• Leadership Hausa
Saturday, June 3, 2023
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Sana’a Sa’a
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Sana’a Sa’a
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Dalilan Da Ka Iya Jinkirta Kaddamar Da Majalisa Ta 10

by Yusuf Shuaibu
1 week ago
in Tambarin Dimokuradiyya
0
majalisar kasa
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Idan aka yi la’akari da canjin da aka samu a cikin karamin lokaci, akwai alamu masu karfi da ke nuna cewa za a iya jinkirta zaben shugabannin majalisar ta 10 wanda za a kaddamar a ranar Talata, 13 ga Yunin 2023.

Wata majiya mai tushe ta shaida wa LEADERSHIP cewa, ganin yadda takun saka a tsakanin zababbun ‘yan majalisar da ke goyon bayan ’yan takarar jam’iyyar APC mai mulki a zauren majalisar ta 10 da kuma masu bijire masu. Sabanin umarnin jam’iyya mai mulki, ana iya dakatar da zaben shugabannin majalisun guda biyu, wanda hakan na iya kawo jinkiri wajen kaddamar da majalisa ta 10, kamar yadda magatakardar majalisar dokoki ta kasa (CNA), Sani Magaji Tambuwal ya shelanta kan kaddamar da sabuwar majalisar, wanda za a iya jinkinta na wani dan lokaci.

  • Shugabancin Majalisa Ta 10: Katsalandan Din Gwamnati Ya Janyo Turka-Turka –  Hon. Bello

Wasikar shelan daga shugaban kasar wata makami ce da za ta bai wa magatakardar damar damar ci gaba da jan ragamar jagorancin majalisa ta 10 kafin zaben shugabanni.

Majiyar daga wurin manyan jiga-jigan jam’iyyar APC, sun shaida wa wakilinmu cewa, dabarar da Asiwaju Bola Ahmed Tinubu zai yi amfani da shi idan aka rantsar da shi a matsayin shugaban kasa shi ne, zai yi amfani da damarsa wajen hada kan ‘yan majalisar jam’iyyar APC wadanda ake ganin masu tayar da kayar baya a zauren majalisan domin kaucewa samun baraka kamar yadda jam’iyyar ta samu a 2011 da 2015.

LEADERSHIP ta ruwaito cewa an bayyana zababben sanata daga yankin kudu maso kudu, Sanata Godswill Akpabio da kuma Sanata Barau Jibril daga Arewa maso yamma a matsayin ‘yan takarar da jam’iyyar APC ta tsayar a matsayin shugaban majalisar dattawa da mataimakinsa. Yayin da aka zabi Tajudeen Abbas daga Arewa maso yamma da Benjamin Kalu daga kudu a matsayin shugabanm majalisar wakilai da mataimakinsa.

Labarai Masu Nasaba

An Fara Kunfar Baki Yayin Da Tinubu Ya Fara Nada Mukamai

Hasashe Game Da Manyan Alkalai Biyar Da Za Su Yanke Hukunci Kan Nasarar Tinubu

Rashin gamsuwa da hukuncin jam’iyyar na rashin tuntubar masu ruwa da tsaki tasa, Sanata Abdul’aziz Yari daga Arewa maso yamma da shugaban mai tsawatarwa na majalisar dattawa mai ci, Sanata Orji Uzor Kalu daga kudu maso gabas da zababben Sanata Osita Izunaso daga kudu maso gabas sun sha alwashin tsayawa takarar shugaban majalisar dattawa, domin kare ’yancin majalisar kamar yadda kundin tsarin mulki na 1999 da kuma dokar majalisar dattawa suna tanadar.

Har ila yau, Sanata Sani Musa daga shiyar Arewa ta tsakiya ya kalubalancin tsarin karba-karba na jam’iyyar APC, wasu zababbun ‘yan majalisu daga yankin Arewa ta tsakiya sun mara masa baya domin neman kujerar mataimakin shugaban majalisar dattawa a kan zaben da jam’iyyar ta tsayar da Barau.

A halin da ake ciki kuma, akwai rahotannin da ke cewa Yari da Kalu da Izunaso su uku na tunanin kulla kawance da tsohon gwamnan Jihar Zamfara a matsayin dan takarar da zai fafata da Akpabio tare da goyon bayan wasu tsirarun zababbun ‘yan majalisar ta 10 da ba a kaddamar da su ba.

Hakazalika, a zauren majalisar wakilai da ba a kaddamar ba, mambobin G6 da suka hada da mataimakin kakakin majalisar, Ahmed Idris Wase daga yankin Arewa ta tsakiya da Hon. Mukhtar Aliyu Betara daga Arewa ta gabas da Hon. Miriam Onuoha daga kudu ta gabas da Hon. Yusuf Adamu Gagdi daga Arewa ta tsakiya da Hon. Aminu Jaji daga Arewa maso yamma da kuma zababben dan majalisar Sada Soli Jibia daga Arewa maso yamma sun sha alwashin samar da dan takara daya tilo daga cikinsu domin ka da APC ta zabi Abbas.

Hukuncin da Yari, Kalu da Izunaso a gefe guda da kuma G6 a majalisar wakilai suka yi na ci gaba da tayar da kura bayan da shugabannin jam’iyyar APC na kasa suka yi watsi da alkawarin da suka yi musu na duba tsarin karba-karba mai cike da ce-ce-ku-ce da jam’iyyar ta dauka.

LEADERSHIP ta ruwaito cewa tuni harsashi ke ta yawo kan zaben Sanata Barau a matsayin mataimakin shugaban majalisar dattawa da kuma Hon. Abbas a matsayin shugaban majalisar wakilai a daidai lokacin da su biyun suka fito daga shiyyar Arewa maso yamma, yayin da jam’iyyar APC ta yi watsi da yankin Arewa ta tsakiya a tsarin karba-karbanta.

Zababben sanatan Zamfara ta yamma, kuma dan takarar shugabancin majalisar dattawa, Abdul’aziz Abubakar Yari ya nuna rashin amincewarsa da tsarin shiyya-shiyya na jam’iyyar APC mai mulki a majalisar dattawa ta 10 a kan cewa ya ci karo da kundin tsarin mulkin na 1999 wanda aka yi wa gyaran fuska.

ShareTweetSendShare
Previous Post

Mika Mulki: Yadda Buhari Ya Fara Damka Ragamar Shugabancin Nijeriya A Hannun Tinubu 

Next Post

Sin Ta Yi Kira Ga Kasa Da Kasa Su Kara Yawan Agajin Jin Kai Ga Yankin Kahon Afrika

Related

Yanzu-yanzu: Tinubu Na Ganawa Ta Farko Da Shugabannin Tsaro
Tambarin Dimokuradiyya

An Fara Kunfar Baki Yayin Da Tinubu Ya Fara Nada Mukamai

52 mins ago
Hasashe Game Da Manyan Alkalai Biyar Da Za Su Yanke Hukunci Kan Nasarar Tinubu
Tambarin Dimokuradiyya

Hasashe Game Da Manyan Alkalai Biyar Da Za Su Yanke Hukunci Kan Nasarar Tinubu

1 week ago
Ohanaeze Ta Bukaci Tinubu Ya Saki Nnamdi Kanu Idan Aka Rantsar Da Shi
Tambarin Dimokuradiyya

‘Yan Adawa Na Ci Gaba Da Kumfar Baki Kan Nasarar Tinubu

2 weeks ago
Shugabancin Majalisa Ta 10: Hannun Agogo Na Neman Koma Wa APC Baya
Tambarin Dimokuradiyya

Shugabancin Majalisa Ta 10: Hannun Agogo Na Neman Koma Wa APC Baya

2 weeks ago
…ACF Ta Nesanta Kanta Da Goyon Bayan Akpabio
Tambarin Dimokuradiyya

…ACF Ta Nesanta Kanta Da Goyon Bayan Akpabio

3 weeks ago
Shugabancin Majalisa Ta 10: Ko ‘Yan Mowar APC Za Su Kai Bantensu?
Tambarin Dimokuradiyya

Shugabancin Majalisa Ta 10: Ko ‘Yan Mowar APC Za Su Kai Bantensu?

3 weeks ago
Next Post
Sin Ta Yi Kira Ga Kasa Da Kasa Su Kara Yawan Agajin Jin Kai Ga Yankin Kahon Afrika

Sin Ta Yi Kira Ga Kasa Da Kasa Su Kara Yawan Agajin Jin Kai Ga Yankin Kahon Afrika

LABARAI MASU NASABA

Yanzu-yanzu: Tinubu Na Ganawa Ta Farko Da Shugabannin Tsaro

An Fara Kunfar Baki Yayin Da Tinubu Ya Fara Nada Mukamai

June 3, 2023
Xi Jinping Ya Jaddada Bukatar Gina Kasar Sin Mai Wayewar Kai Ta Zamani

Xi Jinping Ya Jaddada Bukatar Gina Kasar Sin Mai Wayewar Kai Ta Zamani

June 2, 2023
Kasar Sin Ta Bayyana Korafinta Dangane Da Yarjejeniyar Cinikayya Da Aka Kulla Tsakanin Amurka Da Taiwan

Kasar Sin Ta Bayyana Korafinta Dangane Da Yarjejeniyar Cinikayya Da Aka Kulla Tsakanin Amurka Da Taiwan

June 2, 2023
Taron Tattaunawar Shangri-La Ya Nuna Ra’ayin Tabbatar Da Zaman Lafiya Na Sin

Taron Tattaunawar Shangri-La Ya Nuna Ra’ayin Tabbatar Da Zaman Lafiya Na Sin

June 2, 2023
Shawarwarin Tsohon Shugaban Kasa Babangida Ga Tinubu

Shawarwarin Tsohon Shugaban Kasa Babangida Ga Tinubu

June 2, 2023
Tinubu Ya Yi Alkawarin Inganta Mafi Karancin Albashin Ma’aikata

Tinubu Ya Yi Alkawarin Inganta Mafi Karancin Albashin Ma’aikata

June 2, 2023
Yadda Aka Kammala Gasar Firimiya Ta Bana

Yadda Aka Kammala Gasar Firimiya Ta Bana

June 2, 2023
An Dakatar Da “Wasan Matsorata” Da Jam’iyyun Siyasan Amurka Suke Yi Amma Damuwa Ta Dore

An Dakatar Da “Wasan Matsorata” Da Jam’iyyun Siyasan Amurka Suke Yi Amma Damuwa Ta Dore

June 2, 2023
Tinubu Ya Gana Da Makinde, Wike Da Ibori

Tinubu Ya Gana Da Makinde, Wike Da Ibori

June 2, 2023
RCEP Ta Fara Aiki A Kasashe 15 Da Suka Sa Hannu Kan Yarjejeniyar

RCEP Ta Fara Aiki A Kasashe 15 Da Suka Sa Hannu Kan Yarjejeniyar

June 2, 2023
Advertise with us

© 2022 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2022 Leadership Media Group - All Right Reserved.