Tsohon gwamnan Jihar Kaduna, Nasir El-Rufa’i, ya bayyana cewa ana tilasta wa wasu ‘yan siyasa su koma jam’iyyar APC ko su ci gaba da zama a cikinta.
El-Rufa’i ya yi wannan magana ne yayin da ake shirin tunkarar babban zaɓen 2027.
- Ba Za Mu Aminta Da Hare-haren ‘Yan Bindiga Ba, Dole A Kawo Ƙarshensu — Tinubu
- Roberto De Zerbi Ya Raba Gari Da Olympique Marseille
Yayin tattaunawa da BBC, tsohon gwamnan ya ce, “Ko da yake ba a kama ni ba tukuna, an kama wasu daga cikin mutanen da na yi aiki da su a Kaduna, don haka ina ganin an kusa kama ni.”
A baya-bayan nan, an kama tsohon ministan shari’a na tarayya, Abubakar Malami, inda ake tuhumarsa da cin hanci da rashawa da kuma ɗaukar nauyin ta’addanci.
Malami ya musanta dukkanin waɗannan zarge-zargen.
El-Rufa’i kuma ya yi tsokaci kan gwamnati da jam’iyyar APC, wadda shi kansa ya taɓa kasancewa a ciki har ya kai ga matsayin gwamna na shekaru takwas a Kaduna.















Discussion about this post