ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, July 16, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Da Dumi-Dumi: Doyin Okupe Ya Yi Murabus Daga Daraktan Yakin Zaben Peter Obi

by Khalid Idris Doya
4 years ago
Doyin Okupe

Darakta-janar na kwamitin yakin zaben dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar Labour (LPPCO), Dakta Doyin Okupe, ya ajiye mukaminsa na daraktan yakin zaben. 

 

Okupe a wata babbar wasika mai dauke da kwanan wata 20 ga watan Disamban 2022 da ya aike da ita kai tsaye ga dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar, Peter Obi, ya ce, ya dauki wannan matakin ne lura da cewa a kashin kansa yana neman hanyoyin samun adalci ta hanyar shari’a d kokarin wanke sunansa ta hanyar shari’a, sannan da cewar kada a dalilinshi a samu karkatar da hankali kan alkawarin da ya yi na yin aiki tukuru a matsayin daraktan yakin zabe ya samu tangarda.

ADVERTISEMENT
  • Tsare Okupe Ba Zai Hana Ni Zama Shugaban Kasa A 2023 Ba – Peter Obi 

Ya ce, idan aka nada wani sabon darakta yakin zaben hakan zai bada dama a ci gaba da tafiyar da harkokin yakin zaben ba tare da wani hujumi ko damuwa ba.

 

LABARAI MASU NASABA

Ganduje Ya Buƙaci A Yi Siyasar Aƙida Domin Inganta Dimokuraɗiyya A Nijeriya

Gwamna Yusuf Ya Bai Wa Masu Kula Da Akwatinan Zaɓe Na APC Filaye 1,540 Da Tallafin Miliyan 100

Jaridar LEADERSHIP ta labarto cewa a ranar Litinin ne watan babbar kotun tarayya da ke zamanta a Abuja ta samu Dakta Doyin Okupe da laifin karbar sama da naira miliyan 200 daga hannun tsohon mai bai wa shugaban kasa shawarori kan harkar tsaro (NSA), Kanal Sambo Dasuki (Mai ritaya) kan hakan ne ta masa daurin shekara biyu a gidan yari

 

Wasikar da ya aike na cewa, “Idan za ku iya tunawa dai a jiya na muka bayani kan kokarin da nake yi wajen neman adalci da kokarin wanke sunana ta hanyar shari’a. Ba na son ya zama a sanadin ni kadai a samu karkatar da hankali daga yakin neman zabenka.

 

“Kan hakan na sauka daga mukamina da fatan nada sabon darakta Janar na yakin neman zaben zai cigaba da gudanar da harkokin ba tare da wani hujumi ba,” a cewar Akupe.

 

Ya sha alwashin cewa zai cigaba da kasancewa tare da Peter Obi har zuwa ga samun nasarar zaben 2023, ya ce zai cigaba da kasancewa a tare da shi dari bisa dari.

 

Sannan Okupe ya wallafa ya shafinsa na Tuwita cewa, ya ajiye mukaminsa amma zai cigaba da kasancewa da Peter Obi dari bisa dari har zuwa lokacin da Allah zai ba su nasara a zaben 2023.

 

Idan za ku iya tunawa dai ya ke yanke hukuncin a ranar Litinin, Mai Shari’a Ijeoma Ojukwu, ya ce, Okupe wanda shi ne ake kara na farko a karar da hukumar yaki da cin hanci da rashawa EFCC ta shigar kan karya dokar amfani da kudade ta hanyar zargin babakere da dukiyar kasa.

 

Ya samu wannan hukuncin ne kan zarge-zarge guda 34 ko zabin biyan tara na N500,000.

 

Sannan kotun ta kuma sake yanke masa hukuncin zaman shekara biyu a gidan yari kan tuhume-tuhume 35 zuwa 59 ko zabin biyan tara na N500,000.

Doyin Okupe
Khalid Idris Doya
+ postsBio
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    ATBU Ta Janye Filin Ginin Masallaci Da Ta Bai wa TIMSAN, Ta Amince Kowa Ya Yi Addininsa Yadda Ya Fahimta
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Ɗan Majalisar Dokokin Bauchi, Hon. Wanzam, Ya Rasu
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Tsohon Mataimakin Gwamnan Bauchi, Audu Sule Katagum Ya Rasu
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Kotu Ta Umarci DSS Ta Mutunta Umarninta Kan Shari’ar Filin Firo Na Bauchi

MASU ALAKA

Tinubu Yana Zuba Kyawawan Ayyuka A Nijeriya – Ganduje
Manyan Labarai

Ganduje Ya Buƙaci A Yi Siyasar Aƙida Domin Inganta Dimokuraɗiyya A Nijeriya

July 16, 2026
Gwamna Yusuf Ya Bai Wa Masu Kula Da Akwatinan Zaɓe Na APC Filaye 1,540 Da Tallafin Miliyan 100
Siyasa

Gwamna Yusuf Ya Bai Wa Masu Kula Da Akwatinan Zaɓe Na APC Filaye 1,540 Da Tallafin Miliyan 100

July 15, 2026
‘Yan Ƙasar Turkiyya Sun Nuna Jarumta Da Kare Dimokuraɗiyya Mafi Girma A Tarihi – Erdoğan
Manyan Labarai

‘Yan Ƙasar Turkiyya Sun Nuna Jarumta Da Kare Dimokuraɗiyya Mafi Girma A Tarihi – Erdoğan

July 15, 2026
Next Post
Shin Kasar Amurka Za Ta Iya Cika Alkawarinta?

Shin Kasar Amurka Za Ta Iya Cika Alkawarinta?

LABARAI MASU NASABA

Saliba Zai Yi Jinyar Watanni 5 Bayan Raunin Da Ya Samu A Bayansa

Saliba Zai Yi Jinyar Watanni 5 Bayan Raunin Da Ya Samu A Bayansa

July 16, 2026
Kotu Ta Yanke Wa Wani Hukuncin Ɗaurin Shekara 7 Kan Tallan Wiwi A Kafafen Sada Zumunta

Kotu Ta Yanke Wa Wani Hukuncin Ɗaurin Shekara 7 Kan Tallan Wiwi A Kafafen Sada Zumunta

July 16, 2026
Tinubu Yana Zuba Kyawawan Ayyuka A Nijeriya – Ganduje

Ganduje Ya Buƙaci A Yi Siyasar Aƙida Domin Inganta Dimokuraɗiyya A Nijeriya

July 16, 2026
Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

July 15, 2026
Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

July 15, 2026
Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

July 15, 2026
Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

July 15, 2026
Kevin Kelly: AI Na Iya Taimakawa Wajen Cimma Burin “Koyar Da Dalibai Da Kwazonsu”

Kevin Kelly: AI Na Iya Taimakawa Wajen Cimma Burin “Koyar Da Dalibai Da Kwazonsu”

July 15, 2026
Gwamna Yusuf Ya Bai Wa Masu Kula Da Akwatinan Zaɓe Na APC Filaye 1,540 Da Tallafin Miliyan 100

Gwamna Yusuf Ya Bai Wa Masu Kula Da Akwatinan Zaɓe Na APC Filaye 1,540 Da Tallafin Miliyan 100

July 15, 2026
Sabbin Ministoci

Rashin Tsaro: Majalisar Dattawa Ta Bukaci A Tura Ƙarin Sojoji da ’Yansanda Zuwa Benuwe

July 15, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.