Hukumar da ke kula da kafofin yaɗa labarai a ƙasar Gabon ta sanar da dakatar da amfani da dukkanin kafofin sada zumunta.
Wannan mataki ya biyo bayan yadda abubuwan da ake wallafawa a intanet ke haddasa rikici da rarrabuwar kawuna a cikin al’umma.
- Tinubu Ya Sanya Hannu Kan Dokar Gyaran Zaɓe Duk Da Rikicin Tura Sakamako
- Sabon Rikici Ya Kunno Kai A Jam’iyyar APC A Kano
Jean-Claude Mendome, kakakin Babban Kwamitin Sadarwa, ya ce saƙonnin da ke cin zarafi da ɓata suna suna rusa ɗabi’a, haɗin kai da tsaron ƙasa.
Haka kuma ya ce yaɗuwar labaran ƙarya, cin zarafi, da bayyana bayanan sirri ba tare da izini ba sun kasance wasu daga cikin dalilan dakatarwar.
Mendome ya yi gargaɗin cewa irin waɗannan ayyukan na iya haifar da rikici a al’umma da barazana ga haɗin kai da ci gaban dimokuraɗiyya a Gabon.
Hukumar ba ta fayyace wane kafofin sada zumunta ne dakatarwa ta shafa ba.
Duk da haka, ta jaddada cewa ‘yancin faɗin ra’ayi, ciki har da sukar gwamnati, har yanzu haƙƙi ne wanda yana nan daram.
Tun bayan da Shugaba Brice Oligui Nguema ya hau mulkin ƙasar a shekarar da ta gabata, ya fuskanci zanga-zanga da yajin aiki.
Malamai sun fara yajin aiki kan albashi da yanayin aiki tun a watan Disamban bara, sannan sauran ma’aikatan gwamnati a fannin lafiya da ilimi su ma suka shiga yajin aikin.














Discussion about this post