Amfani da ruɓaɓɓen Tumatari abin sai ƙaruwa yake yi a faɗin tarayyar Nijeriya duk da yake masana harkar lafiya sun jan kunnen mutane domin kuwa yin hakan na da babbar matsalar da za ta shafi lafiya.
Gaba ɗayan ƙasar Nijeriya, masu sayen abinci daga wajen masu dafawa da kuma masu sayar da kayan abincin, da gangan ne suke sayen Tumatarin da ya lalace, wanda ko waɗanda aka sayar da su a farashi mai rahusa.
Jaridar ƙarshen mako ta Daily Trust ta gano cewar da gangan ne waɗansu masu sayen kayan miya lokacin da dare ya fara yi, inda za su saya da arha daga wurin masu sayarwa waɗanda su dama sun ƙosa su sayar da arha, saboda suna sayar da Tumatarin da zafi ya sa a fara lalacewa.
Tumatarin da ya fara lalacewa na ɗauke shi ka shi biyu: na farko waɗanda suka fara lalacewa kaɗan da kuma na biyu waɗanda sun daɗe eda lalacewa. Masu saye sun fi son wanda ya fi lalacewar domin ya fi atrha, musamman ma idan mutum zai saya da yawa.
Masu sayar da abinci na bakin titi da kuma ƙananan masu gidan sayar abinci sun fi son waɗancan nau’in Tumatarin da ya lalace.
Wakilanmu a sassa daban daban na Nijeriya sun bankaɗo yadda aka maida hankali akan sayen Tumatarin da ya fara lalacewa suka kuma tattauna da masana,waɗanda su kuma suka yi jan kunne dangane da irin matsalar lafiyar da za a iya samu idan aka ci gaba da yin hakan.
A jihar Legas Wakilinmu ya bada rahoton yadda ake irin wannan mugun abu na sayen Tumatarin da ya fara lalacewa a kasuwar mil sha biyu, da ta kasance babbar kasuwa ta sayar da kayan abinci ta kuma kasance daga can ne ake rarraba kayan abincin a faɗin Nijeriya da kuma wasu sassa na yammacin Afirka.
Makon da ya gabata ne, aka saki wani bidiyo inda aka kama wata mata a kafar sadarwa ta zamani,da ake zargin tana ƙoƙarin ta niƙa ko markaɗa Barkono ko Tattasan da ke da tsutsotsi a cikin kasuwar.
Faruwar ko aukuwar hakan ce ta sa Gwamnatin Jihar Legas ta fitar da wani bayani na jan kunnen al’umma da su daina amfani da Tumatarin da ya lalace kamar irin yadda wasu abubuwa suka fara rayuwa a kan shi, wanda yin hakan na iya sa a kamu da cututtukan da suke da alaƙa da mu’amala da nau’oin Tumatarin.
Yadda ake samu ƙaruwar lalacewar Tumatari
A Legas da wasu sassan kudu maso gabas ,Tumataren da suka lalace ko Barkonon da Atarugu da suka ruɓe ana kiransu “esa.”
Kamar dai kayan da su kan iya lalacewa bayan sun ɗauki wani lokaci, Tumatari da Barkono suna fuskantar matsalar asara lokacin da suka nuna, ɗaya daga matsalolin da ke damu kayan amfanin gona kamar yadda kamar yadda hukumar (OTACCWA)ta bayyana, irin asarar da ake yi ta kai ta Naira Tiriliyan 3.5 kowace shekara.
Ba tare da wurin da za a ajiye su mai sanyi ba kamar cikin Firig kamar yadda ya dace, kaya masu saurin lalacewa kamar su kayan marmari da kuma ganye suna lalacewa da sauri, kai har ma ya kasance amfani da su zai iya smar da cuta, su kuma rasa fa’aidar amfanin da za su iya yi.
Binciken da Wakilinmu ya yi ya gano wasu Tumatari da Barkono idan har suka fara samun matsala lokacin da aka girbe su, tun daga wancan lokacin ne suke fara lalacewa a lmarin da akan kira su “esa” a wasu wuraren da Yarabawa suke da suka haɗa da Legas.
A shekarun baya,irin su kayan da suka lalace ana yarda su ne, ko kuma a a sayarwa d gida da yafi kowa talauci. Sai dai kuma saboda irin matsin halin da ake ciki sanadiyar llacewa tattalin arziki yana sam mutane da yawa suna amincewa da “esa.”
Bayan waɗanda su lamarin nasu kan yadda ake amfani da shi a wasu gidaje, an kama masu abincin sayarwa suna amfani da Tumatari ko kuma biya an kama hana su ne amfani ne da Tumatarin da ya ɓaci wani wari ya ke yi, ayi miya da su, lamarin da daga ƙarƙshe zai iya cutar al’umma.
Tsadar Tumatari Maikyau Wata abu ce
Wasu masu sayen Tumatarin da masu abincin sayarwa sun yi magana da Jaridar Trust ta ƙarshen mako sun ɗora alhakin yadda farashin Tumatari da Barkono suke ta ƙaruwa saboda yadda suka maida hankalinsu wajen sayaen ruɓaɓɓen Tumatarin.
An samu bayanin cewa Buhun Tumatari mai kilo 50, wanda ake sayar da shi tsakanin Naira 35,000 zuwa Naira 40,000 watan da ya gabata, yanzu ana sayar da shi tsakanin Naira 115,000 zuwa Naira 125,000.
A wasu wurare ne, ƙaaramin kwandon Tumatari ana sayar da shi Naira 2,000 a watan da ya gabata yanzu ana sayar da shi Naira 6,000.
Waɗanda suka tattauna da Wakilanmu sun ce yawancin masu abinci yanzu suna sayen ruɓaɓɓen Tumatarin ne saboda kuɗin da suke dasu ba za su iya saiyen Tumatarin mai kyau ba yanzu suna sayen Tumataren da suka lalace.
“Mutane suna sayen shi hakan Muna ganinsu a Kasuwa. Mutanen da suke sana’ar sayar da abinci suna amfani da shi. Amma ni bani amfani da shi,” cewar wadda take abincin sayarwa, Mrs Desola Adelabi.
Mrs. Adelabi ta ƙara jaddada cewa: “Lokacin da Tumatari da Barkono suka kasance da tsada, shi ma farashin esa yana ƙaruwa. Yana zuwa a nau’oi daban- daban.”
Sai dai kuma duk da hakan ta nuna rashin jin daɗinta,saboda lamarin na iya shafar lafiya musamman idan aaka yi amfani da Tumatarin da ya lalace wajen yin miya lokacin girkin abinci.
“Esa bai da kyau idan ana buƙatar kula da lafiya ne.Saboda baya bada ɗanɗano mai armashi masu sayen abinci ba za su sake dawo ba idan sun gane an yi amfani ne da kayan miyar da suka ruɓe wajen shirya abincin.
“Idan ka zo nan ka ci jar miya kana jin bata da ɗanɗano za ka sake dawowa kamar dai yadda ta yi tambaya’’.















Discussion about this post