ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Friday, June 5, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Da Dumi-Dumi: Doyin Okupe Ya Yi Murabus Daga Daraktan Yakin Zaben Peter Obi

by Khalid Idris Doya
3 years ago
Doyin Okupe

Darakta-janar na kwamitin yakin zaben dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar Labour (LPPCO), Dakta Doyin Okupe, ya ajiye mukaminsa na daraktan yakin zaben. 

 

Okupe a wata babbar wasika mai dauke da kwanan wata 20 ga watan Disamban 2022 da ya aike da ita kai tsaye ga dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar, Peter Obi, ya ce, ya dauki wannan matakin ne lura da cewa a kashin kansa yana neman hanyoyin samun adalci ta hanyar shari’a d kokarin wanke sunansa ta hanyar shari’a, sannan da cewar kada a dalilinshi a samu karkatar da hankali kan alkawarin da ya yi na yin aiki tukuru a matsayin daraktan yakin zabe ya samu tangarda.

ADVERTISEMENT
  • Tsare Okupe Ba Zai Hana Ni Zama Shugaban Kasa A 2023 Ba – Peter Obi 

Ya ce, idan aka nada wani sabon darakta yakin zaben hakan zai bada dama a ci gaba da tafiyar da harkokin yakin zaben ba tare da wani hujumi ko damuwa ba.

 

LABARAI MASU NASABA

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

‘Yan Majalisar Wakilai 6 Daga Oyo Sun Fice Daga PDP Zuwa APM

Jaridar LEADERSHIP ta labarto cewa a ranar Litinin ne watan babbar kotun tarayya da ke zamanta a Abuja ta samu Dakta Doyin Okupe da laifin karbar sama da naira miliyan 200 daga hannun tsohon mai bai wa shugaban kasa shawarori kan harkar tsaro (NSA), Kanal Sambo Dasuki (Mai ritaya) kan hakan ne ta masa daurin shekara biyu a gidan yari

 

Wasikar da ya aike na cewa, “Idan za ku iya tunawa dai a jiya na muka bayani kan kokarin da nake yi wajen neman adalci da kokarin wanke sunana ta hanyar shari’a. Ba na son ya zama a sanadin ni kadai a samu karkatar da hankali daga yakin neman zabenka.

 

“Kan hakan na sauka daga mukamina da fatan nada sabon darakta Janar na yakin neman zaben zai cigaba da gudanar da harkokin ba tare da wani hujumi ba,” a cewar Akupe.

 

Ya sha alwashin cewa zai cigaba da kasancewa tare da Peter Obi har zuwa ga samun nasarar zaben 2023, ya ce zai cigaba da kasancewa a tare da shi dari bisa dari.

 

Sannan Okupe ya wallafa ya shafinsa na Tuwita cewa, ya ajiye mukaminsa amma zai cigaba da kasancewa da Peter Obi dari bisa dari har zuwa lokacin da Allah zai ba su nasara a zaben 2023.

 

Idan za ku iya tunawa dai ya ke yanke hukuncin a ranar Litinin, Mai Shari’a Ijeoma Ojukwu, ya ce, Okupe wanda shi ne ake kara na farko a karar da hukumar yaki da cin hanci da rashawa EFCC ta shigar kan karya dokar amfani da kudade ta hanyar zargin babakere da dukiyar kasa.

 

Ya samu wannan hukuncin ne kan zarge-zarge guda 34 ko zabin biyan tara na N500,000.

 

Sannan kotun ta kuma sake yanke masa hukuncin zaman shekara biyu a gidan yari kan tuhume-tuhume 35 zuwa 59 ko zabin biyan tara na N500,000.

Doyin Okupe
Khalid Idris Doya
+ postsBio
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Zaɓen Fidda Gwani Na Gwamna: Ba Za Mu Lamunci Kaƙaba Mana Ɗan Takara A Bauchi Ba – Mambobin APC
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Sanata Buba Ya Janye Daga Takarar Fidda Gwani Ta Gwamnan APC A Bauchi, Ya Zargi Cewa ‘Ɗauki Ɗaura Ake Yi Ba Zaɓe Ba”

MASU ALAKA

Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe
Siyasa

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
‘Yan Majalisar Wakilai 6 Daga Oyo Sun Fice Daga PDP Zuwa APM
Siyasa

‘Yan Majalisar Wakilai 6 Daga Oyo Sun Fice Daga PDP Zuwa APM

June 3, 2026
Gwamnatina Za Ta Mayar Da Hankali Kan Buƙatun Al’ummar Nasarawa – Wadada
Siyasa

Gwamnatina Za Ta Mayar Da Hankali Kan Buƙatun Al’ummar Nasarawa – Wadada

June 1, 2026
Next Post
Shin Kasar Amurka Za Ta Iya Cika Alkawarinta?

Shin Kasar Amurka Za Ta Iya Cika Alkawarinta?

LABARAI MASU NASABA

Matatar Dangote Ta Ƙara Yawan Man Da Take Tacewa Zuwa Ganga 700,000

Matatar Dangote Ta Ƙara Yawan Man Da Take Tacewa Zuwa Ganga 700,000

June 4, 2026
Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

June 4, 2026
Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

June 4, 2026
Mun Kaɗu Matuƙa Kan Labarin Mutuwar ‘Yan Mauludi A Hanyar Saminaka – Gwamnan Kaduna

Gwamna Sani Ya Kashe Sama Da Naira Biliyan Ɗaya Kan Tallafin Ɗalibai A Kaduna – Kwamishina

June 4, 2026
Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

June 4, 2026
Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

June 4, 2026
Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

June 4, 2026
Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

June 4, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.