ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Friday, June 5, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Cikar Nijeriya Shekara 62: Matsalar Tsaro Ta Inganta A Mulkin Buhari – Lai Mohammed

by Sadiq
4 years ago
Matsalar Tsaro

Ministan yada labarai da al’adu, Lai Mohammed, ya ce rashin tsaro a Nijeriya bai yi munin shekarar 2015 lokacin da Shugaba Muhammadu Buhari ya hau mulki.

A cewar kamfanin dillacin labarai (NAN), Mohammed ya bayyana haka ne a ranar Alhamis, a wajen watalacca ta jama’a, wadda wani bangare ne na ayyukan bikin cikar Nijeriya shekaru 62 da samun ‘yancin kai.

  • ‘Yan Takarar Shugabancin Nijeriya Sun Sanya Hannu Kan Yarjejeniyar Zaman Lafiya
  • NIS Reshen Jihar Bayelsa Ta Yi Shirin Tunkarar Zaɓen 2023

Kalaman ministan na zuwa ne a daidai lokacin da wasu ‘yan bindiga suka kai hare-hare a sassan kasar, wanda ya kai ga yin garkuwa da mutane da kashe-kashe da kuma lalata dukiyoyi.

ADVERTISEMENT

Mohammed ya ce gwamnatin Buhari ta iya sauya labarin rashin tsaro, inda ya kara da cewa jihohin da a baya ba a isa zuwansu ba yanzu abun ya zama tarihi.

“Lokacin da gwamnatin Buhari ta hau kan karagar mulki, galibin yankunan arewa maso gabas ba sa iya shiguwa saboda ayyukan ‘yan ta’addan Boko Haram, wadanda suka mamaye yankin,” in ji shi.

LABARAI MASU NASABA

Mulkin Tinubu A Shekara 3:Ina Aka Fito? Ina Aka Dosa?

Har Yanzu Akwai Sauran Rina A Kaba Game Da Makomar Yara A Nijeriya

“An rufe makarantu, kasuwanci. Sun rufe hanyoyin shiga yankin. A yau al’amura sun canja da sosai.”

Ya kara da cewa a matsayin kasa daya, karfin sojojin Nijeriya yana karuwa kuma zai ci gaba da samun karfin guiwa.

Ya kuma bukaci ‘yan Nijeriya musamman masu fada aji da su hada kai wajen kare kasar, yana mai cewa kowa na da rawar da zai taka domin dawo da zaman lafiya a kasar.

Ministan ya kara da cewa, “Shugaban kasa ya yi imanin cewa manyan mutane za su bunkasa abubuwa da kuma sanya su a cikin al’umma wajen samar da hadin kan kasa da kuma ba da gudummawa ga al’amuran kasa.”

Sai dai wasu na ganin wannan kalamai na ministan ba sh zauna musu duba da ganin yadda wasu yankuna musamman na arewancin Nijeriya ke ci gaba da fuskantar munanan hare-haren ‘yan bindiga.

MASU ALAKA

Babu Wani Shiri Na Kwaso ‘Yan Nijeriya Daga Falasdin Ko Isra’ila –Gwamnatin Tarayya
Manyan Labarai

Mulkin Tinubu A Shekara 3:Ina Aka Fito? Ina Aka Dosa?

June 5, 2026
Har Yanzu Akwai Sauran Rina A Kaba Game Da Makomar Yara A Nijeriya
Manyan Labarai

Har Yanzu Akwai Sauran Rina A Kaba Game Da Makomar Yara A Nijeriya

June 5, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi
Manyan Labarai

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

June 4, 2026
Next Post
Tsarin Kawance Na “BRICS +” Ya Samar Da Sabon Dandalin Hadin Gwiwa Tsakanin Kasashe Masu Tasowa

Tsarin Kawance Na “BRICS +” Ya Samar Da Sabon Dandalin Hadin Gwiwa Tsakanin Kasashe Masu Tasowa

LABARAI MASU NASABA

Ƴansanda Sun Daƙile Yunƙurin Garkuwa Da Wasu Ma’aurata A Abuja

Ƴansanda Sun Daƙile Yunƙurin Garkuwa Da Wasu Ma’aurata A Abuja

June 5, 2026
Kotu Ta Yi Gwanjon Kaddarorin Sani Sha’aban Bisa Taurin Bashi

Kotu Ta Yi Gwanjon Kaddarorin Sani Sha’aban Bisa Taurin Bashi

June 5, 2026
An Yi Suka Kan Mayar Da Nijeriya Jujin Jibge Kwantaina Da Ake Shigowa Da Su

An Yi Suka Kan Mayar Da Nijeriya Jujin Jibge Kwantaina Da Ake Shigowa Da Su

June 5, 2026
Dorewar Tattalin Arzikin Duniya Ya Dogara Ne Kan Ayyukan Tashoshin Jiragen Ruwa Na Afrika Ta Tsakiya, Cewar Dantsoho

Dorewar Tattalin Arzikin Duniya Ya Dogara Ne Kan Ayyukan Tashoshin Jiragen Ruwa Na Afrika Ta Tsakiya, Cewar Dantsoho

June 5, 2026
Sabon Rikicin Manoma Da Makiyaya yayi Ajalin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

Sabon Rikicin Manoma Da Makiyaya yayi Ajalin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

June 5, 2026
Babu Wani Shiri Na Kwaso ‘Yan Nijeriya Daga Falasdin Ko Isra’ila –Gwamnatin Tarayya

Mulkin Tinubu A Shekara 3:Ina Aka Fito? Ina Aka Dosa?

June 5, 2026
Hajji 2026: Mahajjata 1,905 Sun Dawo Nijeriya Daga Saudiyya

Hajji 2026: Mahajjata 1,905 Sun Dawo Nijeriya Daga Saudiyya

June 5, 2026
Har Yanzu Akwai Sauran Rina A Kaba Game Da Makomar Yara A Nijeriya

Har Yanzu Akwai Sauran Rina A Kaba Game Da Makomar Yara A Nijeriya

June 5, 2026
Matatar Dangote Ta Ƙara Yawan Man Da Take Tacewa Zuwa Ganga 700,000

Matatar Dangote Ta Ƙara Yawan Man Da Take Tacewa Zuwa Ganga 700,000

June 4, 2026
Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

June 4, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.