• Leadership Hausa
Saturday, January 28, 2023
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Sana’a Sa’a
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Sana’a Sa’a
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result
Home Daga Birnin Sin

Da Abokin Daka Ake Shan Gari…

by CMG Hausa
6 months ago
in Daga Birnin Sin
0
Da Abokin Daka Ake Shan Gari…

Shaidu da abubuwa na zahiri na kara tabbatar da cewa, Sin da Afirka sun zama abin da Malam Bahaushe ke cewa, ’yan uwa rabin jiki”.

Duk lokacin da bangaren Sin ya ga abin da zai shafi moriyar kasashen Afirka da ma na kasashe masu tasowa, ya kan yi kokarin ankarar da duniya bukatar kare muradunsu tare da mara musu baya, wajen ganin an cimma burin da ake fata.

  • Ma’aikatar Harkokin Wajen Sin: Ra’ayin ‘Yan Afirka Kan Hadin-Gwiwar Sin Da Afirka Ya Fi Muhimmanci

Batu na baya-bayan shi ne yadda zaunannen wakilin kasar Sin a MDD, kuma shugaban kwamitin sulhu na MDD na wannan wata Zhang Jun, ya yi kira ga kasashen duniya, da su goyi bayan Afirka wajen inganta karfinsu na tabbatar da zaman lafiya mai dorewa a cikin kasashensu. Zaman lafiya aka ce ya fi zama dan sarki, kuma sai da zaman lafiya, za a samu duk wani ci gaba da ake fata.

Zhang ya bayyana yayin taron bude muhawarar kwamitin sulhu da kasar Sin ta kira, mai taken “zaman lafiya da tsaro a nahiyar Afirka: samar da karfin tabbatar da zaman lafiya mai dorewa.” Tallafin da kasar Sin din ta gabatar sun kasance a fannoni guda 4 ne, wadanda suka hada da karfafa sanin makamar aiki a fannin tafiyar da harkokin gwamnatoci, da inganta kwazon sassan hukumomin tsaro, da bunkasa ikon samar da ci gaba mai dorewa, da renon kwararru.

Jami’in na kasar Sin ya ce, bisa la’akari da irin kwarewar da kasar Sin ta samu wajen samun bunkasuwa, da gogewa daga hadin gwiwar dake tsakanin Sin da kasashen Afirka, da kuma darussan tarihi daga fadin duniya, kasar Sin ta yi imanin cewa, idan har ana son taimakawa Afirka wajen samun kwanciyar hankali na dogon lokaci, wajibi ne a kara zuba jari mai dorewa, da yin tunani mai zurfi, da kuma gina harsashi mai karfi ga Afirka, don kara karfin hanyar samun ci gaba da ta zaba da kanta, da inganta juriyarta kan abubuwan da za su kawo mata cikas daga waje. Sanin kowa ne cewa, sai an zubar da ruwa a kasa kafin a taka damshi.

Labarai Masu Nasaba

Masani: Sin Za Ta Iya Taka Muhimmiyar Rawa Wajen Bunkasa Ci Gaban Duniya A Shekarar 2023

Kasar Sin: An Yi Tafiye-tafiye Sama Da Miliyan 300 A Lokacin Hutun Bikin Bazara 

Saboda muhimmancin zaman lafiya da kwanciyar hankali ga ci gaban kowa ce kasa a fadin duniya, masu sharhi na kara jaddada cewa, bai kamata a rika gindaya wani sharadi na siyasa da ya shafi samar da taimako ba, kuma bai kamata a rika tsoma baki a harkokin cikin gidan kasashen Afirka ba, ko maye gurbin ayyukan da kananan hukumomi suka saba gudanarwa.

Ba abu ne boyayye ba, baya ga kayayyakin more rayuwa da kasashen Afirka suka amfana da su karkashin hadin gwiwar sassan biyu, wato Sin da Afirka.

Daga lokaci zuwa lokaci ko dai a taruka ko dandalolin kasa da kasa, bangaren Sin kan yi kokarin kare muradun kasashe masu tasowa baki daya. Abin da ke kara tabbatar da sahihancin alakar sassan biyu.

Previous Post

Gwamnatin Kaduna Ta Karyata Jita-jitar Malalar ‘Yan Ta’adda Tsakanin Kaduna Da Zariya

Next Post

Dole Ne A Hukunta Kasar Amurka Wadda Ta Fi Keta Hakkin Dan Adam A Duniya

Related

Masani: Sin Za Ta Iya Taka Muhimmiyar Rawa Wajen Bunkasa Ci Gaban Duniya A Shekarar 2023
Daga Birnin Sin

Masani: Sin Za Ta Iya Taka Muhimmiyar Rawa Wajen Bunkasa Ci Gaban Duniya A Shekarar 2023

39 mins ago
Kasar Sin: An Yi Tafiye-tafiye Sama Da Miliyan 300 A Lokacin Hutun Bikin Bazara 
Daga Birnin Sin

Kasar Sin: An Yi Tafiye-tafiye Sama Da Miliyan 300 A Lokacin Hutun Bikin Bazara 

2 hours ago
An Gudanar Da Bikin Baje Koli Na Bikin Bazara Na Kantunan Littattafan Kasar Sin A Ketare Karo Na 13 
Daga Birnin Sin

An Gudanar Da Bikin Baje Koli Na Bikin Bazara Na Kantunan Littattafan Kasar Sin A Ketare Karo Na 13 

22 hours ago
Alex Ampaabeng:Matakan Yaki Da COVID-19 Na Sin Za Su Taimaka Wajen Dawo Da Tsarin Samar Da Hajoji A Duniya
Daga Birnin Sin

Alex Ampaabeng:Matakan Yaki Da COVID-19 Na Sin Za Su Taimaka Wajen Dawo Da Tsarin Samar Da Hajoji A Duniya

23 hours ago
Kasar Sin Ta Jaddada Muhimmancin Dagewa Nuna Fifiko Ga Ci Gaban Gina Zaman Lafiya
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Ta Jaddada Muhimmancin Dagewa Nuna Fifiko Ga Ci Gaban Gina Zaman Lafiya

24 hours ago
Rahoton MDD: Tattalin Arzikin Kasar Sin Zai Jawo Bunkasuwar Tattalin Arzikin Shiyyar A Shekarar 2023
Daga Birnin Sin

Rahoton MDD: Tattalin Arzikin Kasar Sin Zai Jawo Bunkasuwar Tattalin Arzikin Shiyyar A Shekarar 2023

1 day ago
Next Post
Dole Ne A Hukunta Kasar Amurka Wadda Ta Fi Keta Hakkin Dan Adam A Duniya

Dole Ne A Hukunta Kasar Amurka Wadda Ta Fi Keta Hakkin Dan Adam A Duniya

LABARAI MASU NASABA

Masani: Sin Za Ta Iya Taka Muhimmiyar Rawa Wajen Bunkasa Ci Gaban Duniya A Shekarar 2023

Masani: Sin Za Ta Iya Taka Muhimmiyar Rawa Wajen Bunkasa Ci Gaban Duniya A Shekarar 2023

January 28, 2023
Matsalolin Da APC Ta Jefa ‘Yan Nijeriya Ya Kamata Su Zama Darasi -Jarman Makarfi

Matsalolin Da APC Ta Jefa ‘Yan Nijeriya Ya Kamata Su Zama Darasi -Jarman Makarfi

January 28, 2023
Dole A Hada Karfi Wajen Dakile Bazuwar Makamai A Afirka –Buhari

Ba Don A Wahalar Da Talaka AKa Sauya Kudin Nijeriya Ba —Buhari 

January 28, 2023
Kasar Sin: An Yi Tafiye-tafiye Sama Da Miliyan 300 A Lokacin Hutun Bikin Bazara 

Kasar Sin: An Yi Tafiye-tafiye Sama Da Miliyan 300 A Lokacin Hutun Bikin Bazara 

January 28, 2023
Jan Yara A Jiki Ba Tare Da Duka Ko Zagi Ba Ne Sirrin Nasarar Koyarwa—Saratu Magaji Jahun

Jan Yara A Jiki Ba Tare Da Duka Ko Zagi Ba Ne Sirrin Nasarar Koyarwa—Saratu Magaji Jahun

January 28, 2023
Babu Barazanar Kai Hari A Kano – ‘Yansanda

DPO Ya Yanke Jiki Ya Fadi, Ya Rasu A Jigawa

January 28, 2023
Wasu Daga Cikin Manhajojin Da Ke Bata Wayar Android

Wasu Daga Cikin Manhajojin Da Ke Bata Wayar Android

January 28, 2023
Da Gaske Arteta Ya Kawo Gyara A Arsenal?

Da Gaske Arteta Ya Kawo Gyara A Arsenal?

January 28, 2023
An Yi Gwanjon Rigar Da Pele Ya Buga Kofin Duniya Na Karshe Da Ita

An Yi Gwanjon Rigar Da Pele Ya Buga Kofin Duniya Na Karshe Da Ita

January 28, 2023
Yarfe Da Kazafi Tsakanin Manyan ‘Yan Takarar Shugabancin Nijeriya: Duk Gautar Ja Ce?

Yarfe Da Kazafi Tsakanin Manyan ‘Yan Takarar Shugabancin Nijeriya: Duk Gautar Ja Ce?

January 28, 2023
ADVERTISEMENT
Advertise with us

© 2022 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2022 Leadership Media Group - All Right Reserved.