• English
  • Business News
Sunday, July 13, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Dalilan Da Ka Iya Jinkirta Kaddamar Da Majalisa Ta 10

by Yusuf Shuaibu
2 years ago
in Tambarin Dimokuradiyya
0
majalisar kasa
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Idan aka yi la’akari da canjin da aka samu a cikin karamin lokaci, akwai alamu masu karfi da ke nuna cewa za a iya jinkirta zaben shugabannin majalisar ta 10 wanda za a kaddamar a ranar Talata, 13 ga Yunin 2023.

Wata majiya mai tushe ta shaida wa LEADERSHIP cewa, ganin yadda takun saka a tsakanin zababbun ‘yan majalisar da ke goyon bayan ’yan takarar jam’iyyar APC mai mulki a zauren majalisar ta 10 da kuma masu bijire masu. Sabanin umarnin jam’iyya mai mulki, ana iya dakatar da zaben shugabannin majalisun guda biyu, wanda hakan na iya kawo jinkiri wajen kaddamar da majalisa ta 10, kamar yadda magatakardar majalisar dokoki ta kasa (CNA), Sani Magaji Tambuwal ya shelanta kan kaddamar da sabuwar majalisar, wanda za a iya jinkinta na wani dan lokaci.

  • Shugabancin Majalisa Ta 10: Katsalandan Din Gwamnati Ya Janyo Turka-Turka –  Hon. Bello

Wasikar shelan daga shugaban kasar wata makami ce da za ta bai wa magatakardar damar damar ci gaba da jan ragamar jagorancin majalisa ta 10 kafin zaben shugabanni.

Majiyar daga wurin manyan jiga-jigan jam’iyyar APC, sun shaida wa wakilinmu cewa, dabarar da Asiwaju Bola Ahmed Tinubu zai yi amfani da shi idan aka rantsar da shi a matsayin shugaban kasa shi ne, zai yi amfani da damarsa wajen hada kan ‘yan majalisar jam’iyyar APC wadanda ake ganin masu tayar da kayar baya a zauren majalisan domin kaucewa samun baraka kamar yadda jam’iyyar ta samu a 2011 da 2015.

LEADERSHIP ta ruwaito cewa an bayyana zababben sanata daga yankin kudu maso kudu, Sanata Godswill Akpabio da kuma Sanata Barau Jibril daga Arewa maso yamma a matsayin ‘yan takarar da jam’iyyar APC ta tsayar a matsayin shugaban majalisar dattawa da mataimakinsa. Yayin da aka zabi Tajudeen Abbas daga Arewa maso yamma da Benjamin Kalu daga kudu a matsayin shugabanm majalisar wakilai da mataimakinsa.

Labarai Masu Nasaba

Rashin Ganin Shugabannin APC Yayin Ziyarar Shettima A Kano Ya Haifar Da Zazzafar Muhawara

Hadakar Jam’iyyar ADC Ta Fara Dusashe Karfin PDP A Wasu Jihohin Nijeriya

Rashin gamsuwa da hukuncin jam’iyyar na rashin tuntubar masu ruwa da tsaki tasa, Sanata Abdul’aziz Yari daga Arewa maso yamma da shugaban mai tsawatarwa na majalisar dattawa mai ci, Sanata Orji Uzor Kalu daga kudu maso gabas da zababben Sanata Osita Izunaso daga kudu maso gabas sun sha alwashin tsayawa takarar shugaban majalisar dattawa, domin kare ’yancin majalisar kamar yadda kundin tsarin mulki na 1999 da kuma dokar majalisar dattawa suna tanadar.

Har ila yau, Sanata Sani Musa daga shiyar Arewa ta tsakiya ya kalubalancin tsarin karba-karba na jam’iyyar APC, wasu zababbun ‘yan majalisu daga yankin Arewa ta tsakiya sun mara masa baya domin neman kujerar mataimakin shugaban majalisar dattawa a kan zaben da jam’iyyar ta tsayar da Barau.

A halin da ake ciki kuma, akwai rahotannin da ke cewa Yari da Kalu da Izunaso su uku na tunanin kulla kawance da tsohon gwamnan Jihar Zamfara a matsayin dan takarar da zai fafata da Akpabio tare da goyon bayan wasu tsirarun zababbun ‘yan majalisar ta 10 da ba a kaddamar da su ba.

Hakazalika, a zauren majalisar wakilai da ba a kaddamar ba, mambobin G6 da suka hada da mataimakin kakakin majalisar, Ahmed Idris Wase daga yankin Arewa ta tsakiya da Hon. Mukhtar Aliyu Betara daga Arewa ta gabas da Hon. Miriam Onuoha daga kudu ta gabas da Hon. Yusuf Adamu Gagdi daga Arewa ta tsakiya da Hon. Aminu Jaji daga Arewa maso yamma da kuma zababben dan majalisar Sada Soli Jibia daga Arewa maso yamma sun sha alwashin samar da dan takara daya tilo daga cikinsu domin ka da APC ta zabi Abbas.

Hukuncin da Yari, Kalu da Izunaso a gefe guda da kuma G6 a majalisar wakilai suka yi na ci gaba da tayar da kura bayan da shugabannin jam’iyyar APC na kasa suka yi watsi da alkawarin da suka yi musu na duba tsarin karba-karba mai cike da ce-ce-ku-ce da jam’iyyar ta dauka.

LEADERSHIP ta ruwaito cewa tuni harsashi ke ta yawo kan zaben Sanata Barau a matsayin mataimakin shugaban majalisar dattawa da kuma Hon. Abbas a matsayin shugaban majalisar wakilai a daidai lokacin da su biyun suka fito daga shiyyar Arewa maso yamma, yayin da jam’iyyar APC ta yi watsi da yankin Arewa ta tsakiya a tsarin karba-karbanta.

Zababben sanatan Zamfara ta yamma, kuma dan takarar shugabancin majalisar dattawa, Abdul’aziz Abubakar Yari ya nuna rashin amincewarsa da tsarin shiyya-shiyya na jam’iyyar APC mai mulki a majalisar dattawa ta 10 a kan cewa ya ci karo da kundin tsarin mulkin na 1999 wanda aka yi wa gyaran fuska.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Mika Mulki: Yadda Buhari Ya Fara Damka Ragamar Shugabancin Nijeriya A Hannun Tinubu 

Next Post

Sin Ta Yi Kira Ga Kasa Da Kasa Su Kara Yawan Agajin Jin Kai Ga Yankin Kahon Afrika

Related

Kashim Shettima Ya Mayar Da Martani Kan Tsadar Rayuwa
Tambarin Dimokuradiyya

Rashin Ganin Shugabannin APC Yayin Ziyarar Shettima A Kano Ya Haifar Da Zazzafar Muhawara

1 day ago
Hadakar Jam’iyyar ADC Ta Fara Dusashe Karfin PDP A Wasu Jihohin Nijeriya
Tambarin Dimokuradiyya

Hadakar Jam’iyyar ADC Ta Fara Dusashe Karfin PDP A Wasu Jihohin Nijeriya

1 day ago
Nijeriya Na Fuskantar Siyasa Mara Tabbas —  Peter Obi
Tambarin Dimokuradiyya

2027: Takarar Shugaban Kasa Zan Yi Ba Mataimaki Ba – Peter Obi

1 day ago
Yadda Taron Kungiyar Gwagwarmayar Talakawa Ta Kaya Kan Zaben 2023 A Zariya
Tambarin Dimokuradiyya

INEC Ta Ayyana 16 Ga Agusta Don Gudanar Da Zaben Cike Gurbi A Jihohi 12

1 week ago
Ganduje Na Kara Shan Matsin Lamba A Kan Ya Sauka
Tambarin Dimokuradiyya

APC: Ko Sadaukarwar Ganduje Za Ta Dakile Barazanar Jam’iyyun Adawa A Zaben 2027?

1 week ago
Zaben Gwamnoni: Za Mu Ba Marada Kunya – INEC
Tambarin Dimokuradiyya

2027: Kungiyoyi 110 Ne Ke Neman Rajistan Zama Jam’iyyun Siyasa A Yanzu Haka – INEC

1 week ago
Next Post
Sin Ta Yi Kira Ga Kasa Da Kasa Su Kara Yawan Agajin Jin Kai Ga Yankin Kahon Afrika

Sin Ta Yi Kira Ga Kasa Da Kasa Su Kara Yawan Agajin Jin Kai Ga Yankin Kahon Afrika

LABARAI MASU NASABA

NAFDAC Da Masu Maganin Gargajiya Za Su Tsabtace Sana’ar Sayar Da Maganin Gargajiya A Nijeriya

NAFDAC Da Masu Maganin Gargajiya Za Su Tsabtace Sana’ar Sayar Da Maganin Gargajiya A Nijeriya

July 12, 2025
Shugaban Guinea Bissau Ya Bayyana Sin A Matsayin Abokiyar Hulda Ta Hakika

Shugaban Guinea Bissau Ya Bayyana Sin A Matsayin Abokiyar Hulda Ta Hakika

July 12, 2025
Akwai Bukatar Manyan Jaruman Da Suka Yi Kudi Su Taimaki Na Baya -Barau Dadin Kowa

Akwai Bukatar Manyan Jaruman Da Suka Yi Kudi Su Taimaki Na Baya -Barau Dadin Kowa

July 12, 2025
Wang Yi Ya Yi Karin Haske Game Da Taron Ministocin Harkokin Wajen Sin Da Amurka 

Wang Yi Ya Yi Karin Haske Game Da Taron Ministocin Harkokin Wajen Sin Da Amurka 

July 12, 2025
Yadda Iyaye Ke Rungumar Bokaye Don Samar Wa ‘Ya’yansu Mata Mazaje Masu Kudi

Yadda Iyaye Ke Rungumar Bokaye Don Samar Wa ‘Ya’yansu Mata Mazaje Masu Kudi

July 12, 2025
Sin Ta Yi Kira Da A Karfafa Hadin Gwiwa A Fannin Tattalin Arziki Na Zamani

Sin Ta Yi Kira Da A Karfafa Hadin Gwiwa A Fannin Tattalin Arziki Na Zamani

July 12, 2025
Tinubu Ya Baro Brazil Bayan Halartar Taron BRICS Na 2025

Tinubu Ya Baro Brazil Bayan Halartar Taron BRICS Na 2025

July 12, 2025
Shugaban Nauru: Ci Gaban Sin Darasi Ne Ga Nauru Da Duniya Baki Daya

Shugaban Nauru: Ci Gaban Sin Darasi Ne Ga Nauru Da Duniya Baki Daya

July 12, 2025
Tinubu Yana Goyon Bayan Ƙananan Hukumomi Su Ci Gashin Kan Su – Minista

Tinubu Yana Goyon Bayan Ƙananan Hukumomi Su Ci Gashin Kan Su – Minista

July 12, 2025
Danbun Shinkafa Da Nama Da Kifi

Danbun Shinkafa Da Nama Da Kifi

July 12, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.