ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Domin Rage Kashe Kudi Za A Yi Wa Ma’aikatu Garambawul Ba Korar Ma’aikata Ba – Ministan Labarai

Ba Da Jimawa Ba Za A Fara Rabon Tallafin Kudi - Ministan Kudi

by Leadership Hausa
2 years ago
ma'aikatu

Ministan Yaɗa Labarai Da Wayar Da Kai, Alhaji Mohammed Idris, ya bayyana cewa Majalisar Zartaswa ta Ƙasa ta yanke shawarar yin amfani da rahoton yi wa ma’aikatu da hukumomin Gwamnatin Tarayya garambawul na kwamitin Steve Oronsaye ne domin a rage yawan kashe kuɗaɗen tafiyar da ayyukan gwamnati.

Idris ya ce a karkashin tsarin, wasu Ma’aikatun da Sassa da Hukumomi da Cibiyoyi za a rushe su, sannan za a haɗe wasu da wasu, wasu kuma za a maida su cikin hukumomin gwamnati da suka cancanta.

Ya ce dalilin yin hakan shi ne don gwamnati ta rage kashe kuɗaɗe, amma ba don a kori ma’aikata ba.

ADVERTISEMENT

Ministan, wanda shi da takwaransa na kudi suka yi karin haske ga manema labarai bayan kammala majalisar zartarwa na makon nan ranar Litinin, ya ce nan gaba kadan za a ji adadin yawan ma’aikatu da hukumomin da abin ya shafa ba da daɗewa ba, yayin da aka kafa kwamitin da zai zartar da wannan aiki.

Dangane da batun masu tafiya yajin aiki, Idris ya ce gwamnati ta cika fiye da kashi 85 bisa 100 na yarjejeniyar da ta cimma da Ƙungiyar Ƙwadago ta Nijeriya (NLC) a cikin 2023.

LABARAI MASU NASABA

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Ministan ya buƙaci shugabannin ƙungiyar ƙwadago da su dubi irin ƙoƙarin da gwamnati ke yi wajen ganin ta magance ƙalubalen da ƙasar nan ke fuskanta.

  • Tsadar Rayuwa: Zanga-zangar NLC Ta Mamaye Abuja, Legas, Gombe, Oyo, Ondo, Ribas Da Sauran Jihohi.

Ya ce bai kamata ‘yan ƙwadago su bayar da wata kafa wadda waɗanda ba su yi wa ƙasar nan fatan alheri ka iya kawo ruɗani a wannan mawuyacin halin da ake ciki ba.

Haka nan kuma Majalisar Zartaswa ta amince a ci gaba da biyan kuɗaɗen tallafin marasa galihu a ƙarƙashin shirin NSIP.

Ministan Kuɗi Da Kula Da Tattalin Arziki, Mista Wale Edun, cewa ya yi za a ɗauki matakan da suka dace domin tantance waɗanda suka cancanta su ci gajiyar tallafin.

Ya ce dukkan waɗanda za su ci gajiyar tallafin za a tantance su ne ta hanyar lambar sirri ta asusun bankin su (BVN) da kuma lambar shaidar ɗan ƙasa (NIN), sai kuma lambar asusun bankin su, ko da bayan an biya su kuɗaɗen ne.

Edun ya ce sake farfaɗo da shirin bayar da tallafin kuɗaɗen ya zo daidai ne lokacin da wannan gwamnati ke ƙara  azamar magance ƙalubalen tsadar rayuwa da marasa galihu ke fuskanta.

Ya ce magidanta miliyan 12 ne za su ci moriyar shirin, kuma nan ba da daɗewa ba ne za a fara tura masu N25,000 daga shirin na NSIP.

 

ma'aikatu
Leadership Hausa
Website |  + postsBio
  • Leadership Hausa
    Batun Dakile Shan Taba Sigari A Tsakanin Yara A Nijeriya
  • Leadership Hausa
    Har Yanzu Akwai Sauran Rina A Kaba Game Da Makomar Yara A Nijeriya
  • Leadership Hausa
    Yadda Arsenal Ta Lashe Gasar Firimiya Bayan Shekara 22
  • Leadership Hausa
    Bukatar Kawo Karshen Akidar Kyamar Baki A Kasar Afirka Ta Kudu

MASU ALAKA

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi
Labarai

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”
Ra'ayi Riga

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma
Labarai

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Next Post
Sojoji Sun Kuɓutar Da Mutum 35 Da Aka Yi Garkuwa Da Su A Jihar Katsina

Sojoji Sun Yi Watsi Da Karɓar Cin Hancin Miliyan ₦1.5 Daga Ɓarayin Shanu A Filato

LABARAI MASU NASABA

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026
Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026
Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

June 24, 2026
Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.