da karfin soji, lamarin da ke barazana ga zaman lafiya da kwanciyar hankalin yankin, wanda kuma ke bukatar kasa da kasa su sa ido sosai a kai.
Bisa la’akari da zaman kotu har sau 818, da mutane masu shaida 419 da suka bayyana a kotu da kayayyaki 4,336 da aka gabatar a matsayin shaidu da shafuka 48,000 na tanade-tanaden shari’ar, kotun hukunta laifuffukan yakin duniya na II ta gabatar da munanan laifuffukan da sojojin Japan suka aikata. Bisa sakamakon nazarin CGTN, kaso 64.1 na masu bayar da amsa na ganin cewa, a matsayin hukumar koli ta tabbatar da adalci a duniya, shari’o’in kotun sun bankado tare da samun Japan da aikata laifuffuka.
Haka kuma, kaso 81.6 na masu bayar da amsa sun amince cewa, shari’o’in sun tabbatar da yanayi mai muni na abubuwan da Japan ta aika a lokacin yakin. (Fa’iza Mustapha)















Discussion about this post