Kocin kungiyar kwallon kafa ta Arsenal Mikel Arteta ya bayyana cewa har yanzu Arsenal na da yakinin cewa za ta iya lashe gasar Premier duk da cewa yanzu haka Manchester City ce ke matsayi na daya akan teburin gasar bayan samun nasarar da tayi akan Burnley a tsakiyar mako, kungiyar Arsenal wadda Mikel Arteta ke jagoranta ta rasa matsayinta a teburin bayan City ta doke Burnley da ci 1-0 a ranar Laraba.
Arsenal ta hada maki daya da City hakazalika kwallayensu daya da Manchester City amma kuma City tafi samun nasara a manyan wasanni, Gunners din za ta iya sake samun matsayi na farko ta hanyar guje wa shan kashi a hannun Newcastle a filin wasa na Emirates ranar Asabar.
Arsenal na fatan lashe kofin karo na farko cikin shekaru 22, kofin karshe da kungiyar ta lashe shi ne wanda ta lashe a shekarar 2004, rashin nasara da suka yi a hannun Bournemouth da Manchester City yayi sanadiyar barar da tazarar maki 9 dake tsakaninsu, duk da haka Arteta ya dage cewa Arsenal ba ta rasa karfin gwiwa ba kuma tana tsammanin za su farfado daga rashin nasara da suka yi da ci 2-1 a hannun City ranar Lahadi da ta gabata lokacin da za su karbi bakuncin Newcastle a karshen mako.















Discussion about this post