Hukumar tsaro ta farin kaya (DSS) ta kama tsohon gwamnan Jihar Kaduna, Nasir El‑Rufai, a daren ranar Laraba jim kaɗan bayan da EFCC ta bayar da belinsa, inda take tsare da shi tun ranar Litinin kan zargin rashawa.
Rahotanni sun ce jami’an DSS sun ɗauke shi ne a wajen hedikwatar EFCC da misalin ƙarfe 8 na dare.
- Kudin Tikitin Kallon Fina-finai Yayin Hutun Bikin Bazara Na Kasar Sin Ya Zarce Yuan Biliyan 2
- Gwamnatin Gabon Ta Haramta Amfani Da Kafafen Sada Zumunta A Ƙasar
Sabon kamen yana da nasaba da tuhume-tuhumen laifin kutse da ake zarginsa da aikatawa a wayar mai bai wa shugaban ƙasa shawara kan harkokin tsaro, Nuhu Ribadu.
An shigar da ƙararsa a babbar kotun tarayya, amma har yanzu ba a sanya ranar gurfanar da shi ba, kuma bai yi martani ba.
Lamarin ya biyo bayan wata hira da ya yi a gidan talabijin na Channels, inda ya ce an saurari wayar da Ribadu ya yi na bayar da umarnin a kama shi.
Tun bayan da ya sauka daga kan mulki, yake fuskantar bincike daban-daban.














Discussion about this post