ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Da Dumi-Dumi: Doyin Okupe Ya Yi Murabus Daga Daraktan Yakin Zaben Peter Obi

by Khalid Idris Doya
4 years ago
Doyin Okupe

Darakta-janar na kwamitin yakin zaben dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar Labour (LPPCO), Dakta Doyin Okupe, ya ajiye mukaminsa na daraktan yakin zaben. 

 

Okupe a wata babbar wasika mai dauke da kwanan wata 20 ga watan Disamban 2022 da ya aike da ita kai tsaye ga dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar, Peter Obi, ya ce, ya dauki wannan matakin ne lura da cewa a kashin kansa yana neman hanyoyin samun adalci ta hanyar shari’a d kokarin wanke sunansa ta hanyar shari’a, sannan da cewar kada a dalilinshi a samu karkatar da hankali kan alkawarin da ya yi na yin aiki tukuru a matsayin daraktan yakin zabe ya samu tangarda.

ADVERTISEMENT
  • Tsare Okupe Ba Zai Hana Ni Zama Shugaban Kasa A 2023 Ba – Peter Obi 

Ya ce, idan aka nada wani sabon darakta yakin zaben hakan zai bada dama a ci gaba da tafiyar da harkokin yakin zaben ba tare da wani hujumi ko damuwa ba.

 

LABARAI MASU NASABA

PRP Ta Musanta Zargin Cewa Kwankwaso Ya Sayi Fom 69 Domin Kwace Jam’iyyar

Jam’iyyar APC Ta Tafka Asarar Mabiya A Gombe, Sun Bi Pantami PDP

Jaridar LEADERSHIP ta labarto cewa a ranar Litinin ne watan babbar kotun tarayya da ke zamanta a Abuja ta samu Dakta Doyin Okupe da laifin karbar sama da naira miliyan 200 daga hannun tsohon mai bai wa shugaban kasa shawarori kan harkar tsaro (NSA), Kanal Sambo Dasuki (Mai ritaya) kan hakan ne ta masa daurin shekara biyu a gidan yari

 

Wasikar da ya aike na cewa, “Idan za ku iya tunawa dai a jiya na muka bayani kan kokarin da nake yi wajen neman adalci da kokarin wanke sunana ta hanyar shari’a. Ba na son ya zama a sanadin ni kadai a samu karkatar da hankali daga yakin neman zabenka.

 

“Kan hakan na sauka daga mukamina da fatan nada sabon darakta Janar na yakin neman zaben zai cigaba da gudanar da harkokin ba tare da wani hujumi ba,” a cewar Akupe.

 

Ya sha alwashin cewa zai cigaba da kasancewa tare da Peter Obi har zuwa ga samun nasarar zaben 2023, ya ce zai cigaba da kasancewa a tare da shi dari bisa dari.

 

Sannan Okupe ya wallafa ya shafinsa na Tuwita cewa, ya ajiye mukaminsa amma zai cigaba da kasancewa da Peter Obi dari bisa dari har zuwa lokacin da Allah zai ba su nasara a zaben 2023.

 

Idan za ku iya tunawa dai ya ke yanke hukuncin a ranar Litinin, Mai Shari’a Ijeoma Ojukwu, ya ce, Okupe wanda shi ne ake kara na farko a karar da hukumar yaki da cin hanci da rashawa EFCC ta shigar kan karya dokar amfani da kudade ta hanyar zargin babakere da dukiyar kasa.

 

Ya samu wannan hukuncin ne kan zarge-zarge guda 34 ko zabin biyan tara na N500,000.

 

Sannan kotun ta kuma sake yanke masa hukuncin zaman shekara biyu a gidan yari kan tuhume-tuhume 35 zuwa 59 ko zabin biyan tara na N500,000.

Doyin Okupe
Khalid Idris Doya
+ postsBio
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Ɗan Majalisar Dokokin Bauchi, Hon. Wanzam, Ya Rasu
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Tsohon Mataimakin Gwamnan Bauchi, Audu Sule Katagum Ya Rasu
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Kotu Ta Umarci DSS Ta Mutunta Umarninta Kan Shari’ar Filin Firo Na Bauchi
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Ana Zargin Jami’in Kwastam Da Kashe Kansa A Bauchi Saboda Damuwa

MASU ALAKA

2023: Gwarazan Jam’iyyu A Karon Battar Zaben Shugaban Kasa
Siyasa

PRP Ta Musanta Zargin Cewa Kwankwaso Ya Sayi Fom 69 Domin Kwace Jam’iyyar

June 22, 2026
Jam’iyyar APC Ta Tafka Asarar Mabiya A Gombe, Sun Bi Pantami PDP
Siyasa

Jam’iyyar APC Ta Tafka Asarar Mabiya A Gombe, Sun Bi Pantami PDP

June 22, 2026
ADC Ta Sake Tabbatar Da Ibrahim Khalil A Matsayin Ɗan Takarar Gwamnan Kano Na 2027
Siyasa

ADC Ta Sake Tabbatar Da Ibrahim Khalil A Matsayin Ɗan Takarar Gwamnan Kano Na 2027

June 21, 2026
Next Post
Shin Kasar Amurka Za Ta Iya Cika Alkawarinta?

Shin Kasar Amurka Za Ta Iya Cika Alkawarinta?

LABARAI MASU NASABA

Maroko Ta Zama Ƙasa Ta Farko Daga Afirka Da Ta Tsallaka Zuwa Zagaye Na 32 A Gasar Kofin Duniya

Maroko Ta Zama Ƙasa Ta Farko Daga Afirka Da Ta Tsallaka Zuwa Zagaye Na 32 A Gasar Kofin Duniya

June 25, 2026
Zan Ware 10bn Don Inganta Ilimin Matasa Idan Na Ci Zabe – Atiku

‘Yan Nijeriya Ba Sa Bukatar ‘Yan Jarida Su Faɗa Musu Suna Jin Yunwa’ — Atiku

June 25, 2026
Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026
Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.