Wani mummunan al’amari ya auku a yankin masu haƙo ma’adinai na Zurak da ke Ƙaramar Hukumar Wase, inda aka tabbatar da mutuwar aƙalla mutum 38, yayin da aka kwantar da wasu da dama a asibiti sakamakon zargin shakar isƙar guba a wani ramin haƙo ma’adinai na ƙarƙashin ƙasa.
Lamarin ya faru ne da safiyar ranar Talata, inda ake zargin cewa ma’aikatan sun shaƙi hayaƙi mai guba, wanda ake kyautata zaton sinadarin “carbon monoxide” ne da ya taru a cikin ramin ma’adinan.
- Gwamnatin Gabon Ta Haramta Amfani Da Kafafen Sada Zumunta A Ƙasar
- CMG Ya Gabatar Da Kasaitaccen Shagalin Murnar Shiga Sabuwar Shekarar Gargajiya Ta Kasar Sin
Majiyoyi sun bayyana cewa ma’aikatan sun yi haƙa mai zurfi a ƙasa kafin su ci karo da iskar mai kisa, wadda ta haddasa shaƙewa tare da mutuwar wasu nan take, inda daga baya aka ceto wasu daga cikin su da ransu, tare da garzaya da su zuwa cibiyoyin lafiya domin basu kulawar gaggawa.
Wani jagoran matasa a yankin, mai suna Shafi Sambo, ya tabbatar da faruwar lamarin, yana mai cewa ma’aikatan na bakin aiki ne lokacin da iskar gubar ta bazu cikin ramin, duk da cewa an samu nasarar fitar da wasu da ransu kuma a halin yanzu suna karɓar magani.
A nata ɓangaren, Gwamnatin Jihar Filato, ta bakin Kwamishiyar Yaɗa Labarai, Joyce Lohya Ramnap, ta bayyana alhininta kan wannan mummunan lamari, tana mai cewa tana aiki tare da hukumomin tsaro da jami’an agajin gaggawa da hukumomin lafiya domin shawo kan halin da ake ciki.
Gwamnatin ta kuma tabbatar wa al’umma cewa za ta ɗauki matakan da suka dace domin magance wannan ibtila’i tare da tabbatar da kare rayuka a dukkanin yankunan hako ma’adinai a faɗin jihar.















Discussion about this post