Shugaban ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya ce matakin cire tallafin man fetur da gwamnatinsa ta ɗauka ya ceci Nijeriya daga rushewar tattalin arziƙi, tare da shimfida tubalin farfaɗowar tattalin arziƙin ƙasar. Ya bayyana hakan ne yayin da ya karɓi bakuncin gwamnoni da suka kai masa ziyara domin taya shi murnar Sallah da cikar gwamnatinsa shekaru uku a mulki.
Tinubu ya amince cewa cire tallafin ya jawo wahala ga jama’a, amma ya ce hakan ya zama dole domin daƙile durƙushewar karyewar darajar Naira. A cewarsa, kuɗaɗen da ake kashewa kan tallafin mai tsawon shekaru sun hana muhimman bangarori samun jarin da suke buƙata, yana mai cewa tattalin arziƙin ƙasar ya fara nuna alamun farfadowa, yayin da noma da ayyukan raya ƙasa ke samun ci gaba.
Mataimakin shugaban kasa, Kashim Shettima, ya yabawa shugaban ƙasa bisa jajircewarsa wajen aiwatar da sauye-sauyen tattalin arziƙi duk da ƙalubalen da suka biyo baya. Shi ma shugaban ƙungiyar gwamnonin na ƙasa kuma gwamnan jihar Kwara, AbdulRahman AbdulRazaq, ya ce cire tallafin ya ƙara kudaden shiga na jihohi tare da ba su damar biyan albashi da gudanar da ayyukan raya kasa.
A nasa ɓangaren, shugaban gwamnonin APC kuma gwamnan jihar Imo, Hope Uzodinma, ya ce gwamnoni sun bai wa Tinubu maki ɗari bisa ɗari kan ayyukan gwamnatinsa, yana mai yabawa shugabancinsa inda ya ce ya taimaka wajen dawo da Nijeriya daga barazanar durƙushewa zuwa yanayin daidaito.















Discussion about this post