ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, September 10, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Dattawan Borno Sun Roƙi Tinubu Da Zulum Su Ceto Mutane 116 Da Aka Sace

by Abubakar Sulaiman
3 weeks ago

Taron Dattawan Hawul da Askira-Uba na jihar Borno, gami da iyalan waɗanda abin ya shafa, sun fashe da kuka tare da nuna matuƙar damuwa a yayin da suka yi kira na musamman ga Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu da kuma Gwamna Babagana Umara Zulum. Sun roƙi shugabannin da su gaggauta ɗaukar matakin ceto mutane 116 da suka haɗa da ɗalibai 78 da wasu mutane 38 da suka kwashe kwanaki 100 cif suna hannun masu garkuwa da mutane.

Da ya ke jawabi a madadin dattawan a taron manema labarai da suka gudanar a Abuja a ranar Juma’a, Sakataren ƙungiyar dattawan, Malla Gadzama, ya bayyana cewa ɗalibai 42 na makarantar firamare da ƙaramar sakandare ta Mussa da ke ƙaramar hukumar Askira-Uba an sace su ne tun ranar 15 ga watan Mayun 2026. Ya koka da cewa iyalan waɗannan yara sun shafe kwanaki 100 na raba-ido, da baƙin ciki, da tsoro, da kuma fargaba marar musaltuwa. Gadzama ya kuma tunatar da yadda aka sace wasu dalibai da malamai a jihar Oyo a ranar ɗaya, amma tuni aka ceto su, saɓanin nasu na Borno da har yanzu suke tsare a jeji.

Sakataren dattawan ya yi kira ga Gwamna Zulum da ya yi amfani da dukkan ƙarfin ofishinsa don haɗa kai da gwamnatin tarayya da hukumomin tsaro wajen gano mutanen. Haka zalika, wani ɗan majalisa mai wakiltar mazabar Askira-Uba da Hawul, Hon. Midala Balami, wanda shi ma yana cikin tawagar taron, ya koka kan rashin taɓuka abin kirki daga ɓangaren gwamnati duk da cewa ya gabatar da batun a gaban zauren majalisar tarayya a matsayin lamari mai matuƙar muhimmanci a lokacin da abin ya faru. Ya nemi gwamnati ta tashi tsaye wajen tabbatar da tsaron rayuka da dukiyoyin ƴan ƙasa, wanda hakan shi ne babban nauyin da ya rataya a wuyanta.

ADVERTISEMENT

A wani ɓangaren kuma, Gwamna Babagana Zulum ya karɓi bakuncin wasu daga cikin iyalan yaran na garin Mussa a gidan gwamnati da ke Maiduguri a ranar Juma’a, inda ya kwantar musu da hankali tare da tabbatar musu da cewa gwamnati na ci gaba da aikin ganin an ceto yaran nasu lami lafiya. Gwamnan ya isar da sakon jaje daga Shugaba Tinubu sannan ya tabbatar da cewa shugaban ƙasar ya riga ya ba jami’an tsaro umarnin ceto dukkan waɗanda lamarin ya shafa.

Wannan batu dai na ci gaba da janyo hankalin al’umma, yayin da iyalan da abin ya shafa suke ci gaba da zura idon ganin ranar da za a ceto ƴaƴansu da sauran ƴan uwansu daga wannan halin kuncin.

LABARAI MASU NASABA

Ku Daure Ku Sake Zaɓar Mijina A 2027 – Remi Tinubu

’Yansanda Sun Cafke Matar Da Ta Kwara Wa Maƙociyarta Tafasasshen Ruwan Zafi A Abuja

Abubakar Sulaiman
Website |  + postsBio
  • Abubakar Sulaiman
    Iyalin El-Rufai Sun Bai Ministan Tsaro Wa’adin Kwana 7 Kan Zargin Rikicin Kudancin Kaduna
  • Abubakar Sulaiman
    Atiku Ya Zargi Gwamnatin Tarayya Da Cin Bashi Kamar Mashayin Da Kuɗi Ya Ƙarewa
  • Abubakar Sulaiman
    Boko Haram Ta Kai Hari Adamawa, Ana Fargabar Mutuwar Mutane 11
  • Abubakar Sulaiman
    Ƴan Bindiga Sun Kai Hari Sokoto, Sun Kashe Mutane 7, Sun Yi Garkuwa Da 12

MASU ALAKA

Ku Daure Ku Sake Zaɓar Mijina A 2027 – Remi Tinubu
Manyan Labarai

Ku Daure Ku Sake Zaɓar Mijina A 2027 – Remi Tinubu

September 9, 2026
’Yansanda Sun Cafke Matar Da Ta Kwara Wa Maƙociyarta Tafasasshen Ruwan Zafi A Abuja
Manyan Labarai

’Yansanda Sun Cafke Matar Da Ta Kwara Wa Maƙociyarta Tafasasshen Ruwan Zafi A Abuja

September 9, 2026
’Yan Takarar ADC A Arewa Maso Yamma Sun Yi Alƙawarin Biyan N110,000 A Matsayin Mafi Ƙarancin Albashi
Manyan Labarai

’Yan Takarar ADC A Arewa Maso Yamma Sun Yi Alƙawarin Biyan N110,000 A Matsayin Mafi Ƙarancin Albashi

September 9, 2026
Next Post

Rasha Da Ukraine Sun Zafafa Hare-hare Kan Juna Bayan Yaƙinsu Ya Ɗauki Sabon Salo

LABARAI MASU NASABA

Sin Na Fatan Amurka Za Ta Dakatar Da Furta Karairayi Da Nufin Bata Mata Suna

Sin Na Fatan Amurka Za Ta Dakatar Da Furta Karairayi Da Nufin Bata Mata Suna

September 9, 2026
An Kashe Shahararren Mai Sharhin Siyasar Kano, Ibrahim Dan Shagamu

An Kashe Shahararren Mai Sharhin Siyasar Kano, Ibrahim Dan Shagamu

September 9, 2026
Sin Ba Ta Taba Janyewa Wata Kasa Tsani Ba

Sin Ba Ta Taba Janyewa Wata Kasa Tsani Ba

September 9, 2026
Xi Ya Aike Da Gaisuwa Albarkacin Ranar Malamai Yana Mai Kira Da A Samar Da Matasa Masu Hazaka Domin Kara Farfado Da Kasa

Xi Ya Aike Da Gaisuwa Albarkacin Ranar Malamai Yana Mai Kira Da A Samar Da Matasa Masu Hazaka Domin Kara Farfado Da Kasa

September 9, 2026
Ku Daure Ku Sake Zaɓar Mijina A 2027 – Remi Tinubu

Ku Daure Ku Sake Zaɓar Mijina A 2027 – Remi Tinubu

September 9, 2026
Renon Matasa A Kan Kyakkyawar Turba Ginshiki Ne Na Gina KasaBy

Renon Matasa A Kan Kyakkyawar Turba Ginshiki Ne Na Gina KasaBy

September 9, 2026
Bikin CIFTIS Zai Ingiza Bude Kofa A Kasar Sin

Bikin CIFTIS Zai Ingiza Bude Kofa A Kasar Sin

September 9, 2026
“Ajin Tashar Sararin Samaniya Na Hong Kong Da Macau” Ya Kara Wa Matasa Sha’awar Kimiyya Da Karfafa Kishin Kasa

“Ajin Tashar Sararin Samaniya Na Hong Kong Da Macau” Ya Kara Wa Matasa Sha’awar Kimiyya Da Karfafa Kishin Kasa

September 9, 2026
’Yansanda Sun Cafke Matar Da Ta Kwara Wa Maƙociyarta Tafasasshen Ruwan Zafi A Abuja

’Yansanda Sun Cafke Matar Da Ta Kwara Wa Maƙociyarta Tafasasshen Ruwan Zafi A Abuja

September 9, 2026
Taron Kolin Urumqi Ya Mayar Da Hankali Kan Kwarewar Shugabanci A Xinjiang Da Muhimmancinta Ga Duniya

Taron Kolin Urumqi Ya Mayar Da Hankali Kan Kwarewar Shugabanci A Xinjiang Da Muhimmancinta Ga Duniya

September 9, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.