ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Friday, June 26, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Da Abokin Daka Ake Shan Gari…

by CMG Hausa
4 years ago
Sin

Shaidu da abubuwa na zahiri na kara tabbatar da cewa, Sin da Afirka sun zama abin da Malam Bahaushe ke cewa, ’yan uwa rabin jiki”.

Duk lokacin da bangaren Sin ya ga abin da zai shafi moriyar kasashen Afirka da ma na kasashe masu tasowa, ya kan yi kokarin ankarar da duniya bukatar kare muradunsu tare da mara musu baya, wajen ganin an cimma burin da ake fata.

  • Ma’aikatar Harkokin Wajen Sin: Ra’ayin ‘Yan Afirka Kan Hadin-Gwiwar Sin Da Afirka Ya Fi Muhimmanci

Batu na baya-bayan shi ne yadda zaunannen wakilin kasar Sin a MDD, kuma shugaban kwamitin sulhu na MDD na wannan wata Zhang Jun, ya yi kira ga kasashen duniya, da su goyi bayan Afirka wajen inganta karfinsu na tabbatar da zaman lafiya mai dorewa a cikin kasashensu. Zaman lafiya aka ce ya fi zama dan sarki, kuma sai da zaman lafiya, za a samu duk wani ci gaba da ake fata.

ADVERTISEMENT

Zhang ya bayyana yayin taron bude muhawarar kwamitin sulhu da kasar Sin ta kira, mai taken “zaman lafiya da tsaro a nahiyar Afirka: samar da karfin tabbatar da zaman lafiya mai dorewa.” Tallafin da kasar Sin din ta gabatar sun kasance a fannoni guda 4 ne, wadanda suka hada da karfafa sanin makamar aiki a fannin tafiyar da harkokin gwamnatoci, da inganta kwazon sassan hukumomin tsaro, da bunkasa ikon samar da ci gaba mai dorewa, da renon kwararru.

Jami’in na kasar Sin ya ce, bisa la’akari da irin kwarewar da kasar Sin ta samu wajen samun bunkasuwa, da gogewa daga hadin gwiwar dake tsakanin Sin da kasashen Afirka, da kuma darussan tarihi daga fadin duniya, kasar Sin ta yi imanin cewa, idan har ana son taimakawa Afirka wajen samun kwanciyar hankali na dogon lokaci, wajibi ne a kara zuba jari mai dorewa, da yin tunani mai zurfi, da kuma gina harsashi mai karfi ga Afirka, don kara karfin hanyar samun ci gaba da ta zaba da kanta, da inganta juriyarta kan abubuwan da za su kawo mata cikas daga waje. Sanin kowa ne cewa, sai an zubar da ruwa a kasa kafin a taka damshi.

LABARAI MASU NASABA

Sin Ta Habaka Karfin Soja Ne Don Kare Ikon Mallakar Kasa Da Muradun Ci Gaba

Sin Ta Yi Allah Wadai Da Amfani Da Haraji Ba Bisa Ka’ida Ba Ta Fakewa Da Zargin “Kwadagon Tilas”

Saboda muhimmancin zaman lafiya da kwanciyar hankali ga ci gaban kowa ce kasa a fadin duniya, masu sharhi na kara jaddada cewa, bai kamata a rika gindaya wani sharadi na siyasa da ya shafi samar da taimako ba, kuma bai kamata a rika tsoma baki a harkokin cikin gidan kasashen Afirka ba, ko maye gurbin ayyukan da kananan hukumomi suka saba gudanarwa.

Ba abu ne boyayye ba, baya ga kayayyakin more rayuwa da kasashen Afirka suka amfana da su karkashin hadin gwiwar sassan biyu, wato Sin da Afirka.

Daga lokaci zuwa lokaci ko dai a taruka ko dandalolin kasa da kasa, bangaren Sin kan yi kokarin kare muradun kasashe masu tasowa baki daya. Abin da ke kara tabbatar da sahihancin alakar sassan biyu.

Sin
CMG Hausa
+ postsBio
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Shugabannin Kasashen Duniya Sun Yi Wa Sin Fatan Alheri A Sabuwar Shekara
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    San Francisco sabon mafarin hadin gwiwar Sin da Amurka ne
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Xi Ya Halarci Kwaya-Kwaryan Taron Shugabannin Mambobin APEC
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Shugaban Kasar Sin Ya Gabatar Da Rubutaccen Jawabi Ga Taron Jagororin Masana’antu Da Kasuwanci Na APEC

MASU ALAKA

Sin Ta Habaka Karfin Soja Ne Don Kare Ikon Mallakar Kasa Da Muradun Ci Gaba
Daga Birnin Sin

Sin Ta Habaka Karfin Soja Ne Don Kare Ikon Mallakar Kasa Da Muradun Ci Gaba

June 26, 2026
Sin Ta Yi Allah Wadai Da Amfani Da Haraji Ba Bisa Ka’ida Ba Ta Fakewa Da Zargin “Kwadagon Tilas”
Daga Birnin Sin

Sin Ta Yi Allah Wadai Da Amfani Da Haraji Ba Bisa Ka’ida Ba Ta Fakewa Da Zargin “Kwadagon Tilas”

June 26, 2026
Xi Ya Mika Jaje Kan Mummunar Girgizar Kasar Venezuela
Daga Birnin Sin

Xi Ya Mika Jaje Kan Mummunar Girgizar Kasar Venezuela

June 26, 2026
Next Post
Dole Ne A Hukunta Kasar Amurka Wadda Ta Fi Keta Hakkin Dan Adam A Duniya

Dole Ne A Hukunta Kasar Amurka Wadda Ta Fi Keta Hakkin Dan Adam A Duniya

LABARAI MASU NASABA

Sin Ta Habaka Karfin Soja Ne Don Kare Ikon Mallakar Kasa Da Muradun Ci Gaba

Sin Ta Habaka Karfin Soja Ne Don Kare Ikon Mallakar Kasa Da Muradun Ci Gaba

June 26, 2026
Sin

Dalilin Gwamnatin Tarayya Na Fara Aikin Gina Mayankar Zamani A Garin Jos

June 26, 2026
Sin Ta Yi Allah Wadai Da Amfani Da Haraji Ba Bisa Ka’ida Ba Ta Fakewa Da Zargin “Kwadagon Tilas”

Sin Ta Yi Allah Wadai Da Amfani Da Haraji Ba Bisa Ka’ida Ba Ta Fakewa Da Zargin “Kwadagon Tilas”

June 26, 2026
NDC Ta Ce Za Ta Ɗaukaka Ƙara Kan Hukuncin Soke Rajistarta

NDC Ta Ce Za Ta Ɗaukaka Ƙara Kan Hukuncin Soke Rajistarta

June 26, 2026
An Fitar da Jadawalin Wasannin Zagayen Farko Na Gasar Carabao Cup ta 2026/2027

An Fitar da Jadawalin Wasannin Zagayen Farko Na Gasar Carabao Cup ta 2026/2027

June 26, 2026
Katsina: Kotu Ta Yanke Wa Hauwa’u Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya Kan Taimaka Wa ’Yan Bindiga

Kotu Ba Ta Da Hujjar Umartar INEC Ta Soke Rajistar Jam’iyyu —Uban Doman Lafiya

June 26, 2026
Xi Ya Mika Jaje Kan Mummunar Girgizar Kasar Venezuela

Xi Ya Mika Jaje Kan Mummunar Girgizar Kasar Venezuela

June 26, 2026
Gwamnatin Tarayya, Bankin Duniya Da Cibiyar IITA Za Su Bunkasa Noma Ta Fasahar Zamani

Bankin Duniya Ya Ɗora Tashoshin Apapa Da Tincan Kan Sikelin Maki Na 20 A Duniya

June 26, 2026
sikila

Buƙatar Mayar Da Hankali Wajen Kawo Ƙarshen Ciwon Sikila A Nijeriya

June 26, 2026
Sin Ta Bankado Laifukan Miyagun Kwayoyi 12,000 A Watanni Biyar Na Farkon Bana

Sin Ta Bankado Laifukan Miyagun Kwayoyi 12,000 A Watanni Biyar Na Farkon Bana

June 26, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.