ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, July 15, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Daukaka Karar Shari’o’in Zabe: Wasu Hukunce-hukunce Sun Yi Ba-zata

by Yusuf Shuaibu
3 years ago
Zabe

A ci gaba da sauraron kararrakin zabe da aka shigar a kotunan daukaka kara da ke Abuja da Legas, an samu bazata a wasu daga cikin hukunce-hukuncen da aka zartar da hukunci a wannan mako, musamman ma a shari’o’in ‘yan majalisa na jiha da kuma na gwamna.

Idan dai za a iya tunawa, an rarraba shari’o’in zuwa bangare guda biyu, inda aka mayar da dukkan shari’o’in zaben da aka daukaka kara na yankin arewa a sashin kotun daukaka kara da ke Abuja, yayin da reshen kotun daukaka kara da ke Legas zai yanke hukuncin dukkanin kararrakin zabe na yankin kudu.

  • Gwamnatin Tarayya Ta Yi Fatali Da Zargin Da Obi Ya Yi Mata Kan Karin Kasafin Kuɗi
  • Gaza: Majalisar Dattawa Ta Nemi Nijeriya Ta Matsa Lambar Kafa Kasashe Biyu

Kotun daukaka kara da ke Abuja ta kori nasarar Musa Ilyasu Kwankwaso na jam’iyyar APC, a matsayin dan majalisa mai wakiltar mazabar Kura/Madobi/Garun Malam.
Ta tabbatar da nasarar dan takarar jam’iyyar NNPP, Yusuf Umar Datti, a matsayin halattaccen dan majalisa.

ADVERTISEMENT

A hukuncin da ta yanke mai alkalai uku karkashin jagorancin mai shari’a Tunde Oyebamiji Awotoye, kotun ta tabbatar da nasarar Datti, wanda tun farko hukumar zabe mai zaman kanta ta kasa (INEC) ta ayyana a matsayin wanda ya lashe zabe.

Sai dai kuma kotun sauraron kararrakin zabe da ke zamanta a Jihar Kano, ta bai wa Kwankwaso nasara.

LABARAI MASU NASABA

‘Yan Ƙasar Turkiyya Sun Nuna Jarumta Da Kare Dimokuraɗiyya Mafi Girma A Tarihi – Erdoğan

Amurka Ta Yi Alƙawarin Sa Ido Sosai A Zaɓen Nijeriya Na 2027

Mai shari’a Awotoye cewa kotun sauraron kararrakin zabe ta yi kuskure. Alkalin ya lura cewa an yi amfani da sashe na 77 na dokar zabe. Ya ce babu wata kotu da ke da hurumin yin kasalandan a rikicin cikin gida na jam’iyya.

A bangare guda kuma, kotun daukaka kara reshen Jihar Legas ta kuma kori Darlington Nwokocha, shugaban marasa rinjaye na majalisar dattawa, mai wakiltar Abiya ta tsakiya a karkashin jam’iyyar LP.

Kotun ta bayyana Augustine Akobundu na jam’iyyar PDP a matsayin wanda ya lashe zaben da aka gudanar a ranar 25 ga watan Fabrairu na yankin majalisar dattawa.
Yayin da kotun daukaka kara da ke zamanta a Abuja ta kuma kori tsohon gwamnan Jihar Benuwai, Gabriel Suswam daga majalisar dattawa.

Kotun ta ayyana Mista Emmanuel Udende na jam’iyyar APC a matsayin wanda ya yi nasara.

Haka kuma kotun daukaka kara da ke Abuja ta kuma kori Sanata Ishaku Abbo, dan majalisa mai wakiltar Adamawa ta Arewa a majalisar dattawa, wanda ta ayyana dan takarar jam’iyyar PDP, Amos Yohanna a matsayin wanda ya yi nasara.

Kotun daukaka kara da ke zamanta a Abuja ta kuma kori dan majalisa mai wakiltar Mubi ta Arewa da Mubi ta Kudu da kuma Maiha ta Jihar Adamawa a zauren majalisar wakilai, Hon. Jingi Rufai.

Kotun ta kori dan takarar jam’iyyar PDP a zaben majalisar, yayin da ta bayyana Hon. Jaafar Magaji na jam’iyyar APC a matsayin wanda ya lashe zaben mazabar kuma ta umurci INEC da ta ba shi takardar shaidar cin zabe.

Sai dai kotun daukaka kara da ke Abuja ta tabbatar da Natasha Akpoti-Uduagan, ‘yar takarar jam’iyyar PDP a matsayin wacce ta lashe zaben Sanatan Kogi ta Tsakiya da aka gudanar a farkon watan Fabrairu.

Kotun ta yi watsi da karar da Sanata Abubakar Sadiku Ohere na jam’iyyar APC ya shigar saboda rashin cancantata.

Kotun ta Abuja ta kuma yi watsi da wani hukuncin da kotun sauraren kararrakin zabe ta yanke a Jihar Adamawa, ta tabbatar da Mohammed Salihu a matsayin wanda ya lashe zabe a karkashin tutar jam’iyyar PDP a matsayin dan majalisar wakilai.

Haka zalika, kotun daukaka kara da ke zamanta a Abuja ta kammala sauraron karar da Gwamna Abba Kabir Yusuf ya shigar domin kalubalantar tsige shi da kotun sauraron kararrakin zabe ta yi a Jihar Kano.

Alkalan kotun sauraron kararrakin zabe mai mutum uku karkashin jagorancin mai shari’a Oluyemi Akintan Osadebay, suka sauke nasarar Abba a ranar 20 ga Satumba, 2023, inda suka bayyana cewa kuri’u 165,663 ba su da inganci, saboda babu sa hannun INEC kuma babu sitamfin.

Daga nan sai aka rage kuri’un gwamnan zuwa 853,939, yayin da Ganuwa ya samu kuri’u 890,705.

Gwamna Abba ya ki amincewa da hukuncin kotun, wanda ya bayyana a matsayin “Rashin adalci”, inda ya garzaya kotun daukaka kara.
A zaman kotun na ranar Litinin, jagorar lauyoyin gwamnan, Wole Olanipekun, ya bukaci a yi watsi da hukuncin kotun sauraron karar zabe.

Da yake nuna adawa da hukuncin da aka yanke a kan kuri’un bogi, babban lauyan ya ce wannan shi ne karo na farko a tarihi da kotun sauraron karar zabe ta soke zaben da aka yi kan rashin sanya hannu a bayan kuri’un da aka kada lokacin zabe.

Sai dai lauyan APC, Akin Olujimi, ya ki amincewa da bukatarsa, yana mai cewa kotun daukaka kara ta bayyana karara cewa rashin sanya hannu kan kuri’u ya kasance hanyar yin magudin zabe.

Ya kara da cewa dokokin INEC sun bayyana cewa dole ne kowacce kuri’a a sanya hannu tare da rubuta kwanan wata a wata.
Daga karshe kotun daukaka kara ta ce za a sanar da ranar yanke hukunci ga dukkan bangarorin.

Zabe
Yusuf Shuaibu
+ postsBio
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Amurka Ta Yi Alƙawarin Sa Ido Sosai A Zaɓen Nijeriya Na 2027
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Sautin Muryar Da Aka Fallasa Kan El-Rufai Ya Haifar Da Zazzafar Muhawara
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Ci-ma-zaunen Ƴan Siyasa Ne Ke Tunanin Yin Maguɗi A Zaɓen 2027 – Makarfi
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    An Samu Ruɗani Kan Rashin Bayyana Jerin Ƴan Takarar Jam’iyyun Siyasa Na Zaɓen 2027

MASU ALAKA

‘Yan Ƙasar Turkiyya Sun Nuna Jarumta Da Kare Dimokuraɗiyya Mafi Girma A Tarihi – Erdoğan
Manyan Labarai

‘Yan Ƙasar Turkiyya Sun Nuna Jarumta Da Kare Dimokuraɗiyya Mafi Girma A Tarihi – Erdoğan

July 15, 2026
Amurka Ta Yi Alƙawarin Sa Ido Sosai A Zaɓen Nijeriya Na 2027
Tambarin Dimokuradiyya

Amurka Ta Yi Alƙawarin Sa Ido Sosai A Zaɓen Nijeriya Na 2027

July 11, 2026
Sautin Muryar Da Aka Fallasa Kan El-Rufai Ya Haifar Da Zazzafar Muhawara
Tambarin Dimokuradiyya

Sautin Muryar Da Aka Fallasa Kan El-Rufai Ya Haifar Da Zazzafar Muhawara

July 11, 2026
Next Post
PDP

Gwamnonin PDP Sun Karyata Shirin Mubaya’a Ga Tinubu

LABARAI MASU NASABA

Sabbin Ministoci

Rashin Tsaro: Majalisar Dattawa Ta Bukaci A Tura Ƙarin Sojoji da ’Yansanda Zuwa Benuwe

July 15, 2026
GDPn Sin A Rabin Farko Na Shekarar 2026 Ya Karu Da Kashi 4.7% Idan Aka Kwatanta Da Na Kwatankwacin Lokacin Bara

GDPn Sin A Rabin Farko Na Shekarar 2026 Ya Karu Da Kashi 4.7% Idan Aka Kwatanta Da Na Kwatankwacin Lokacin Bara

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Tsaurara Tsaron Iyakokin Kano Bayan Hare-haren ‘Yan Bindiga 

Atiku Ya Nuna Damuwa Kan Kasafin Naira Biliyan 6.44 Don Gasar Cin Kofin Duniya ta 2026

July 15, 2026
Masana Kandagarkin Cututtuka Na Sin Sun Tashi Zuwa Kasar Uganda Don Aikin Hadin Gwiwar Magance Cutar Ebola

Masana Kandagarkin Cututtuka Na Sin Sun Tashi Zuwa Kasar Uganda Don Aikin Hadin Gwiwar Magance Cutar Ebola

July 15, 2026
‘Yan Ƙasar Turkiyya Sun Nuna Jarumta Da Kare Dimokuraɗiyya Mafi Girma A Tarihi – Erdoğan

‘Yan Ƙasar Turkiyya Sun Nuna Jarumta Da Kare Dimokuraɗiyya Mafi Girma A Tarihi – Erdoğan

July 15, 2026
Majalisa Ta Ba da Tallafin ₦50m Ga Iyalan Malamai Da Jami’an Tsaro Da Aka Kashe A Aikin Ceto A Oyo

Majalisa Ta Ba da Tallafin ₦50m Ga Iyalan Malamai Da Jami’an Tsaro Da Aka Kashe A Aikin Ceto A Oyo

July 15, 2026
Xi Ya Bukaci A Mayar Da Hankali Kan Bukatun Jama’a Yayin Rangadin Da Ya Yi A Shanghai

Xi Ya Bukaci A Mayar Da Hankali Kan Bukatun Jama’a Yayin Rangadin Da Ya Yi A Shanghai

July 15, 2026
Katsina: Kotu Ta Yanke Wa Hauwa’u Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya Kan Taimaka Wa ’Yan Bindiga

Lalata Da Ƙaramar Yarinya: Kotu Ta Yanke Wa Tsoho Mai Shekara 75 Hukuncin Ɗaurin Shekara 10 A Ribas

July 15, 2026
Ci Gaban Fasaha Na Hidimtawa Jama’a Cikin Kowane Yanayi A Kasar Sin

Ci Gaban Fasaha Na Hidimtawa Jama’a Cikin Kowane Yanayi A Kasar Sin

July 15, 2026
‘Yan Bindiga Sun Sace Shugaban Makaranta, Jami’in NECO Da Ɗalibai A Kogi

‘Yan Bindiga Sun Sace Shugaban Makaranta, Jami’in NECO Da Ɗalibai A Kogi

July 15, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.