ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Saturday, September 12, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Da Dumi-Dumi: Doyin Okupe Ya Yi Murabus Daga Daraktan Yakin Zaben Peter Obi

by Khalid Idris Doya
4 years ago
Doyin Okupe

Darakta-janar na kwamitin yakin zaben dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar Labour (LPPCO), Dakta Doyin Okupe, ya ajiye mukaminsa na daraktan yakin zaben. 

 

Okupe a wata babbar wasika mai dauke da kwanan wata 20 ga watan Disamban 2022 da ya aike da ita kai tsaye ga dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar, Peter Obi, ya ce, ya dauki wannan matakin ne lura da cewa a kashin kansa yana neman hanyoyin samun adalci ta hanyar shari’a d kokarin wanke sunansa ta hanyar shari’a, sannan da cewar kada a dalilinshi a samu karkatar da hankali kan alkawarin da ya yi na yin aiki tukuru a matsayin daraktan yakin zabe ya samu tangarda.

ADVERTISEMENT
  • Tsare Okupe Ba Zai Hana Ni Zama Shugaban Kasa A 2023 Ba – Peter Obi 

Ya ce, idan aka nada wani sabon darakta yakin zaben hakan zai bada dama a ci gaba da tafiyar da harkokin yakin zaben ba tare da wani hujumi ko damuwa ba.

 

LABARAI MASU NASABA

Ku Daure Ku Sake Zaɓar Mijina A 2027 – Remi Tinubu

Rashin Mulki Ke Firgita Atiku – Kakakin APC Na Kaduna

Jaridar LEADERSHIP ta labarto cewa a ranar Litinin ne watan babbar kotun tarayya da ke zamanta a Abuja ta samu Dakta Doyin Okupe da laifin karbar sama da naira miliyan 200 daga hannun tsohon mai bai wa shugaban kasa shawarori kan harkar tsaro (NSA), Kanal Sambo Dasuki (Mai ritaya) kan hakan ne ta masa daurin shekara biyu a gidan yari

 

Wasikar da ya aike na cewa, “Idan za ku iya tunawa dai a jiya na muka bayani kan kokarin da nake yi wajen neman adalci da kokarin wanke sunana ta hanyar shari’a. Ba na son ya zama a sanadin ni kadai a samu karkatar da hankali daga yakin neman zabenka.

 

“Kan hakan na sauka daga mukamina da fatan nada sabon darakta Janar na yakin neman zaben zai cigaba da gudanar da harkokin ba tare da wani hujumi ba,” a cewar Akupe.

 

Ya sha alwashin cewa zai cigaba da kasancewa tare da Peter Obi har zuwa ga samun nasarar zaben 2023, ya ce zai cigaba da kasancewa a tare da shi dari bisa dari.

 

Sannan Okupe ya wallafa ya shafinsa na Tuwita cewa, ya ajiye mukaminsa amma zai cigaba da kasancewa da Peter Obi dari bisa dari har zuwa lokacin da Allah zai ba su nasara a zaben 2023.

 

Idan za ku iya tunawa dai ya ke yanke hukuncin a ranar Litinin, Mai Shari’a Ijeoma Ojukwu, ya ce, Okupe wanda shi ne ake kara na farko a karar da hukumar yaki da cin hanci da rashawa EFCC ta shigar kan karya dokar amfani da kudade ta hanyar zargin babakere da dukiyar kasa.

 

Ya samu wannan hukuncin ne kan zarge-zarge guda 34 ko zabin biyan tara na N500,000.

 

Sannan kotun ta kuma sake yanke masa hukuncin zaman shekara biyu a gidan yari kan tuhume-tuhume 35 zuwa 59 ko zabin biyan tara na N500,000.

Doyin Okupe
Khalid Idris Doya
+ postsBio
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    PDP Ta Musanta Mara Wa APM Baya A Bauchi
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Yaro Ya Harbe Kansa Har Lahira Bayan Mafarauci Ya Yi Sakaci Da Bindigarsa A Bauchi
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    An Kama Mutane 5 Da Sassan Jikin Ɗan’Adam Za Su Yi Tsafi A Bauchi
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Tsohon Mai Neman Takarar Gwamnan Bauchi, Bala Jibrin, Ya Fice Daga APC Kan Zargin Ɗoki-ɗora

MASU ALAKA

Ku Daure Ku Sake Zaɓar Mijina A 2027 – Remi Tinubu
Manyan Labarai

Ku Daure Ku Sake Zaɓar Mijina A 2027 – Remi Tinubu

September 9, 2026
Rashin Mulki Ke Firgita Atiku – Kakakin APC Na Kaduna
Siyasa

Rashin Mulki Ke Firgita Atiku – Kakakin APC Na Kaduna

September 9, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027
Siyasa

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Next Post
Shin Kasar Amurka Za Ta Iya Cika Alkawarinta?

Shin Kasar Amurka Za Ta Iya Cika Alkawarinta?

LABARAI MASU NASABA

Sin Ta Nuna Rashin Jin Dadinta Ga Italiya Da Tarayyar Turai Kan Ziyarar Jami’ar DPP

Sin Ta Nuna Rashin Jin Dadinta Ga Italiya Da Tarayyar Turai Kan Ziyarar Jami’ar DPP

September 11, 2026
Sin Tana Son Cin Moriya Tare Da Sassan Duniya A Fannin Kirkire-kirkire

Sin Tana Son Cin Moriya Tare Da Sassan Duniya A Fannin Kirkire-kirkire

September 11, 2026
Sin Da Indiya Na Shirye-shiryen Ganawar Xi Da Modi

Sin Da Indiya Na Shirye-shiryen Ganawar Xi Da Modi

September 11, 2026
Hadin Gwiwar Hada-Hadar Ba Da Hidima Tsakanin Sin Da Afirka Na Karfafa Karfin Afirka

Hadin Gwiwar Hada-Hadar Ba Da Hidima Tsakanin Sin Da Afirka Na Karfafa Karfin Afirka

September 11, 2026
Zaben 2027: Jam’iyyun Siyasa Sun Bayyana Shirinsu Yayin Da INEC Ta Fitar Da Jawalin Zabe

Dalilan Da Ya Sa Jam’iyyun Siyasa Suka Jinkirta Ƙaddamar Da Kwamitin Yaƙin Neman Zaɓen

September 11, 2026
Nazarin CGTN: Kungiyar BRICS Tana Kara Taka Rawar Gani A Harkokin Duniya

Nazarin CGTN: Kungiyar BRICS Tana Kara Taka Rawar Gani A Harkokin Duniya

September 11, 2026
Za A Ci ’Yan Siyasa Masu Kalaman Ɓatanci Tarar Miliyan 10 Da Ɗaurin Watanni 12 — INEC

2027: A Karon Farko INEC Za Ta Ƙaddamar Da Na’urar Bibiyar Zaɓen Nijeriya

September 11, 2026
Me Ya Sa Kamfanonin Amurka Ke Kyautata Zato Ga Sabuwar Damar Sin?

Me Ya Sa Kamfanonin Amurka Ke Kyautata Zato Ga Sabuwar Damar Sin?

September 11, 2026
Gwarzuwar Ma’aikaciyar Gwamnati Ta Shekarar 2026  Mrs Zubaida Umar

Gwarzuwar Ma’aikaciyar Gwamnati Ta Shekarar 2026 Mrs Zubaida Umar

September 11, 2026
Sin Ta Kafa Manufar Shiga Sahun Manyan Kasashen Dake Da Karfi A Harkar Kera Motoci A Duniya Nan Da Shekarar 2030

Sin Ta Kafa Manufar Shiga Sahun Manyan Kasashen Dake Da Karfi A Harkar Kera Motoci A Duniya Nan Da Shekarar 2030

September 11, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.