ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, July 15, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Domin Rage Kashe Kudi Za A Yi Wa Ma’aikatu Garambawul Ba Korar Ma’aikata Ba – Ministan Labarai

Ba Da Jimawa Ba Za A Fara Rabon Tallafin Kudi - Ministan Kudi

by Leadership Hausa
2 years ago
ma'aikatu

Ministan Yaɗa Labarai Da Wayar Da Kai, Alhaji Mohammed Idris, ya bayyana cewa Majalisar Zartaswa ta Ƙasa ta yanke shawarar yin amfani da rahoton yi wa ma’aikatu da hukumomin Gwamnatin Tarayya garambawul na kwamitin Steve Oronsaye ne domin a rage yawan kashe kuɗaɗen tafiyar da ayyukan gwamnati.

Idris ya ce a karkashin tsarin, wasu Ma’aikatun da Sassa da Hukumomi da Cibiyoyi za a rushe su, sannan za a haɗe wasu da wasu, wasu kuma za a maida su cikin hukumomin gwamnati da suka cancanta.

Ya ce dalilin yin hakan shi ne don gwamnati ta rage kashe kuɗaɗe, amma ba don a kori ma’aikata ba.

ADVERTISEMENT

Ministan, wanda shi da takwaransa na kudi suka yi karin haske ga manema labarai bayan kammala majalisar zartarwa na makon nan ranar Litinin, ya ce nan gaba kadan za a ji adadin yawan ma’aikatu da hukumomin da abin ya shafa ba da daɗewa ba, yayin da aka kafa kwamitin da zai zartar da wannan aiki.

Dangane da batun masu tafiya yajin aiki, Idris ya ce gwamnati ta cika fiye da kashi 85 bisa 100 na yarjejeniyar da ta cimma da Ƙungiyar Ƙwadago ta Nijeriya (NLC) a cikin 2023.

LABARAI MASU NASABA

Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

Rashin Tsaro: Majalisar Dattawa Ta Bukaci A Tura Ƙarin Sojoji da ’Yansanda Zuwa Benuwe

Ministan ya buƙaci shugabannin ƙungiyar ƙwadago da su dubi irin ƙoƙarin da gwamnati ke yi wajen ganin ta magance ƙalubalen da ƙasar nan ke fuskanta.

  • Tsadar Rayuwa: Zanga-zangar NLC Ta Mamaye Abuja, Legas, Gombe, Oyo, Ondo, Ribas Da Sauran Jihohi.

Ya ce bai kamata ‘yan ƙwadago su bayar da wata kafa wadda waɗanda ba su yi wa ƙasar nan fatan alheri ka iya kawo ruɗani a wannan mawuyacin halin da ake ciki ba.

Haka nan kuma Majalisar Zartaswa ta amince a ci gaba da biyan kuɗaɗen tallafin marasa galihu a ƙarƙashin shirin NSIP.

Ministan Kuɗi Da Kula Da Tattalin Arziki, Mista Wale Edun, cewa ya yi za a ɗauki matakan da suka dace domin tantance waɗanda suka cancanta su ci gajiyar tallafin.

Ya ce dukkan waɗanda za su ci gajiyar tallafin za a tantance su ne ta hanyar lambar sirri ta asusun bankin su (BVN) da kuma lambar shaidar ɗan ƙasa (NIN), sai kuma lambar asusun bankin su, ko da bayan an biya su kuɗaɗen ne.

Edun ya ce sake farfaɗo da shirin bayar da tallafin kuɗaɗen ya zo daidai ne lokacin da wannan gwamnati ke ƙara  azamar magance ƙalubalen tsadar rayuwa da marasa galihu ke fuskanta.

Ya ce magidanta miliyan 12 ne za su ci moriyar shirin, kuma nan ba da daɗewa ba ne za a fara tura masu N25,000 daga shirin na NSIP.

 

ma'aikatu
Leadership Hausa
Website |  + postsBio
  • Leadership Hausa
    Tallafa Wa Yara Masu Buƙatu Na Musamman Shi Ne Burina
  • Leadership Hausa
    Dole Mata Su Rungumi Sana’o’i Domin Tsira Daga Takaicin Zamani —Ramatu Bello
  • Leadership Hausa
    Batun Dakile Shan Taba Sigari A Tsakanin Yara A Nijeriya
  • Leadership Hausa
    Har Yanzu Akwai Sauran Rina A Kaba Game Da Makomar Yara A Nijeriya

MASU ALAKA

Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya
Labarai

Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

July 15, 2026
Sabbin Ministoci
Labarai

Rashin Tsaro: Majalisar Dattawa Ta Bukaci A Tura Ƙarin Sojoji da ’Yansanda Zuwa Benuwe

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Tsaurara Tsaron Iyakokin Kano Bayan Hare-haren ‘Yan Bindiga 
Labarai

Atiku Ya Nuna Damuwa Kan Kasafin Naira Biliyan 6.44 Don Gasar Cin Kofin Duniya ta 2026

July 15, 2026
Next Post
Sojoji Sun Kuɓutar Da Mutum 35 Da Aka Yi Garkuwa Da Su A Jihar Katsina

Sojoji Sun Yi Watsi Da Karɓar Cin Hancin Miliyan ₦1.5 Daga Ɓarayin Shanu A Filato

LABARAI MASU NASABA

Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

July 15, 2026
Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

July 15, 2026
Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

July 15, 2026
Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

July 15, 2026
Kevin Kelly: AI Na Iya Taimakawa Wajen Cimma Burin “Koyar Da Dalibai Da Kwazonsu”

Kevin Kelly: AI Na Iya Taimakawa Wajen Cimma Burin “Koyar Da Dalibai Da Kwazonsu”

July 15, 2026
Gwamna Yusuf Ya Bai Wa Masu Kula Da Akwatinan Zaɓe Na APC Filaye 1,540 Da Tallafin Miliyan 100

Gwamna Yusuf Ya Bai Wa Masu Kula Da Akwatinan Zaɓe Na APC Filaye 1,540 Da Tallafin Miliyan 100

July 15, 2026
Sabbin Ministoci

Rashin Tsaro: Majalisar Dattawa Ta Bukaci A Tura Ƙarin Sojoji da ’Yansanda Zuwa Benuwe

July 15, 2026
GDPn Sin A Rabin Farko Na Shekarar 2026 Ya Karu Da Kashi 4.7% Idan Aka Kwatanta Da Na Kwatankwacin Lokacin Bara

GDPn Sin A Rabin Farko Na Shekarar 2026 Ya Karu Da Kashi 4.7% Idan Aka Kwatanta Da Na Kwatankwacin Lokacin Bara

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Tsaurara Tsaron Iyakokin Kano Bayan Hare-haren ‘Yan Bindiga 

Atiku Ya Nuna Damuwa Kan Kasafin Naira Biliyan 6.44 Don Gasar Cin Kofin Duniya ta 2026

July 15, 2026
Masana Kandagarkin Cututtuka Na Sin Sun Tashi Zuwa Kasar Uganda Don Aikin Hadin Gwiwar Magance Cutar Ebola

Masana Kandagarkin Cututtuka Na Sin Sun Tashi Zuwa Kasar Uganda Don Aikin Hadin Gwiwar Magance Cutar Ebola

July 15, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.