ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Sunday, June 14, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Dalilan Da Ka Iya Jinkirta Kaddamar Da Majalisa Ta 10

by Yusuf Shuaibu
3 years ago
majalisar kasa

Idan aka yi la’akari da canjin da aka samu a cikin karamin lokaci, akwai alamu masu karfi da ke nuna cewa za a iya jinkirta zaben shugabannin majalisar ta 10 wanda za a kaddamar a ranar Talata, 13 ga Yunin 2023.

Wata majiya mai tushe ta shaida wa LEADERSHIP cewa, ganin yadda takun saka a tsakanin zababbun ‘yan majalisar da ke goyon bayan ’yan takarar jam’iyyar APC mai mulki a zauren majalisar ta 10 da kuma masu bijire masu. Sabanin umarnin jam’iyya mai mulki, ana iya dakatar da zaben shugabannin majalisun guda biyu, wanda hakan na iya kawo jinkiri wajen kaddamar da majalisa ta 10, kamar yadda magatakardar majalisar dokoki ta kasa (CNA), Sani Magaji Tambuwal ya shelanta kan kaddamar da sabuwar majalisar, wanda za a iya jinkinta na wani dan lokaci.

  • Shugabancin Majalisa Ta 10: Katsalandan Din Gwamnati Ya Janyo Turka-Turka –  Hon. Bello

Wasikar shelan daga shugaban kasar wata makami ce da za ta bai wa magatakardar damar damar ci gaba da jan ragamar jagorancin majalisa ta 10 kafin zaben shugabanni.

ADVERTISEMENT

Majiyar daga wurin manyan jiga-jigan jam’iyyar APC, sun shaida wa wakilinmu cewa, dabarar da Asiwaju Bola Ahmed Tinubu zai yi amfani da shi idan aka rantsar da shi a matsayin shugaban kasa shi ne, zai yi amfani da damarsa wajen hada kan ‘yan majalisar jam’iyyar APC wadanda ake ganin masu tayar da kayar baya a zauren majalisan domin kaucewa samun baraka kamar yadda jam’iyyar ta samu a 2011 da 2015.

LEADERSHIP ta ruwaito cewa an bayyana zababben sanata daga yankin kudu maso kudu, Sanata Godswill Akpabio da kuma Sanata Barau Jibril daga Arewa maso yamma a matsayin ‘yan takarar da jam’iyyar APC ta tsayar a matsayin shugaban majalisar dattawa da mataimakinsa. Yayin da aka zabi Tajudeen Abbas daga Arewa maso yamma da Benjamin Kalu daga kudu a matsayin shugabanm majalisar wakilai da mataimakinsa.

LABARAI MASU NASABA

2027: Kallo Ya Koma Kan Yadda APC, ADC Da PDP Ke Neman Abokan Takarar Mataimakin Shugaban Kasa

Ko INEC Na Da Hannu A Rikice-rikicen Jam’iyyun Siyasa A Nijeriya?

Rashin gamsuwa da hukuncin jam’iyyar na rashin tuntubar masu ruwa da tsaki tasa, Sanata Abdul’aziz Yari daga Arewa maso yamma da shugaban mai tsawatarwa na majalisar dattawa mai ci, Sanata Orji Uzor Kalu daga kudu maso gabas da zababben Sanata Osita Izunaso daga kudu maso gabas sun sha alwashin tsayawa takarar shugaban majalisar dattawa, domin kare ’yancin majalisar kamar yadda kundin tsarin mulki na 1999 da kuma dokar majalisar dattawa suna tanadar.

Har ila yau, Sanata Sani Musa daga shiyar Arewa ta tsakiya ya kalubalancin tsarin karba-karba na jam’iyyar APC, wasu zababbun ‘yan majalisu daga yankin Arewa ta tsakiya sun mara masa baya domin neman kujerar mataimakin shugaban majalisar dattawa a kan zaben da jam’iyyar ta tsayar da Barau.

A halin da ake ciki kuma, akwai rahotannin da ke cewa Yari da Kalu da Izunaso su uku na tunanin kulla kawance da tsohon gwamnan Jihar Zamfara a matsayin dan takarar da zai fafata da Akpabio tare da goyon bayan wasu tsirarun zababbun ‘yan majalisar ta 10 da ba a kaddamar da su ba.

Hakazalika, a zauren majalisar wakilai da ba a kaddamar ba, mambobin G6 da suka hada da mataimakin kakakin majalisar, Ahmed Idris Wase daga yankin Arewa ta tsakiya da Hon. Mukhtar Aliyu Betara daga Arewa ta gabas da Hon. Miriam Onuoha daga kudu ta gabas da Hon. Yusuf Adamu Gagdi daga Arewa ta tsakiya da Hon. Aminu Jaji daga Arewa maso yamma da kuma zababben dan majalisar Sada Soli Jibia daga Arewa maso yamma sun sha alwashin samar da dan takara daya tilo daga cikinsu domin ka da APC ta zabi Abbas.

Hukuncin da Yari, Kalu da Izunaso a gefe guda da kuma G6 a majalisar wakilai suka yi na ci gaba da tayar da kura bayan da shugabannin jam’iyyar APC na kasa suka yi watsi da alkawarin da suka yi musu na duba tsarin karba-karba mai cike da ce-ce-ku-ce da jam’iyyar ta dauka.

LEADERSHIP ta ruwaito cewa tuni harsashi ke ta yawo kan zaben Sanata Barau a matsayin mataimakin shugaban majalisar dattawa da kuma Hon. Abbas a matsayin shugaban majalisar wakilai a daidai lokacin da su biyun suka fito daga shiyyar Arewa maso yamma, yayin da jam’iyyar APC ta yi watsi da yankin Arewa ta tsakiya a tsarin karba-karbanta.

Zababben sanatan Zamfara ta yamma, kuma dan takarar shugabancin majalisar dattawa, Abdul’aziz Abubakar Yari ya nuna rashin amincewarsa da tsarin shiyya-shiyya na jam’iyyar APC mai mulki a majalisar dattawa ta 10 a kan cewa ya ci karo da kundin tsarin mulkin na 1999 wanda aka yi wa gyaran fuska.

majalisa
Yusuf Shuaibu
+ postsBio
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    2027: Kallo Ya Koma Kan Yadda APC, ADC Da PDP Ke Neman Abokan Takarar Mataimakin Shugaban Kasa
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Ko INEC Na Da Hannu A Rikice-rikicen Jam’iyyun Siyasa A Nijeriya?
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Hukuncin Kotu Na Barazana Ga Zaben 2027 —INEC
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Matsalar Tsaro Da Tsadar Kayan Noma Na Barazana Ga Samar Da Abinci A Daminar Bana

MASU ALAKA

2027: Kallo Ya Koma Kan Yadda APC, ADC Da PDP Ke Neman Abokan Takarar Mataimakin Shugaban Kasa
Tambarin Dimokuradiyya

2027: Kallo Ya Koma Kan Yadda APC, ADC Da PDP Ke Neman Abokan Takarar Mataimakin Shugaban Kasa

June 12, 2026
Ko INEC Na Da Hannu A Rikice-rikicen Jam’iyyun Siyasa A Nijeriya?
Tambarin Dimokuradiyya

Ko INEC Na Da Hannu A Rikice-rikicen Jam’iyyun Siyasa A Nijeriya?

June 12, 2026
Gwamnatin Tinubu “Kasuwa Ce Mara Amfani Ga Talaka” – PDP
Tambarin Dimokuradiyya

Zaben Fitar Da Gwani Na APC: Tinubu Zai Shiga Tsakani Wajen Warware Rikicin Jam’iyyar

June 5, 2026
Next Post
Sin Ta Yi Kira Ga Kasa Da Kasa Su Kara Yawan Agajin Jin Kai Ga Yankin Kahon Afrika

Sin Ta Yi Kira Ga Kasa Da Kasa Su Kara Yawan Agajin Jin Kai Ga Yankin Kahon Afrika

LABARAI MASU NASABA

Cututtukan Da Aka Fi Fama Da Su Lokacin Damina Da Yadda Za A Kauce Musu (1)

Cututtukan Da Aka Fi Fama Da Su Lokacin Damina Da Yadda Za A Kauce Musu (1)

June 13, 2026
Talauci Ya Sake Karuwa Da Kashi 63 Duk Da Sauye-sauyen Tattalin Arzikin Da Gwamnati Ta Yi – IMF

Talauci Ya Sake Karuwa Da Kashi 63 Duk Da Sauye-sauyen Tattalin Arzikin Da Gwamnati Ta Yi – IMF

June 13, 2026
Muhallin Halittu Da Aka Yi Gado A Kasar Sin Sun Samu Ci Gaba Ta Fuskar Ba Su Kariya

Muhallin Halittu Da Aka Yi Gado A Kasar Sin Sun Samu Ci Gaba Ta Fuskar Ba Su Kariya

June 13, 2026
Gwamnonin Arewa-maso-yamma Sun Kaddamar Da Shirin Rage Radadin Talauci A Yankin

Gwamnonin Arewa-maso-yamma Sun Kaddamar Da Shirin Rage Radadin Talauci A Yankin

June 13, 2026

Sake Jan Damarar Soja Da Japan Ke Yi Karin Alama Ce Mai Hadari

June 13, 2026
NANS Ta Kafa Kwamitin Ganin Yadda Ake Tafiyar Da Ayyukan TETFund

NANS Ta Kafa Kwamitin Ganin Yadda Ake Tafiyar Da Ayyukan TETFund

June 13, 2026
Shugaban Majalisar Bayar Da Shawara Kan Harkokin Siyasa Ta Kasar Sin Ya Yi Kira Da A Raya Dangantakar Gabobi Biyu Na Mashigin Tekun Taiwan Cikin Lumana

Shugaban Majalisar Bayar Da Shawara Kan Harkokin Siyasa Ta Kasar Sin Ya Yi Kira Da A Raya Dangantakar Gabobi Biyu Na Mashigin Tekun Taiwan Cikin Lumana

June 13, 2026
Ghana Za Ta Kai Ƙarar Canada Kotu Kan Hana Thomas Partey Shiga Ƙasar

Ghana Za Ta Kai Ƙarar Canada Kotu Kan Hana Thomas Partey Shiga Ƙasar

June 13, 2026
Sin Ta Zama Abin Koyi Na Sauyi Da Ci Gaba Ga Kasashe Da Dama, In Ji Shalva Papuashvili

Sin Ta Zama Abin Koyi Na Sauyi Da Ci Gaba Ga Kasashe Da Dama, In Ji Shalva Papuashvili

June 13, 2026
Garkuwa Da Mutane Na Barazana Ga Dalibai Miliyan 1.9 Masu Jarrabawar WAEC A Sassan Nijeriya

Garkuwa Da Mutane Na Barazana Ga Dalibai Miliyan 1.9 Masu Jarrabawar WAEC A Sassan Nijeriya

June 13, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.