Hukumar Tsaron Farin Kaya (DSS), ta kama mutane biyar, ciki har da ‘yan ƙasar Nijar biyu, bisa zargin samar da makamai ga ‘yan bindigar da suka sace ɗalibai da ma’aikatan Makarantar Katolika ta St. Mary’s da ke garin Papiri a Jihar Neja a watan Nuwamban 2025.
Hukumar ta kuma ƙwato bindigogi ƙirar AK-103 guda 15, mujallu 15 da harsasai 1,434 a yayin samamen.
Majiyoyin tsaro sun ce an kama Yusuf Mohammed, wanda aka fi sani da Bature, da Mubarak Ibrahim a kan hanyar Zariya zuwa Kaduna yayin da suke kan hanyarsu ta karɓo makamai.
Bincike ya kai ga kama Goni Ibrahim, wani dillalin makamai daga yankin Diffa na Jamhuriyar Nijar, da abokinsa Tukur Sani.
Daga baya kuma an kama Alhaji Adamu, wanda aka fi sani da Gado Banufe, a Yauri ta Jihar Kebbi.
Ana zarginsa da samar da makamai ga masu aikata laifuka a yankin.
Jami’an tsaro sun ce bincike ya nuna cewa mutanen biyar ɗin na cikin masu kai wa ‘yan bindigar da suka kai hari makarantar makaman da suke amfani da su.
A ranar 21 ga watan Nuwamban 2025, ‘yan bindiga sun kai hari makarantar tare da sace ɗalibai da malamai da dama.
Yayin da wasu suka tsere, sun sace sama da mutum 250 zuwa dajin Kainji.
Daga bisani, a ranar 21 ga watan Disamba, 2025, gwamnati ta tabbatar da ceto tare da dawo da sauran mutanen da aka sace cikin ƙoshin lafiya.
A gefe guda kuma, Ƙungiyar Kiristocin Arewa (NCA), ta yaba wa DSS da Darakta-Janar ɗinta, Oluwatosin Ajayi, kan kama waɗanda ake zargin.
Shugaban ƙungiyar, Joseph John Hayab, ya ce ya kamata a riƙa yaba wa hukumomi idan sun samu nasara, kamar yadda ake sukar su idan sun gaza.















Discussion about this post