ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Daukaka Karar Shari’o’in Zabe: Wasu Hukunce-hukunce Sun Yi Ba-zata

by Yusuf Shuaibu
3 years ago
Zabe

A ci gaba da sauraron kararrakin zabe da aka shigar a kotunan daukaka kara da ke Abuja da Legas, an samu bazata a wasu daga cikin hukunce-hukuncen da aka zartar da hukunci a wannan mako, musamman ma a shari’o’in ‘yan majalisa na jiha da kuma na gwamna.

Idan dai za a iya tunawa, an rarraba shari’o’in zuwa bangare guda biyu, inda aka mayar da dukkan shari’o’in zaben da aka daukaka kara na yankin arewa a sashin kotun daukaka kara da ke Abuja, yayin da reshen kotun daukaka kara da ke Legas zai yanke hukuncin dukkanin kararrakin zabe na yankin kudu.

  • Gwamnatin Tarayya Ta Yi Fatali Da Zargin Da Obi Ya Yi Mata Kan Karin Kasafin Kuɗi
  • Gaza: Majalisar Dattawa Ta Nemi Nijeriya Ta Matsa Lambar Kafa Kasashe Biyu

Kotun daukaka kara da ke Abuja ta kori nasarar Musa Ilyasu Kwankwaso na jam’iyyar APC, a matsayin dan majalisa mai wakiltar mazabar Kura/Madobi/Garun Malam.
Ta tabbatar da nasarar dan takarar jam’iyyar NNPP, Yusuf Umar Datti, a matsayin halattaccen dan majalisa.

ADVERTISEMENT

A hukuncin da ta yanke mai alkalai uku karkashin jagorancin mai shari’a Tunde Oyebamiji Awotoye, kotun ta tabbatar da nasarar Datti, wanda tun farko hukumar zabe mai zaman kanta ta kasa (INEC) ta ayyana a matsayin wanda ya lashe zabe.

Sai dai kuma kotun sauraron kararrakin zabe da ke zamanta a Jihar Kano, ta bai wa Kwankwaso nasara.

LABARAI MASU NASABA

2027: Rashin Hadin Kan Atiku Da Obi Da Kwankwaso Na Iya Taimaka Wa Tazarcen Tinubu

Jam’iyyun Siyasa A Nijeriya Sun Shiga Rudani A Yayin Da Wa’adin Mika Sunayen Mambobi Ya Shude

Mai shari’a Awotoye cewa kotun sauraron kararrakin zabe ta yi kuskure. Alkalin ya lura cewa an yi amfani da sashe na 77 na dokar zabe. Ya ce babu wata kotu da ke da hurumin yin kasalandan a rikicin cikin gida na jam’iyya.

A bangare guda kuma, kotun daukaka kara reshen Jihar Legas ta kuma kori Darlington Nwokocha, shugaban marasa rinjaye na majalisar dattawa, mai wakiltar Abiya ta tsakiya a karkashin jam’iyyar LP.

Kotun ta bayyana Augustine Akobundu na jam’iyyar PDP a matsayin wanda ya lashe zaben da aka gudanar a ranar 25 ga watan Fabrairu na yankin majalisar dattawa.
Yayin da kotun daukaka kara da ke zamanta a Abuja ta kuma kori tsohon gwamnan Jihar Benuwai, Gabriel Suswam daga majalisar dattawa.

Kotun ta ayyana Mista Emmanuel Udende na jam’iyyar APC a matsayin wanda ya yi nasara.

Haka kuma kotun daukaka kara da ke Abuja ta kuma kori Sanata Ishaku Abbo, dan majalisa mai wakiltar Adamawa ta Arewa a majalisar dattawa, wanda ta ayyana dan takarar jam’iyyar PDP, Amos Yohanna a matsayin wanda ya yi nasara.

Kotun daukaka kara da ke zamanta a Abuja ta kuma kori dan majalisa mai wakiltar Mubi ta Arewa da Mubi ta Kudu da kuma Maiha ta Jihar Adamawa a zauren majalisar wakilai, Hon. Jingi Rufai.

Kotun ta kori dan takarar jam’iyyar PDP a zaben majalisar, yayin da ta bayyana Hon. Jaafar Magaji na jam’iyyar APC a matsayin wanda ya lashe zaben mazabar kuma ta umurci INEC da ta ba shi takardar shaidar cin zabe.

Sai dai kotun daukaka kara da ke Abuja ta tabbatar da Natasha Akpoti-Uduagan, ‘yar takarar jam’iyyar PDP a matsayin wacce ta lashe zaben Sanatan Kogi ta Tsakiya da aka gudanar a farkon watan Fabrairu.

Kotun ta yi watsi da karar da Sanata Abubakar Sadiku Ohere na jam’iyyar APC ya shigar saboda rashin cancantata.

Kotun ta Abuja ta kuma yi watsi da wani hukuncin da kotun sauraren kararrakin zabe ta yanke a Jihar Adamawa, ta tabbatar da Mohammed Salihu a matsayin wanda ya lashe zabe a karkashin tutar jam’iyyar PDP a matsayin dan majalisar wakilai.

Haka zalika, kotun daukaka kara da ke zamanta a Abuja ta kammala sauraron karar da Gwamna Abba Kabir Yusuf ya shigar domin kalubalantar tsige shi da kotun sauraron kararrakin zabe ta yi a Jihar Kano.

Alkalan kotun sauraron kararrakin zabe mai mutum uku karkashin jagorancin mai shari’a Oluyemi Akintan Osadebay, suka sauke nasarar Abba a ranar 20 ga Satumba, 2023, inda suka bayyana cewa kuri’u 165,663 ba su da inganci, saboda babu sa hannun INEC kuma babu sitamfin.

Daga nan sai aka rage kuri’un gwamnan zuwa 853,939, yayin da Ganuwa ya samu kuri’u 890,705.

Gwamna Abba ya ki amincewa da hukuncin kotun, wanda ya bayyana a matsayin “Rashin adalci”, inda ya garzaya kotun daukaka kara.
A zaman kotun na ranar Litinin, jagorar lauyoyin gwamnan, Wole Olanipekun, ya bukaci a yi watsi da hukuncin kotun sauraron karar zabe.

Da yake nuna adawa da hukuncin da aka yanke a kan kuri’un bogi, babban lauyan ya ce wannan shi ne karo na farko a tarihi da kotun sauraron karar zabe ta soke zaben da aka yi kan rashin sanya hannu a bayan kuri’un da aka kada lokacin zabe.

Sai dai lauyan APC, Akin Olujimi, ya ki amincewa da bukatarsa, yana mai cewa kotun daukaka kara ta bayyana karara cewa rashin sanya hannu kan kuri’u ya kasance hanyar yin magudin zabe.

Ya kara da cewa dokokin INEC sun bayyana cewa dole ne kowacce kuri’a a sanya hannu tare da rubuta kwanan wata a wata.
Daga karshe kotun daukaka kara ta ce za a sanar da ranar yanke hukunci ga dukkan bangarorin.

Zabe
Yusuf Shuaibu
+ postsBio
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Masana Tattalin Arziki Sun Yi Watsi Da Rahoton NBS Kan Tattalin Arziki
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Alƙawarin Wa’adi Ɗaya Na Peter Obi Ya Raba Kawunan Ƴan Arewa
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    ‘Yan Majalisar Wakilai 50 Da Suka Rasa Tikitin Takara A Zaɓen Fid Da Gwani Na APC
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Zaɓen Fitar Da Gwani: APC Na Fuskantar Barazanar Tawaye

MASU ALAKA

Zabe
Tambarin Dimokuradiyya

2027: Rashin Hadin Kan Atiku Da Obi Da Kwankwaso Na Iya Taimaka Wa Tazarcen Tinubu

May 16, 2026
Adawa
Tambarin Dimokuradiyya

Jam’iyyun Siyasa A Nijeriya Sun Shiga Rudani A Yayin Da Wa’adin Mika Sunayen Mambobi Ya Shude

May 15, 2026
Abincin Da Ya Kamata Ku Ci Lokacin Al’ada
Tambarin Dimokuradiyya

2027: Hadakar ‘Yan Adawa Ta Rushe Yayin Da Tikitin Takarar Shugaban Kasa Ya Raba Kan Shugabannin ADC

May 9, 2026
Next Post
PDP

Gwamnonin PDP Sun Karyata Shirin Mubaya’a Ga Tinubu

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026
Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.